BIYAYYAH

By maryamad856

41.8K 1.9K 467

Labari ne akan wasu masoya guda biyu da suka had'u wajen yiwa iyayensu BIYAYYA. 'Kir'kirarran labari ne b... More

BIYAYYAH
BIYAYYAH
BIYAYYAH....
BIYAYYAH...
BIYAYYAH...
BIYAYYAH......
BIYAYYAH....
BIYAYYAH.....
BIYAYYAH....
BIYAYYAH....
BIYAYYAH......
Biyayyah......
biyayyah.......!
biyayyah.....!
biyayyah.....!
biyayyah....!
Biyayyah....!
Biyayyah.....!
Biyayyah.....!
Biyayyah....!
biyayyah.....!
biyayyah....! 59-60
Biyayya....61-62
biyayya....62-63
biyayya.... 65-66
part.....67
biyayy.....68
biyayy....69
biyayy....70
biyayya......
biyayya.....
biyayya....73
biyayya......73
biyayya.....74
biyayy......75
biyayya......76
biyayya....77
biyayya.....78
biyayya.....79
biyayya.....80
biyayya....81
biyayya.....82
Last page....83
Appology/Biyayya....12-14

biyayyah....!

768 41 1
By maryamad856

💎💎💎💎💎
💎💎💎💎
     💎💎💎
        💎💎

*BIYYYAH*

   *Story...writing*
By
   *Maryam Abdul*

       Wattpad.
#miss #gentle

*Typing.....*⌨

💫 *DA BAZARMU WRITERS ASS*💫

We are here to make you happy.... Smile and educated to realized that we are the best among all..... *DABAZAMU MUKE TUN'KAHO*💃💃

Da bazarmu writers ass. Fatan alkhairi ga kowa da kowa.... Ku kasance cikin farin ciki da annushuwa na har abada.
 

   Ina matu'kar godiya ga addu'arku gareni my *Fans*....Allah ya bar zumunci....ya barmu a tare...ameen.

*page.... 49-50*

Bismillahir rahmanir raheem.

--------Falon d'akin ta fara gyarawa daga nan ta wuce band'aki sai da ta gama duk abinda zatai tsaf sannan ta shige bayi ta watsa ruwa.kan gadon ta ta zauna tare da fad'in" wash, wannan aiki ko masifa?"

Tana nan zaune taji turowar 'kofar dakin nata, d'aga kai tai ta kalli 'kofar dan a tunanin ta auta ce, sai dai sa'banin hakan da ta gani.

Yana sanye cikin kayan shan iska kayan sun yimishi kyau sosai..." Ki fito falo" ya fad'a yana me juyawa.

Cunu baki tai tace" kai wannan jaraba ba za'abar mutum ya huta ba, daga wannan sai wannan"


Kamar yadda yace mata" ta sameshi a falo" hakan kwa akai yana zaune yana shan coffee d'in da ya amso awajen mom kallon ta yai yace" yawwa inaso ki bud'e kunnuwanki da kyau kijini, Imran zaizo Dan haka be careful, idan kuma kika kuskura kikai abinda ban lamunta da shiba to kiyi kuka tun kan na kamaki, kin san Allah......"

Bai 'karasaba ta katseshi da fad'in" nikam na sanshi....tunda dai ina bauta mai" ta fad'a tana murgud'a baki.

Sakin baki yai yana kallon ta kafin ya matso kusa da ita yace" oh kinyi girman da kafin a gama magana kin 'karasa da taki ko?", to wllh ki kiyayeni "

Turo baki tai tace" nifa duk abinda kacema ban fahimci ko d'aya ba sabida hankalina sam bai wajen"

Da mamaki ya kalleta ta kafin yace" kina nufin na sakya mai-maitawa kenan?"

Gyad'a mai kai tai tace" ehh man sabida ba abinda na gane aciki"

Matsowa ya kuma yi daf da ita tare da Jan kunnanta d'aya kafin yace" bazan mai-maita ba, abinda kikaji nace kiyi aiki dashi Wanda bakijiba hukunci yasa ki fahimta...sannan idan har wannan tasisin bakin naki bazai sami ladaf d'in shiru ba to zan sai tashi nan bada dad'ewa ba, Dan haka in kinaso tsira da shi to kisa ya nutsu"

Turo bakin ta 'karayi kafin tace" amma ai kowa da irin bakin da aka tsagamai ko?, kuma ai ba a hana mutum da magana...Allah ya gani ni daman can haka nake ko Iya ta shaida ce ma"

Bakin ya falla da d'an yatsunsa biyu kafin yace" yanzu ai ya fara mutuwa ko, wannan ma kad'an kika gani"

Cikin sauri ta Sosa wajen tare da fad'in " alqur"'an da saura sai randa na bar duniya wannan kyakkyawan bakin zai mutu"

