BIYAYYAH

By maryamad856

41.8K 1.9K 467

Labari ne akan wasu masoya guda biyu da suka had'u wajen yiwa iyayensu BIYAYYA. 'Kir'kirarran labari ne b... More

BIYAYYAH
BIYAYYAH
BIYAYYAH....
BIYAYYAH...
BIYAYYAH...
BIYAYYAH......
BIYAYYAH....
BIYAYYAH.....
BIYAYYAH....
BIYAYYAH....
BIYAYYAH......
Biyayyah......
biyayyah.......!
biyayyah.....!
biyayyah.....!
biyayyah....!
biyayyah....!
Biyayyah....!
Biyayyah.....!
Biyayyah.....!
Biyayyah....!
biyayyah.....!
biyayyah....! 59-60
Biyayya....61-62
biyayya....62-63
biyayya.... 65-66
part.....67
biyayy.....68
biyayy....69
biyayy....70
biyayya......
biyayya.....
biyayya....73
biyayya......73
biyayy......75
biyayya......76
biyayya....77
biyayya.....78
biyayya.....79
biyayya.....80
biyayya....81
biyayya.....82
Last page....83
Appology/Biyayya....12-14

biyayya.....74

813 46 23
By maryamad856

*BIYAYYA*


Writing by
*Maryam Abduul*

Wattpad@Maryamad856.

💫 *DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*💫

*page....74*

BISIMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM.

-------------Ashraf bai shigoba sai da yai salla shima koda yashigo batta qasan, itakam ta bashi dama akan yasamu yaci dan tasan tabbas yaga tayi zai zauna yacin.

Shima deban yai ya hayewarsa sama, batare da yatsaya wani bata lokaciba.

Cikin wannan weekend din ba laifi sukanyi magana jefe-jefe, kuma ko gaisheshi tai zai amsa amma fa duk wad'annan ayyukan bai janye mata ko d'aya daga cikiba, haka zalika bai bafasa cin abincintaba.



........Yanzu sunyi jarrabawar zangon karatu na qarshe yayinda in sun koma aji biyi zasu ahiga wato ss2.

Wannan hutun da suka samu ta sami mom akan ta tambayar matashi tanason taje taga gida kuma jummai ba lafiya ita hankalinta yahaza kwanciya.

Mom kwa sanin tasan halinsa yasa tace mata" to" aikam ta tambayar mata kuma yabarta saidai wani barin na zuciyarsa na cemasa" yayi missing fa na abinci" amma ba yadda zaiyi.

Dije kam shiri take sosai sanda zata tafi roqon yaya Imran tai akan yakaita, bai musa mataba yakaita.sanda suka je koda tasanar da jummai tare suke dashi sosai ta miqe kamar ba mara lafiya ba.hakan yasa dije fahimtar wani abu saidai tunda taqi gayamata to itama zata 'boye abun aranta amma tabbas zata temakawa qawartata wajen samun cimma burinta.

Kwanata biyar ta juyo a wad'annan kwanakin sosai Ashraf kejinsa wani iri yanaji kamar yarasa wani abu nasa, mai yasama yafara cin abincin nata maiyasa yasabarwa dakansa cinsa gashi yanzu yamazar masa jidali yanajin ko wanne abinci wani iri.

Ba abinda yake ci sai biskit da lemo ko cake da lemo, har dije ta dawo.randa ta dawo kam kamar yai mai dan murna.sai dai ga mamakinsa sai yadinga ganin wayam gashi yau kwananta hud'u da dawowa.

Gashi kuma baida ikon yin magana tunda yace" kada ta rinqa girkawa dashi" yanzu yazaiyi gaahi baison cin ko wanne abinci inba nataba.

Kullum yana zuba ido da hanci amma ba sauyi sai daima uban qamshin turaruka dasuke cikamai hanci, hakan yasa ya rage zaman gidan sai ya koma zaman office sai ya yini yakai dare.

Sanda yaiwa Imran magana cayai" qanwar tasa takoma garinsu" shi kuma baison nuna masa cewa" yagane abinda suka shirya masa" amma sam baijin dad'in kwanakin gaba d'aya.

