BIYAYYAH

Av maryamad856

41.8K 1.9K 467

Labari ne akan wasu masoya guda biyu da suka had'u wajen yiwa iyayensu BIYAYYA. 'Kir'kirarran labari ne b... Mer

BIYAYYAH
BIYAYYAH
BIYAYYAH....
BIYAYYAH...
BIYAYYAH...
BIYAYYAH......
BIYAYYAH....
BIYAYYAH.....
BIYAYYAH....
BIYAYYAH....
BIYAYYAH......
Biyayyah......
biyayyah.......!
biyayyah.....!
biyayyah.....!
biyayyah....!
biyayyah....!
Biyayyah....!
Biyayyah.....!
Biyayyah.....!
Biyayyah....!
biyayyah.....!
biyayyah....! 59-60
Biyayya....61-62
biyayya....62-63
part.....67
biyayy.....68
biyayy....69
biyayy....70
biyayya......
biyayya.....
biyayya....73
biyayya......73
biyayya.....74
biyayy......75
biyayya......76
biyayya....77
biyayya.....78
biyayya.....79
biyayya.....80
biyayya....81
biyayya.....82
Last page....83
Appology/Biyayya....12-14

biyayya.... 65-66

821 40 10
Av maryamad856

💎💎💎💎
   💎💎💎💎
     💎💎💎
        💎💎

*BIYAYYA*

*Story...writing*
   By
   *Maryam Abdul*

*Typing.....*⌨

   💫 *DA BAZARMU WRITERS ASS*💫

We are here to make you happy.... Smile and educated to realized that we are the best among all..... *DABAZAMU MUKE TUN'KAHO*💃💃

Masoyana ina matuqar alfahari daku....masu comment, vote, like and share duk inatare daku...wad'anda banasamun damar mayar musu da amsa kuyi haquri kunji...amma kuna raina sosai.

Wannan shafin nakine, gaba d'aya littafin sadaukarwane gareki *Nana Khadija* ina alfahri dake sosai.

Kuyi haquri readers nayi mantuwar page ana baya zansa *page 63-64* sai nasa *62-63* amin afuwa duk d'an adam tara yake bai cika gomaba....nagode.

*page....65-66*

*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM*

-------------Koda ta miqo mata abincin girgiza mata kaita alamar bata ci, duk yacce Fiddausee taso Dije taci abincin hakan baisamuba.

Duk da yau tafara zuwa makarantar amma hakan baihanata jin dad'in makarantar ba dan sosai makarantar ta burgeta matuqa.

Koda akatashi tana kallon kowa ana zuwa d'aukanshi suna tafiya itakam sai samun wajetai tazauna.duk dadai dad baicemata za'a zo d'aukantaba amma ita inatason hanyar gidanma balle tace zata koma dakanta.

Tana cikin wannan tunanin ne taji andafata, d'ago  da kanta tai takalli wanda yadafatan, Fiddausee ce tsaye tana kallonta cikin tuhumar zaman me takeyi anan ita kad'ai?

Dije ta d'an gyara zamanta kafin tace" ba'azo d'aukata bane"

Fiddausee tai murmushi kana tace" kizo muje sai drivern ya saukeki wace unguwa kike?"

Dije tai murmushi tace" ah bakomi nagode nasan suna hanyama"

Tana qarasawa taji muryar auta na fad'in" auntynmu"

Waigawatai cike da fara'a ta kalli autan tace" ah auta harkun taso?"

Auta ta gyad'a kai kawai, sai alokacin ta lura da Fiddausee dake tsaye, hannu ta miqamata tare da murmusawa.

Ganin hakan yasa Fiddausee n miqamata nata hannun itama fuskarta cike da qyataccen murmushi.

Cikin qanqanin lokaci suka bud'e babin hira tsakanin Fiddausee da auta, sai Dije tamusu magana ganin abin nasu ba qaraubane.nan sukai sallama tare da musayar lamba.

Ko amota Dijece tai tayiwa auta fad'a" wai akanme daga had'uwa da mutum rana d'aya lokaci d'aya zata sakewa mutum fuska"

Auta tai murmushi tace" aunty ancefa mutane rahmane shiyasa, kuma wllh kallo d'aya namata naji kawai ta kwantamin"

Dije ta ta'be baki kafin tace" uhmm kiyi dai ahankali" daga haka bata sakya cewa wani abuba ahaka har suka qarasa gida.

Koda suka qarasa gida agajiye Dije ta koma kaitsaye d'akinta ta wuce auta da mom nata tsokanarta wai" ahaka za'adinga zuwa school d'in ana dawowa" ita dai batace kanzil ba inbanda haurawa sama datai.