Tana ''karasawa ta mi'ke a 360 tai d'akin ta, fad'i take" wai Allah ya soni nasha ai yau dana shiga uku...car ubancan wai namiji da suna hajara"



Shikam da kallon mamaki ya bita dashi lallai wannan yarinyar wato taga makwancinsa kenan....lallai ba shakka  sai ya gyara mata zama"

Ya 'kara Jan tsaki tare da yin murmushi kafin yace" sai rashin kunya ga kuma shegen tsoro, zamu gaurayane"


Yana nan kwanci yaji wayarshi na 'Kara, screen d'in wayar ya kalla sunan Imran ne ya bayyana tsaki yaja kafin yace" maye saida kazo d'in " yana gama fad'a yana sauka 'kasa.


A falo ya tadda shi ya danne-dannen Waya kallonshi yai tare da Jan tsaki yace" aikin banza sai da kabiyonin ko?
Kai dai wllh in mayene da tuni kaci jama'a da yawa"

Imran yai murmushi yace" ehh d'in anzo wajenka nazo ko kuwa.....au kai bakason mayen bane."


Harararsa yai yace" kai kasani kuma...sai kace kanka da kanka"

Imran yaja tsaki yace" ni dai ina mom da 'kanwa ta?."

"Ban saniba" ya bashi amsa ata'kaice.

Suna haka auta ta shigo falon ganin ya Imran zaune yasata washe baki game da fad'in " lah yaya saukar yaushe?"

Murmushi yai yace" yanzun nan 'kanwata, ina mom da auntyn naki?"

" mom tana d'aki, aunty kuma bara na kirawota inaga batason ka zoba"

" OK gdy nake 'kanwata" ya fad'a yana murmushi.

Shikam Ashraf inbanda harara ba abinda yake banka musu.

Nan dai auta ta haura part d'in mom ta sanar da ita zuwan Imran, sannan ta haura 'bangaren Dije.

Tura 'kofar tai tare da sallama, tana zaune tayi ta gumi tunanin halin da take ciki take, ita ayanzu ba'abinda tafiso illa taganta gata ga iyan ta.

Bata son sanda auta ta shigo ba sai jitai an dafa ta tare da fad'in" aunty lafiya me yake damunki?"

Dije ta kalleta tare da murmushi tace" lah bakomi me kika gani?"

Auta tace" naga kinyi tagumi kina tunanin har bakison na shigoba"

Dije tai murmushi kana tace" bakomi autan mom"

Auta tace" shikkenan kizo muje ya Imran yazo"

Cikin hanzari ta mi'ke tare da fad'in " da gaske kike, yana ina?"

Auta tace" da gaske man, yana falo"

Nan suma rankaya zuwa 'kasa.koda suka 'karasa sungama gaisawa da mom nan aka shiga sabuwar gaisuwa atsakanin Imran da dije sai washe baki takeyi kamar gonar auduga.

Imran ya kalleta yace" 'kanwata fatan komi lafiya ko?, ba wata matsala dai ko?"

'Daga kanta tai alamar nazari kafin tace" ehh baza a rasaba kam gaskiya"

Imran ya gyara zamansa yace" to 'kanwata meya faru kuma?, fad'a min inaji"

Dai-dai lokacin Ashraf ya tsoma baki had'e da fad'in" wuce kije ki kawo mai ruwa da lemo" ya ''karasa fuska a had'e.

Nan ta mi'ke tana zun'buro baki had'e da gunguni.

Imran ya kalleshi yace" kodai akwai abinda yake faruwane, Dan naga kana 'ko'kari hanata magana, ko akwai abinda kake mata ba dai-dai ba?"

Dalla mai harara yai yace" ban sani ba ni ina ruwana ma da maganar ku, can ta matse muku" ya ''karasa fuskar dai a had'e.

Imran yace" kai ma ta matsema kuma bari mom tazo sai na gayamata in yaso ita ta binkici koma meke faruwa"

Ashraf ya d'an rage had'e fuskar kana yace" kai wai meyasa kake da matsalane, kabari ta dawo ba saika tambayeta ba"

Imran yace" ah basai na tambaya ba mom ma ta ishe komi "

Ashraf ya dallah mai wata uwar harara kana yace" sai kai ta fad'a ai, Dan Allah kar kabari 'kuda ma yariga ka"

Dai-dai lokacin dije ta dawo hannun ta d'auke da lemo da ruwa a try Dan auta ce ta bita ta jera mata komi.