Imran kwa na lura da duk yadda yake, dan ya lura baison cin abinci daga biskit sai lemo, kuma hakan baisa ya tambayeshiba saima banza da yamasa.

A zahirin gaskiya kuwa Imran d'in ne yace" ta daina har zuwa wani lokaci" shiyasa dije ta daina girki saidai taci kayan qwala damashe ko kuma in yafita ta girka kad'an iya cikinta kan yadawo ta gyara ko ina.



.........Yanzu dije anshiga aji biyu karatu suke sosai ba kama hannun yara, yayinda gefe guda tana cigaba da zuwa wajen Hafsy ga kuma malamin leaaon d'in ta da yake zuwa shima.

Duk randa taje gida kuwa mom da Hanne basa barinta haka.za'a tulu mata kayan anfani nasha da gogawa ko mittsikawa ajiki.

Hanne kam takan qara mata da wasu sirrikan na iya zama da miji.hakan yanamata dadi kuwa sosai.

Zaman dasu kai da hanne nema take gayamata halin data ke ciki wanda shima din saida Hannen ta matsamata sabida taga tayi rama.shine take gayamata halin datake ciki, wanda kullum takeyi kuma ba fashi ga kuma makaranta ga wajen koyan girki shiyasa abubuwa suka mata yawa.

Sosai Hanne ta jimanta hakan wannan wani irin al'amarine wannan meyasa Ashraf bazai yadda da qaddararsaba. Nan dai Hanne ta tausheta akan tacigaba da haquri kamar yadda takeyi wata rana sai labari.

Auta ce tashigo bayan duk tagama jin abinda suke tattaunawa akai, goge qwallar da tazubu akan kumatunta tai tana kallon dije tace" aunty khadija haka daman kike rayuwa agidan ya Ashraf, gaba d'aya ya maidake baiwa kamar ba mutum ba, meyasa bazaki sanar dasu mom halin dakike cikiba meyasa aunty?"

Basusan ma tashigo saidai jin maganarta dasukai daga sama, hakan yasa suka kalli juna tare da kallon inda take dije ce tai hanzarin tarar nunfashinta tare da fad'in " a'a auta bahakabane abinda kike tunani duk ba haka bane, meyasa zan gayawa su mom alhalin yana da 'yancin da zaisani duk abinda yaga dama kar ki manta ni dinfa matarsa ce dan haka yana da ikon juyani duk yadda ransa yakeso"

Auta ta sauke ajjiyar nunfashi kan tace" wannan sam ba adalci bane aunty tabbas qarshen wahalarki tazo dan bazan lamuntaba zan sanar da dad duk abinda ke faruwa"

Cikin sauri dije ta riqeta tare da fad'in " a'a auta dan Allah kada ki kuskura koda wasa naji maganar nan ta fita, kimin alqawari dan Allah"

Auta ta kalleta ciki da takaice kan tace" haba aunyy meyasa zakimin hakane wannan sam ba abinda yakamata bane, kinsan kwa me yaya ya aikata ai bai kamata aqyaleshi hakaba, angaya mai qiyayya haukace kema ai basan nashi kike ba amma me sai kika daure kika haqura kika rungume qaddara, wllh aunty saina gayawa dad abinda ke faruwa"

Janyo hannuta tai da qarfi tare da had'e rai kan tace" bana cemiki banason maganar nan ta fitaba, meyasa hakane auta meyasa bakki jin magana, ni akwa koma menene dan haka ba ruwanki, koba komi shi d'in mijina ne kuma inason kayana kada ki kuskura kiyi abinda zai rabani dashi na gaya miki"

Auta da ranta yagama 'baci batare data qara cewa komiba ta fice daga d'akin.

Hanne ce ta kalli dije kan tace" anya kina ganin zata qyale maganar nan kuwa?"

Dije ta sauke ajjiyar nunfashi kana tace" bazata fad'a ba auta tanasona kuma bata son bacin raina na tabbata tunda taga na bata rai to bazata taba fad'a ba"

Hanne tace" ok yayi amma dai kije ku qara magana da ita, yawwa naji kince kina son Ashraf da gaske kike?"