Tanashiga ta fad'a kan gadonta tare da mimmiqewa, tana nan kwance har auta tashigo ta taddata.

Kallonta tai tace" kaddai aunty kice tund'azo kina zaune ahaka ko uniform d'in ma baki cireba?"

Dije taja tsaki kafin tace" hmm kedai bari Allah duk jinaki jikina namin wani iri kamar ana sassarawa"

Auta ta qyalqyale da dariya tare da nuna Dije tace" kai aunty daga farawa"

Dije ta miqe afusace tayo kan auta tace" ni sa'ar kice dazaki dingamin dariya" ganin hakan yasa auta artawa aguje tayi qasa.

Dije ganin hakan yasa tayin qwafa tare da fad'in " yarinya zan kamakine ai batsira kikaiba".

Toilet ta fad'a ta watsa ruwa kana tafito, wata dogowar riga tasa ta atamfa amma tamata kyau duk da bawani ado garetaba saidai tsiyar Dije wani d'ankwalin ta d'akko daban tad'ora akai, duk dacewa auta nayawan gayamata bata kyau intai wannan had'in gambizar amma ina ita batagani.

Saida ta qara hutawa sannan ta sakko qasa, auta ta tarar zaune afalo tana kallon wani series film a MBC2, matsawa tai daf da kan table d'in dake tsakiyar falon cikin sauri da azama tasa hannunta ta d'auke remote d'in.

Auta ganin hakan yasa ta miqewa tare da qarasawa wajen Dije tace" aunty plz dan Allah karki kashe" dan tafahimce mai dije zatai da remote d'in.

Dije tai wani qayataccen murmushi tace" ai wllh saina kashe badai ni kikewa dariyaba"

Auta ta tsugunna tare da kama kunnenta tace" plz aunty sorry" ta qarasa cikin marairaici fuska.

Dije tasaki wata dariya tace" yarinya ni zaki yiwa wayo"

Auta tace" a'a auntynmu ta yaya bada kanki asare kije gida kice ya fad'i"

Dije taja tsaki tace" yarinya kin qara wani laifinma ai, laifi biyi"

Kafin auta tai magana Mom da sakkowarta kenan tace" a'a lafiya meyafaru kuma daga dawowa?"

Auta tai caraf tace" mim kinga fa wai kallo nake shine saita kashe haka kawai"

Mom ta kalli Dije tace" d'iyata meyafaru?"

Dije ta gyara tsaiwa kan tace" yawwa mom kingafa rashin kunya tamin shine dan nace baza'akai tashar nanfa take min gwalo wai dole sai ankalla"

Mom ta riqe baki tare da kallon auta tace" rashin kunyar take har takai haka, matar yayan naki ki kekewa haka"

Auta ta marairaici fuska tace" wllh ba haka bane mom, nifa ba abinda namata Allah ma shaidane"

Mim tace" dalla ni rufen baki, maza ki 'bacen daga gani"

Auta ta miqe tare ta turo baki, har tayi taku d'aya Dije tace" mom qyaleta zoki zauna badan halinkiba yarinya"

Mom tai murmushi dan tanayiwa wannan yarinta tasu dariya sosai, sai suyi fad'a su shirya ka rantse sa'annine, dataiwa Dije maganama catai ai tafi jin dad'i akan tazauna ita kad'ai, kuma yadda ta fahimce Dijen ita d'in mai saiqin kaice dan san shiga jama'a ba ruwanta dakowa.

Nanfa auta tajuyo tare da murmusawa takoma tazauna.Mom ce tace" musu sunci abinci kuwa?"

Auta ta girgiza kai tace" a'a mom daman kwa cikina tun dazu yake kuka"

Mom tace" dalla can rufen baki, ke kam kinzama acici wllh"

Dariya dije tai tace" kamar kinsani mom, kuma yanzu fa naga taci biscuite har guda biyu"

Mom tace" ai zakiga abinda yafi hakama, wannan ai mijinta yashiga uku"

Hannece ta katsemusu hirar tasu da fad'in" Hajiya angama abincin"

" Yawwa Hanne sannu da qoqari, ajera a dinning" mom tafad'a cike da fara'a afuskarta.

Dije ce tabi bayan hannen tare da fad'in" bara na temaka miki ko"

Batajira amsartaba ta kwaso kayan abincin tayo waje, a dinning d'in ta jerasu kamar yadda akeyi.

Suna gama cin abincin Dije ta d'akko jakar makarantarta tare da zaro littafin english ta miqawa mom

Mom ta kalli littafin kana ta kalli Dije tace" yadai 'yata lafiya dai ko?"