Imran ya kalleta ta yace" masha Allah sannu 'kanwata, amma nifa girki nazo ci ba ruwa  nazo shaba"

Dije ta gyad'a kai tace" yanzu za'a d'ora yau hannen ce bata jini dad'i tun safe shiyasa komi bai tafiya da sauri Dan ma mom na temaka mata shiyasa ba'a gama na Daren ba"

Imran ya langabar da kai yace" nifa ba na 'yar aiki da mom zanci ba na amarya zanci, ke zaki dafan"

Dije ta gwalo ido tace" kai alqur'an ban Iya ba, sai dai kaci jagwalgwalo, ni in banda tuwo me na Iya sai d'an malele in zakaci inma"

Zaro ido Imran yai yace" kai 'kanwata ba abinda kika Iya gaki ga mom baki cewa" ta rin'ka koya miki"

Dije ta girgiza kai tace" ni bana cewa haka, me zanyi da wani girki wahala ce fa kawai"

Imran yai murmushi yace" ai kam ke zakiyi dashi...amma kisha kuruminki zaki Iya har kifi mom ma iyawa"

Ashraf yaja tsaki dayake yana jinsu yace" daman me zaki Iya kina fama da rashin kunya da fitsara, kai kuma ka sani ba Wanda zai kamo mom a Iya girki balle kuma wannan kuchakar"

Dije jin hakan yasa ta saurin cafewa da fad'in " alqur'an ni ba kucaka bace, sai dai in kai....."

Bata 'karasa ba ya falle bakin nata, aikam wannan karan taji zafi sosai fiye da yadda ta mata d'azu, kallon tabyai yace" gobe ma kya kuma"

Aikam Dije ta saki kuka, dai-dai nan mom ta sako kai " ah lafiya kuma Khadija, me yafaru kike kuka"

Kamar wacce take jiran a tambayeta tai carab tace" ba ya Ashraf ne ya mari ne ba akan na kawo lemon da bayaso ni kuma nace" wanne za'a kawo" shine ya haune da fad'a" wai da can banson Wanda yake shaba" Dan nace" eh" shine ban san hawa ban san sau kaba naji kawai ya falle ni da mari a duka kumatuna"

Jin hakan yasa mom saurin 'karasowa ta d'agota kana tace" meye haka Ashraf, mari kuma banso gaskiya ka kiyayeni daga tayi kuskure haka daman kake dukanta ban saniba to wllh tun wuri ka sauya hali, ai ita ba jaka aka kawo maba, itama mutum ce kamar kai"

Imran ya dube mom yace" kai-kai mom harda shatin yatsu wajen yayi"

Jin hakan yasa mom saurin dubawa...shiko Ashraf kallon Imran yai kana ya juya yana kallon fuskar Dijen da shi Sam bai sa hannun sa a wajen ba amma ji uban sharrin da ta mai har mom ta fara yimai fad'an da ba gairaba dalili, gashi shi kuma wannan uban d'an zugan har da cewa" wai da shatin yatsunsa" lallai dole zaiwa tufkar hanci.


Vote
Comment and
Share.....


*Miss Gentle ta kuce....*

Continue Reading

You'll Also Like

1.5M 190K 123
အေဒီ ၇၉ ခုနှစ် .. ပုံပေမြို့.. ရောမအင်ပါယာ ဒဏ္ဏာရီမဟုတ်တဲ့ ရာဇဝင်ထဲက အဖြစ်အပျက်လေးတစ်ခုလား ဒါမှမဟုတ်.. ရာဇဝင်တွင်မကျန်ခဲ့တဲ့ ဒဏ္ဏာရီဇာတ်လမ်းလေးပဲလာ...
39.6K 2.9K 24
ʙᴏᴏɴ ᴛʜᴀᴛ ᴄʜᴀɴɢᴇꜱ ᴇᴠᴇʀʏᴛʜɪɴɢ ᴏʀ ᴡɪʟʟ ɪᴛ? ɪꜱ ɪᴛ ᴀ ʙᴏᴏɴ ᴏʀ ᴡɪʟʟ ɪᴛ ʙᴇᴄᴏᴍᴇ ᴀ ᴄᴜʀꜱᴇ? ᴡᴏᴜʟᴅ ᴛʜᴇ ᴄʜᴀɴɢᴇ ʙᴇ ɢᴏᴏᴅ ᴏʀ ɴᴏᴛ? ᴡɪʟʟ ᴛʜᴇ ᴛʜɪʀꜱᴛ ᴏꜰ ᴛʜᴇ ᴀɢᴏɴʏ ᴏꜰ ᴀ ᴍ...
1.9M 336K 200
I Became A Virtuous Wife And Loving Mother In Another Cultivation World Original Title - 贤妻良母 (xiánqī-liángmǔ) Original Author - 金元宝 (jīn yuánbǎo) En...
348K 62.9K 107
Original Title : 当年万里觅封侯 English Title : Those Years in Quest of Honor Mine Original Author : Man Man He Qi Duo (漫漫何其多) Original publisher : jjwxc C...