Dije ta kalli Hanne tare da runtse ido kan tace" aunty tabbas inason ya Ashraf amma zuciyata na qaryata hakan badan komi naceba inasonshiba saidan bayadda zanyi dan shi d'in mijinane kuma nason bazan ta'ba rabuwaba muddin ba mutuwaba to danme bazanyi qoqarin sawa kaina sonshiba, saidai tsanar dayake min tana hanani yarda da son dana kemasa, aunyy Hanne ina sonshi har cikin raina duk dana son shi basona yakeba"

Hanne taja nunfashi kan tace" turqashi wai hakane amma kiyi qoqarin danne wannan son nasa kada ki kuskura yasan da cewa kinasonsa dan haka zai qara jamiki wani baqin jinin ne da kuma wulaqanci, dan haka ki cigaba da addu'a wata rana sai labari kamar yadda nasha gaya miki"

Dije ta gyad'a kai kan ta miqe tace" bari naje wajen auta"

Hanne tace" to kidai lalla'bata sosai dan gaskiya banson ace su dad susan halin dakuke ciki, gwara dai har Allah ya had'a kanku zaisa su samun farin ciki sosai."

Nan dije ta fice tana shiga d'akin auta ta taddata zaune tayi ta gumi, cire mata hannayen tai kan tace" bakyau ta gumi dai"

Auta ta juyar dakai gefe batare da tace da Dijen qalaba.

Ganin hakan yasa dije juyawa 'barin da fuskarta take ta tallafota kana tace" kiyi haquri autar mom, kisani banson duk wani abu da zai hanasu samun farin ciki, yanzu mekike tunani idan suka son hakan daga gareshi, wllh nasan ransu ba matuqar 'baci zaiyiba, shiyasa nace kimin alqawari bazaki fad'a ba dan Allah"

Auta tai saqaqe kan tace" shikkenan amma wllh suk randa yakaine bango saina tona asiri sai dai kuwa rannashi ya 'baci"

Dije ta buge mata baki kan tace" au har naso mom da dad ai kam danaki yafi kowa samun matsala"

Nan suka sa dariya.

Mom ma dataga ramarta tayi mamaki sosai dan tayi duhu ta rame sabida tsabar wuyar aiki da takesha, amma duk yadda mom taso tagayamata meke damunta qi tai, ba yadda ta iya haka ta qyaleta amma qasan zuciyarta namata wani iri " kodai Ashraf namata wani abunne basu saniba?" wannan tambayar takan yiwa kanta.

Koda dije zata tafi sai da auta tabata wani agogo wanda tajima da siyanshi tana taso ta kaimata bata sami damaba, sai yanzu da tasamu dijen tazo.


Sosai dije take duk wasu ayyuka nata ga kuma karatu datake yawan tilawarsa duk dacewa anyi hutu amma hakan baisa ta yada karatunba.

Kuma yanzu kullum take zuwa wajen Hafsy bata fashi duk wani abu da zaisa taqi zuwa bata fatansa.dan baqaramin jin dad'in zama da Hafsy takeba.

Takoyi abubuwa da dama a wajenta takoyi zaman takewar rayuwa yanzu itama kanta yafara wayewa.uwa uba ga zaman dasuke da Fiddausee itama bata barinta haka.

Takanas Hafsy taje ta kwasowa dije english wears da kayan make up akan tadinga yi agidanta dan tattaro hankalin oga Ashraf.

Sai dai duk wani abu da dije zatai shi sam baya gabansa, abu daya kawai yadamu dashi shine abincinta wanda yanzu sam yagaza samun haka, bai kumason yazai yiba.

Sai dai duk sa'in daya ra'beta yakanji qamshin jikinta na matuqar yimasa dad'i, hakama qamshin da yazauna agidan wanda kullum ake turara gidan na matuqar yimasa dad'i amma shi yafi karkata ga abincin da yake burin samu yaci.





*********

Bayan sati uku.