Dije ta turo baki tace" mim kinga abinda akamana kuma Allah ni ba abinda nagane aciki"

Mom tai murmushi tare da sha kan Dijen tace" sorry my daughter komi ai sai asannu, kuma ai malamin lesson zai fara zuwa nanda gobe insha Allahu baki da matsala kinji"

Dije ta gyad'a kai alamar ehh.

Nan Mom tayimata bayanin aikin da akai ataqaice yadda zatafi saurin fahimtar karatun.sosai kwa dije ta fahimce saqon da akeson isarwa.

..........Imran ne zaune gabanahi laptop suna video call da Ashraf kallonshi kafin yace" wai kam ka kira gida kaji lafiyar matarka?"

Ashraf yaja tsaki tare da fuzur da iska kafin yace" nisha gayama sam kwata-kwata nibanda mata kagane, amma amma sabida kai dulhu makanine kakasa fahimta ko?" yaqarasa tare dayin qwafa.

Imran ya harareshi kana yace" a kamanta dulhu jaki ne ba makaniba, kuma kada Allah yasa kayi matar, aikin banza"

Ashraf yayi wani qayataccen murmushi kan yace" matsala ta dakai d'aya ce rashin fahimtar abu, wllh ina tausayawa matar dazaka aura"

Imran yace" banza kai ba'ace ana tausayawa matar dake tare dakaiba sai kaine kake tausayawa wata matar da kuma bahakanne zai kasanceba, wllh Allah yatemakeki kasami mata mai kawaici da haquri"

Ashraf yaja wani qatan tsaki yace" baka da aikin yine ai, yarinyar da sam bata da d'a amma kake wani cewa wai mai kawaici da haquri, na zageka wllh"

Imran yace" yaro kafasa wllh Ashraf kana wasa da damarka seriously nakema maganar nan, sabida kasami mata tagari wllh yarinyacefa kaga kai zaka juyata yadda ranka yakeso, kuma kaga bata waye irin wayewar yarin zamanin yanzuba"

"Mits! Ashraf yaja tsaki baka da aikin yi haryanzu na gayama, ni kaga tafiyata" yana qarasa fad'a yakatse kiran. Imran kuwa murmushi yai tare da girgiza kai" tabba yasan Ashraf yadad'e dayin nisa bazai ta'ba jin kiraba bare yai wai-waye, amma har yanzu yana fata ubangiji yajuyo da hankalinsa ya fahimce gaskiyar al'amurannan" da wannan tunanin ya fad'a tiolet dan watsa ruwa, sabida yadda gari yai zafi sosai.

.........Jummai zaune tana aikin tunanin nata da yanzu yazame mata jiki, cikin zuciyarta namata wani iri duk lokacin da ta tuno da cewar al'amarinfa ba lallai yakasance yadda take hasasheba, dankwa tanajin hakan kamar zaiyi wuya, ita dashi kai ina anya kuwa.

Goge qwallar data zu'bomata tai akan kumatunta tare da furta" Allah kaga baiwarka, ka bani mafita acikin wannan al'amari nawa, bashakka inasonsa sosai ya Allah kakawon mafita"

Nik nace" ti jummai me kikeso hakane, amma dai ameen "

Miqewa tai ta fad'a d'akin Iya tare da gaidata dan yau bata shigo gidan da wuriba, kuma yanzunma data shigo sai tunanin masoyinta yatsaidata a soro.

Nan ta d'ora musu girki dan yau Inna azumi take hakan yasa bata d'ora abincin da wuriba, koda yakema Jummance ta hanata tace" ta girka musi"

Iya dai sam barka tana matuqar jin dad'in zama da Jummai, kuma tana d'aukemata kewar jikartata, wannan yasa takasance cikin farin ciki sosai da sosai.

..........Dije ce cikin shirinta na makaranta, saidai yau sam batajin sha'awar zuwa makarantar dan ta kwa yau da wani matsanancin ciwin mara ta tashe, saidai abin mamakinta bai wuce tunda tazo gidannan bataiba sai yanzu, to me hakan yake nufe? kodai tayi cikine da ake cewa mace tana ciki sai al'adarta ta d'auke tsawon wasu watanni, innalillahi kawai take ta ambata, inkwa hakane kam ita tashiga uku wllh da wannan mugun "

Nikam nace" hhhhh kai dije haka ake cikin, kodai aruwa kisha ne bamusaniba"

Mom na kallonta taga fuskarta duk ayamutse " Khadija lafiyarki kuwa, ko makarantarce bakkison zuwa?" mom ta jero mata wad'annan tambayoyin.

