17

4.4K 335 10
                                    

*El'mustapha*

*Haske Writers Association*

Fertymerh Xarah💞

17

'Anty kiyi haquri bada son raina bane, nima ban san yanda akayi ba, laifin xuciyata ne.

Laifin xuciyarki da tayi me uwani? Jiddah ta tambaya tana kallonta cikin rudewa, me kike nufi.

wlhy sonsa nake bansan yanda akayi xuciyata ta kamu da soyayyar sa, anty kiyi haquri wlhy xanyi qoqari na cire amma shine asalin damuwa ta.

Photon dake hannun jiddah ya subulce ya fadi qasan tiles, me take ji a bakin uwani haka, idan mafarki takeyi Allah ya farkar da ita daga wannan mummunan barcin, uwani ke son el'mustapha din ta, mutumin da bata hada shi da kowa da komai ba, mutumin da batason ko wacce mace ta rabe sa, mutumin da take gani ita kadaice a xuciyarsa har qarshin rayuwarta, taya xata iya rayuwa dashi da wata mace, macen ma uwani yar uwarta, impossible, juyawa tayi ta fita jiri na neman kada ta, she can't say anything for now amma uwani tayi mata baxata kuma ta cuceta idan har da gaske tana son el'mustapha.

Kallonta uwani keyi har lokacin da ta fice, tausayinta da dana sanin furta mata ya sanyata fargama amma ya xatayi tunda ta kamata dumu dumu da hotonsa a hannu meyiwuwa hakan xaisa ta amince mata ga auren mijinta.

Maida kanta tayi jikin pillow tana kuka sosai, bata iyayen ta takeyi ba yanda el'mustapha xai amince da auren ta shine matsalar, babu boka babu malami alqawari ne na daukar wa kaina ko ta halin qaqa sai na auri el'mustapha, sai ya xamo mallakina a gidannan, ta share hawayen fuskarta, ai ba dan mace daya akayi namiji ba, kowacce kissarta ta fiddata amma ina son el'mustapha kuma sai na rabi inuwarsa, ta share hawayen fuskarta hade da shigewa toilet.

Jiddah kuwa tunda ta shiga dakinta kanta ke mata wani irin nauyi, ta kasa gasgasta abinda kunnuwanta suka jiye mata a yau, uwani ke son mijinta, to ko uwani ta manta dangantakar su ne ta manta matsayinta na yayarta har take son kishi da ita.

Nan take ta fara tunanin take taken uwani akan el'mustapha tabbas biri yayi kama da mai, idan hakane uwani ta cuce ta batayi halin iyayenta na amana ba.

Yinin ranar gabaki daya a daki tayi sa ko abinci bata ci ba har lokacin da su Aryan suka dawo, su kansu sunsan mamin tasu tana cikin damuwa a yau duk surutun da suke mata shiru take a yau sai faman tunani, har lokacin da el'mustapha ya dawo.

Tunda ya shigo falonta yake kiran sunanta cikin muryarsa mai sanyi da dadin sauraro, tayi qoqarin sai ta xuciyarta kada ya gano tana cikin damuwa amma kallo daya yayi mata ya gano hakan a idanuwanta,

Da sassarfa ya isa gareta, ya dora hannunsa akan fuskarta yana kallonta sosai,

'meke damun jiddana, meyasa idanunki sukayi ja haka.

Da kyar ta hadiye kukan ta haqe da qago murmushin da iya karsa lebbanta,

'tun daxu nake fama da ciwon kai, dana sha maganine na sami barci inajin wannan daliline ya sanya sauyawar idanuna.

Allah ya baki lfy jiddana, gashi yau ina buqatar kulawar ki, ya xakiyi dani.

Dogon hancinsa taja tana dariya, abinda kake so shi xaa yi idan dai inada wannan iko, shima dariya yayi yayi gaba tana biye dashi a baya har dakin su,

Juyowa yayi yana kallonta, kinsan me Ibrahim yayi kuwa?

Ta girgixa kai tana kallonsa yayin da take qoqarin balle masa botiran rigarsa,

'aure xai qara next week, har ya bada sadaki amma bada sanin matar sa ba hadixa.

Jiddah ta xaro idanu tana kallonsa, yayin da gabanta ya tsananta bugawa,

El'mustapha Where stories live. Discover now