Yawan aikin da dije keyi yasa mata ciwon jiki sosai ga bayanta badama tayi wani yinquri sai ya amsa.

Ranar laraba kam da zazza'bi ta kwan ga ciwon kai da jiki, bata iya ta'buka komi aranar taga tashin hankali dankwa cikin dare wani matsanancin ciwon marane ya turnuqeta sunan Allah kawai take ambata sai na iya da mom. Fad'i take" zata mutu su ceceta" ahaka har gari yawaye.

Ashraf da yagama shirinsa na fita, koda yasakko qasa kamar kullum dinning wayam hakan yaqara 'bata ransa kodai tagano yanacine?"

Ya tambaye kansa, wajen mota ya nufa sai yaga itama ba'awankeba kuma jiya saida ya jaddadamata akan ta wanke da wuri dan zai fita da wuri zasuyi meeting da wasu manyan baqi, amma shine tayi kunnen qashi ta qeqashi hakan ko"

Horn shida yai amma ba alamar zata fito, hakan yasa cikin fishi ya haura saman, qofar d'akin ya tura Allah yaso bata sa key ba, kwanci ya hanhota can qarshen gado ta rufa da bargo "lallaima wato bacci takeyi" juyawa yai ya sauka qasa kitchen ya fad'a tare da bud'e fridge ya d'akko gorar ruqan sanyi wanda har yafara qanqara.

Yana zuwa ya yaye bargon ya d'aga jarkar ya tuttula mata akan fuskarta, dije kam tuni ta saki wata ajjiyar zuciya tare da sakya lumahe idanuwa.

Ganin hakan yasashi yaye bargon nata gaba d'aya, runtse ido yai dan daurin qirjine ajikinta kuma har zanin yafara kwancewa. Tunda tai wanka ta kwanta bata samu tasa kayanba.

Ganin bata motsaba yasashi tabata sai dai mai shiru yaji hakan yasa shi fara kiran sunanta amma shiru ba amsa, hannunsa yasa akan hancinta nan yaji bata nunfashi sai alokacin yakai hannunsa jikinta dan yaji fuskarta da zafi ai kam zau yajishi.

Innalillahi yahau anbata, nan ya shiga bayinta ya debo ruwa ya watsa mata amma sam ba alamun dawowar nunfashin nata.take jikinsa ya mutu kardai 'yar mutane ta mutu yasalma yanzu yazaiyi?"

Iya qololowa hankalinsa yatashi yarasa wani taimakon zai bata haka ya daure yasa mata dogowar riga kana ya kinkimeta sai asibiti.

Allah yasoshi dr.Saleem abokinsa bai dade da dawowaba daga saudiya hakan yasa baisha wahalar ganinsaba shi yakar'bi dije d'aki na musamman aka bata, tare da qoqarin samu kanta.

Sai alokacin Ashraf yasamu nutsuwar fidda wayarsa daga aljihu ya danna number din Imran.

Ringin d'aya ya d'aga, cikin dasassheyiyar murya ya gayamai halin da ake ciki har asibitin dasuke.

Dayake Imran d'in yasan asibitin hakan baisa yasha wahalar gano wajenba cikin mintina qalilan sai gashi a asibitin.

Dr.Saleem iya rudewa yayi dan sosai abubiwan dake damunta suka daga mai hankali garin yaya yarinyarta da ita mai yajawo mata hakan.

Fuskarsa ba annuri yadube Ashraf kan yace" gaskiya dai abinciken danai na gano matsaloli ba kad'an ba, wanda da yawa zance da sakacinka ko kuma nace da rashin kulawarka gareta, meyasa Ashraf meyasa kake da taurin kai na baka shawarwari ba kadanba amma meyasa kake da taurin kai haka"

Ashraf da zuciyarsa ke buguwa amma duk da hakam sai ya waske ya kalli abokin nasa yace" kaga inzaka fad'i meye matsalar to kawai kafad'a sai wani kwana-kwana kake"

Saleem da Imran suka kalli juna yayin da kuma dr.Saleem ya kalli Ashraf yace" wow yayi sai izzarka tasa na fada ai, bazan fad'i meye damuwar taba har sainaga ahlinta"

Yana gama fad'a yai waje tare da barin Ashraf saqaqe yana kallonsa. Imran ma ficewa yai yabar masa office d'in yana jinjina wannan qarfin hali irin na Ashraf.