Dike ta girgiza kai kana tace" mom cikina ke ciwo tun da natashi da safe yake ta murd'amin"

Mom tace" ayya sannu, to ko zamuje asibiti ne adubaki?"

Girgiza kai Dije tai kan tace" a'a mom, ai na warkema" itakam tsoronta d'aya bai wuce ace cikin ne da ita.

Duk yadda mom taso dije ta haqura da zuwa school d'in abin baiyiwoba dan dagewa taiakan ita yadainamata ciwofa, bayadda mom ta iya haka ta qyaleta suka tafi.

Kamar dai jiyan saida aka sauke auta atata makarantar sannan aka sauke dije atata itama.

Tana shiga aji bata dad'e da zamaba malamar maths d'insu ta shigo, aiki ta musu sosai wanda har da yimusu test, dije kam sai zazzaro ido takeyi dan ba abunda ta iya aciki ga kuma mararta datake murd'amata kamar zata cire.

Malamar ce take d'an zagayesu tana duba yadda suke test d'in, dai-dai lokacin da dije ta sauka qasa daga kan deak d'in tare da cizon lips d'in ta duka biyun.

Malamar ce taganta durqushe aqasa hakan yasa ta tambayar wace aqasan bench?"

Jin shiru ba amsamata ba yasata fusata dan malamar akwai saurin fushi, abinda bata saniba shine itafa sam dije batason me malamar take cewabane.

Ganin malamar tasu ta  d'an fusata kuma sunsan tsaf zata iya zaneta ko tasata wankin bayi

Fiddausee ce ta miqe tare damata bayanin kowace, dakuma nunamata kamar sunga batta jin dad'ine sabida tunda ta shigo suka ganta wani iri"

Jin hakan yasa malamar umartar Fiddausee n data kamata suje clinic, nanfa ta miqar daita tare da ficewa daga ajin.

A hanya kuwa sai tambayarta take meke damunta amma taimata shiru, abinda kwa Fiddausee bata saniba shine" ita Dije tana tsoron yadda zata gayamata abinda ke damunta kar itama tace cikinne"

Da wannan tunanin suka qarasa clinic d'in. "Alhmdulillah" abinda Fiddausee tace kenan da ta tarar da wata nurse zaune dan batason dr.Fareed sabida takula yanayinsa d'an rainin hankaline da tambaye-tambaye shiyasa bassa shiri dashi gashi baida kirki ko kad'an.

Nanfa nurse d'in ta buqaci Dije taimata bayani, saidai inda gizo kesaqar shine qememe Dije taqi bud'a baki tai magana, saida Fiddausee taitamata magiya sannan ta gayamusu halin da take ciki amma bata sanar dasu rashin ganin al'adartaba sai yanzu.

Jin hakan yasa nurse d'in yin murmushi dan talura kamar dijen kunya takeji, nan tace ce" tashiga bayi ta gyara jikinta tare da bata pad  da sabin pant daman suna ajjiye shi sabida hakan tace ta sanya"

Nanfa Dije tashiga raba ido dan ita batason yadda zatayi anfani da itaba, lura da hakanne yasa Fiddausee karbar kayan tasamata komi tare da nunamata yadda zatai.

Nan ta karba tashige bayain, tafi minti goma aciki sannan tafito, nan nurse d'in ta bata maganin ciwon marar suka fice.

A hanya kam Fiddausee mamaki take tayi yadda Dije sam bata iya anfanin da pad d'in, saidai duba da yadda tace" mata ita d'in 'yar qauyece" yasata d'anyin murmushi, a ranta tace" zaki waye sosai khadija kizama 'yar gayu indai ina tare dake, insha Allahu"

A fili kuwa kallon dije tai tace" amma kikace kina zaune anan cikin kano amma ya akayi baki iya anfani da pad ba meyasa"

Dije tace" ni banta'ba anfani da ita ba shiyasa"

Fiddausee tace" to dame kike anfani?"

Dije tace" ni banayima na dad'e banyiba tun ina qauye yau kusan wata nawa"

Fiddausee ta zaro ido kana tace" meyasa baki fad'awa nurse ba ai da matsala, nidai naji ana cewa masu ciki kanyi wata ko watanni qalilan basu ganin al'adarsu, ko kuma mutum inyana da infection wato cutar sanyi, wanne ke kike dashi?"

Dije tace" ko d'aya kawai inaga Allah ne bai kawoba"

Fiddausee tace" amma dai duk da haka ki fad'a ko agidane, sai aje kiga likita"

Dije tace" shikkenan kada kidamu, na gode da kulawa"

Fiddausee tace" bakomi, wai meyasa naji jiya auta nacemiki auntynsu, kodai wani nata ne kesinki?"

