BIYAYYAH

By maryamad856

41.8K 1.9K 467

Labari ne akan wasu masoya guda biyu da suka had'u wajen yiwa iyayensu BIYAYYA. 'Kir'kirarran labari ne b... More

BIYAYYAH
BIYAYYAH....
BIYAYYAH...
BIYAYYAH...
BIYAYYAH......
BIYAYYAH....
BIYAYYAH.....
BIYAYYAH....
BIYAYYAH....
BIYAYYAH......
Biyayyah......
biyayyah.......!
biyayyah.....!
biyayyah.....!
biyayyah....!
biyayyah....!
Biyayyah....!
Biyayyah.....!
Biyayyah.....!
Biyayyah....!
biyayyah.....!
biyayyah....! 59-60
Biyayya....61-62
biyayya....62-63
biyayya.... 65-66
part.....67
biyayy.....68
biyayy....69
biyayy....70
biyayya......
biyayya.....
biyayya....73
biyayya......73
biyayya.....74
biyayy......75
biyayya......76
biyayya....77
biyayya.....78
biyayya.....79
biyayya.....80
biyayya....81
biyayya.....82
Last page....83
Appology/Biyayya....12-14

BIYAYYAH

4.2K 114 3
By maryamad856


  
   *BIYAYYAH*

      
By

    *Maryam Abdul*
   

💫  *DA BAZARMU WRITTERS ASS*💫

  
  We are here to make you happy....smile, educated and to realized that you are the best among all.... *DA BAZARMU MUKE TUNK'AHO*💃💃

*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM*

INA RO'KON ALLAH DAYA BANI IKON ISAR DA SA'KON DANA KESON ISARWA...ALLAH YASA NAFARA A SA'A...YA KUMA BANI IKON KAMMALAWA KAMAR YADDA NAFARA...AMEEN.

*page....1-8*

   

   
...............Gudu yake sosai kamar zai tashi sama, can k'asan zuciyarsa kuma wani irin tuk'uk'in bak'in ciki ne ke tashi "Me ya sa? Dan me Daddynsa zai yi masa haka? Ta yaya ma zai had'ashi da kucakar yarinya wacca sam ba ta da aji?" Wad'annan tambayoyin ya dinga yi wa kansa. Wayar shi ce ta hau ruri, sai da ya yi kusan sakan biyar sannan ya duba kan gilashin wayar dan ganin waye ke kiransa a cikin wannan mood d'in da yake ciki? Wani wawan tsaki yaja ganin sunan IMRAN ya bayyana akai ɓaro-ɓaro. (Abokin shi ne kuma tare  suka taso, duk abin da ke damun d'aya to zai gayawa d'ayan dan su haɗu su samar wa da kansu mafita). Ya yi kusan sakan shida sanann ya ɗaga tare da karawa a kan fatar kunnensa. Ko da ya d'aga d'in bawai ya yi magana ba ne a'a ya yi masa shiru ne, ganin shirun ya yi yawa kuma ga kud'i na tafiya a aikin banza ya sanya wanda ya yi kiran yin magana, dan yasan ko kwana za su yi a haka in bai ga damar yin magana ba ba zai yi ba.
  
  "Ya yi kyau abin da kake yi ASHRAF, kai kana ganin hakan shi ne daidai?" Imran ya fad'a cikin zafin rai.

Iska ya furzar mai huce kafin ya ce, "So meye ruwanka a ciki? Ni dai na riga da na rantse, wallhi duk wacce ta yi gigin aurena sai ta gane kurenta, me ya sa baku gane wa ne?"

Imran ya girgiza kai tamar yana gabansa kafin ya ce, "Wai kai me ya sa kake da taurin kaine Ashraf? Haba ya kamata ka yi biyayya ga Daddy ko bakomai mahaifin kane ai"

"Tun yaushe a ke yin biyayyar, me ya sa ni ma baza a bar ni na zab'i zab'ina ba? Haba zamani fa ya canja IMRAN" ya fad'a ransa a matuƙar ƙolukowar b'aci.

Imran da shi ma ransa ya soma b'ace sosai ya ce, "Wai kai wani irin mutumne ASHRAF? Me ya sa kake san canja wasu halaye naka? Na tabbata yanzun a ka ce ka fito da wacce kakeso d'in cewa za ka yi babu, to yaya kakeso a yi maka?"

"A bar ni har zuwa lokacin da za'a haifa mini matar da zan aura, ni fa na gayama har yanzu ba a haife ta ba, balle ma kusa ran aurar da ni, so plz kabar ni na huta"
     Yana gama fad'in haka ya datse kiran, domin a yanzu kansa wani irin sarawa yake yi masa, shin ta yaya zai b'ullo wa wannan al'amari, sam Daddy yak'i ya fahimce shi. Da wannan tunanin ya k'arasa wani katafaren gida, wanda ni kaina sai da na tsorata da ganin shi, daman akwai irin gidajen nan anan garin KANO, cab wai, ai bazan iya fasalta muku gidan ba domin sai yajuyarmin da hankali, amma gaskiya ya had'u yaji naira sosai.

Horn biyu ya yi mai gadi ya wangale mai tangameman gate d'in, cab ai anan na dad'a tsurewa, lallai wannan gida ya gaji da had'uwa, wajen parking space yayi nan naga motoci kala-kala, wasuma ban tab'a ganin irinsuba anan kasarba, yana gamawa naga yanufe wata k'ofa wacce zata sada shi da ainihin gidan, hoo hoo kunsan me nagani readers hmm lifter ce wacce se ka hau zata kaika ainihin gidan, kai alqur'an gidannan ba a KANO yakeba, cab lallai.