Wayarsa ya fidda daga aljihu ya danna layin mom, aikam ringin biyi tai ta daga, nan yashiga sanar mata da abinda ke faruwa, da asibitin da suke.

Cikin rudewa mom takira dad tace" duk abinda yake ya baro yazo asibiti yanzu-yanzu" hankalin sa tashe yace " to"

Mom suna gama wayar da dad ta yafa mayafinta ta fice, tana qoqarin fita auta na shigowa dan taje gidansu Imran, ganin halin da mom take ciki yasata bin bayanta, mom nashiga gidan baya itama ta shige, nan driver yajasu.

Suna shiga asibitin batare da sungama parking ba auta tahau tambayar meke faruwa, mom ko takanta bata biba tai cikin asibitin hakan yasa itama auta take mata baya, sai dai zuciyarta fal cike da tambayiyi kala-kala, me yake faruwa?, me yakawosu asibiti kuma?, waye ba lafiya, kodai dad ne?" haka tai ta saqe-saqenta har suka shiga ward d'in

Imran suka hanga zaune kan wani bench da sauri mom ta qarasa tana fad'in " ina 'yata tana ina gayamin?"

Imran ya d'ago da sauti tare da riqe hannun mom yace" tana lafiya mom ki kwantar da hankalinki tana dakin hutu bata fatka bane"

"Innalillahi mom tahau fada, kada acemin 'yata ta mutu Dan Allah "

Imran ya dafa ta kan yace" bata mutuba mom tana nan da ranta"

Sai alokacin auta tasan meke faruwa wato dije ce ba lafiya, yasalam" ta furta.batare data yi qwaqqwarar maganaba dad ya qaraso wajen da suke tare da tambayar lafiya?"

Nan mom ta sanar mai da abinda ke faruwa" " ya salam kawai yake anbata"

Ganin harda dad awajen yasa Imran cewa" su shiga office d'in "

Ashraf na zaune inda suka barshi yana danne-danne a waya suka shigo. Ko kallon inda yake mom bataiba kujera taja ta zauna, yayinda shi kuma yasauka ya bawa dad kujerar da yake kai, nan dad ya zauna. Yana gaishesu amma dad ne kawai ya amsa mom kwa banza tamasa.

*Wai nanma bataji meke danun 'yarta taba, wai inaga tasani"*

Editing is not allow......

Vote,
Comment,
Share and Like....

*Mrs.Abddul ce*

Continue Reading

You'll Also Like

694K 72.6K 99
Description လျောင်ချင်းချင်းနိုးလာတဲ့အခါနှစ်သက်ခြင်းမခံရတဲ့ဇနီးငယ်လေးအဖြစ်ကူးပြောင်းသွားတယ်။ အင်ပါယာနန်းတော်ထဲဝင်ပြီးနောက် မနှစ်သက်ခံရတဲ့လျန်ရိတစ်ယော...
1.1M 161K 154
စစ္သူႀကီးမ်ိဳးရိုး၏ ပဏာမသမီးေတာ္၊ ျဖဴစင္၊ ရိုးသား၍ အလိမ္အညာခံရလြယ္ေသာ၊ မင္းသားသင္းအား ရူးရူးမိုက္မိုက္ခ်စ္ႀကိဳက္မိသူ သူမ သူ႔ဇနီးမယားအရာရေအာင္ ႀကိဳးပမ...
1.9M 336K 200
I Became A Virtuous Wife And Loving Mother In Another Cultivation World Original Title - 贤妻良母 (xiánqī-liángmǔ) Original Author - 金元宝 (jīn yuánbǎo) En...
348K 62.9K 107
Original Title : 当年万里觅封侯 English Title : Those Years in Quest of Honor Mine Original Author : Man Man He Qi Duo (漫漫何其多) Original publisher : jjwxc C...