Dije tace" a'a ko d'aya ni ai yayartace haka take cemin ko a inama"

Fiddausee ta gayad'a kai tace" ok, yanzu muje muyi aikin da aunty tayi nasan baki ganeba, gashi kuma tayi test, amma nasan zatamana daga baya"

Dije tace" to" nan suka wuce aji, koda suka shiga auntyn tafita amma tabar sallahu Fiddauseen ta sameta a staff d'in su in anfitosu break.

Suna d'an dudduba matshs d'inne malamin Biilogy dinsu yashigo, wanda shima test d'in ya musu, yana gamawa ya karba ya fice, saidai ko alif dije bata rubutaba banda sunanta kawai da tasanya sai question d'in data kwafa akan fefar.

Bayan fitarsane kuma wani malamin yashigo ahaka har suka fita break yayinda Dije bata fahimce komiba, banda maths d'in daaukai da Fiddausee d'azu.

Suna fita Fiddausee tace" mata tazo ta rakata wajen malamar"

Dije kam catai" bazata iya zuwa sabida har yanzu mararta ariqe take" hakan yasa Fiddausee tafiya ita kad'ai. ta na fita wata yarinya ta miqe tare da matsawa kusa da Dije tana wata yatsina tace" hi stupid girl, wani tsautsayin ne yasa kika shigo makarantar da bata dace dakeba, tunda kinsan kan ba komi acikinsa"

Dije da mararta ke murd'awa amma hakan bai hanata kallon yarinyarba, a girme tasan bashakka yarinyar ta girmeta hatta atsayima bazata auna tsayinta da itaba.kallo d'aya tamata ta kauda kanta.

Ganin hakan yasa yarinyar juyi da kan dije side d'in da take tare cewa" ke har kin isa ina magana ke kauda kai gefe"

Wata yarinyace daje gefensu tana rubutu tace" ke dan Allah zuby meyasa kike hakane dan kinga Fiddausee bata nan ko?"

"Dalla rufewa mutane baki, stupid kawai wacce batason ciwin kantaba, ai saiki tazama ackad'an kina kallo shashasha kawai" wacca aka kira da zuby d'in ce ke fad'in hakan cikin fusata.

Yarinyar datai maganarce tace" Allah yabaki haquri, amma wllh ki canza hali bakyau dai Allah"

Bata bi takanta ba ta juyo inda Dije take tace" ke kuma daqiqiya na dawo kanki, wllh ki fita harkar fiddy dan ita d'in basa'ar kibace kinji ko, ko babanki yayi kad'an"

Dije jin an anbaci babanta aciki yasata miqea a hankali, kallon zuby d'in tai kan tace" dakata malama ni ba sa'arki bace da zan tsaya kina zagina wllh kinyi kad'an bana jurar wannan iskancin kingane, dan haka kishiga taitayinki"

Zuby da sauran 'yan ajin da sukai saranda suna kallon dije amma dayake zubyn bata yaddaba saima matsawa ta qarayi tare da dungure kan dije tace" in anqifa sai yaya, nace uban naki ko kina da abunda zakiyine"

Kafin zuby tarufe baki saijin hannun Dije tai kan wuyanta ta shaqemata shi, take tafara kakarin amai tare da futar da nunfashi d'ai-d'ai tuni 'yan ajin suka tsure ganin yadda Dije ta sauya lokaci d'aya kamar ba iatce mara lafiyar nanba data durqushe d'azu, har aka kaita clinic.

Editing is not allow......

Vote,
Comment,
Like and share.....

*Mrs.Abduul ce*

Fortsett å les

You'll Also Like

1.9M 336K 200
I Became A Virtuous Wife And Loving Mother In Another Cultivation World Original Title - 贤妻良母 (xiánqī-liángmǔ) Original Author - 金元宝 (jīn yuánbǎo) En...
151K 22.5K 104
Name - Fisherman Author - Island in the World Chapter - 82 parts main Mc /MC Gong ၊ Transmigration ၊ rag to rich ၊ Male prag ၊ sweet and warm ၊ no...
442K 47.2K 147
Myanmar Translation of " It's Better to be the Empress Dowager" 135 Chapters + 8 extras Crd September...
67.9K 6.9K 97
"မှားယွင်းသော လက်ထပ်ခြင်းမှသည်..... ကောင်းမွန်သော အိမ်ထောင်သည်ဘဝဆီသို့...(၂)" MM Translation (Just for fun) Chapter 41 in complete "မွားယြင္းေသာ လက္ထ...