Cikin isa da tak'ama ya shiga falon, wata kyakkyawar mata nagani zaune a falon tana cin kayan marmari, a k'alla zata kai shekara 45, sedai zaka iya rantsewa shekarunta basufi 32, domin tanacin me kyau da kuma samun waje me kyau, cikin farin ciki da walwala tace "ah my son har ka dawo?"

Zunb'oro baki ya yi yace "wllh mom duk kun gajiyar dani, nifa aikin nan yana wahalar dani, kawai a bari na k'ara samun k'arfin k'ashi"

Dariya ta yi tace "lallai my son yanzu har a wannan k'warin k'ashin kake buk'atar dad'in wani k'warin" ta k'arasa tana me kama dan tsansa.

"auch! " ya fad'a tare da rik'e wajen cikin shagwab'e fuska yace "haba mom da zafi fa, salon kawai ki karya d'an autan naki ko"

Kafin ta yi magana wata kyakkyawar yarinya, wacce ba zata wuce shekara goma sha d'aya ba, ta yi sallama , kamarsu d'aya da matar dake zaune a falon, sedai ita bak'ace amma irin black beuty d'innan, cikin shagwab'a ta k'arasa tare da d'anewa kan cinyar mom d'in tasu tace "wash! wllh mom nagaji, yau zanine akai akan wai banyi assigment ba, kalle wajen yadda yai" tak'arasa tana bud'e mata hannunta.

"wai-wai garin yaya haka, baby, meyasa baki bawa yaya ya miki aikinba?"

Zunb'uro baki tai tace "nafa bashi, tun jiya da safe shine yace wai baze sami damar yiminba, daman aiso yake azanine kawai mom, kuma Allah ni kiramamin"

Sai a sannan ya d'ago ya kalleta, dan tunda suka fara hirarsu hankalinsa na kan waya yana game .

"yo ai kema zaki iya ramawa base kinsa mom ba, shashashar banza, kullum se wasa ki ka iya amma ba karatu, aini gwara da ma aka zane kin, inama sun farfasa miki jiki"

Cikin murya kamar tame kuka tace "kinji ko mom, kuma alhalin ina karatu"

Mom ta kalleta tace "k'yaleshi baby, yayi ya gama kuma sena rama miki dukanki"

"yeee shiyasa nakesonki mom, I love you ke kad'ai"

Ashraf ya kalleta yace "dallah tashi kiban waje mummunar kawai, me za'ai da bak'in mummuna kamar ki" ya k'arashe yana gintse dariyarsa aciki, dan yasan halinta battason wannan kalaman dayake gayamata.

Cikin d'aga murya ta sake  kuka tare da fad'in  "ai wllh kaine dai mummuna aljanin kawai"  tana k'arasa wa ta arta aguje, dan kar ya dank'eta a hannu, dan tasan besan ace mai yana kama da aljanu.

"Yarinya zan kamakine, wato kinga wajen kwana na ko?" ya fad'a.

Mom tai murmushi tace "kai kaja ai, kafara tsokanarta, yawwa wai kam kaje wajen yarinyar nan kuwa my son?"

Kamar wanda aka kiramai mutuwa haka ya murtuke fuska kamar betab'a dariya yace "a'a ba yanzuba, se na kammala wasu ayyuka" yana gama fad'a ya mik'e tare da sake fad'in "is tym for my sleeping, bye" ya haura sama.

Ita kam k'wafa tai tare da girgiza kai, da jinjina hali irin na ASHRAF, sam bayajin magana ko kad'an, batason yaushe ze gama hankaliba.

Koda ya shiga b'angarensa kai tsaye toilet ya fad'a, yayi kusan 30mnt a ciki, kai ka rantse canza fata zeyi.

Wasu lafiyyayyan mayuka naga ya fara shafe jikinsa dasu, take wani k'amshi ya gauraye d'akin.

A hankali ya bud'e wadrof d'in tasa wacce take cike mak'el da kaya, kuma ko wanne ajjiye cikin tsari, b'angaren kayan shan iska ya mik'a hannayensa, nan ya zaro wasu pink colour d'in riga da wando amma wandon three quater ne se rigar da take shimi.

Seda ya gama shiryawarsa tsaf sannan ya sakko falon k'asa dan bawa cikinsa hak'k'insa.











******** K'auyen Rimin gado, tafe na ke ina hangen bishiyoyin da suke ka d'aw, ji nake ina ma na zauna nai ta kwasar iskar ALLAH ta a'la. can dai na dad'a mek'awa dan kutsawa cikin garin dan naga wace wainar ake tuyawa.

K'auyen b'utu_b'utu dake cikin garin Rimin gadon, nan na nufa. wani d'an madai daicin gida na tsaya, sedai gidanfa tam masha Allah, domin tun daga wajen gidan zaka san yana buk'atar gyara, domin ko fulasta babu a ka tangun gidan. ciki nashiga nanfa nasakke bud'e ido dan abinda na hanga nasan cewa lallai wannnan gida yana buk'atar gyara.

DIJE DIJE naji ana k'wala wa me sunan kira, wata matashiyar yarinya naga ta fito wacce ba zata wuce shekara goma sha takwas ba(18), daga ke wayen gidan wato band'aki. cikin sauri ta k'araso tare da fad'in " na'am iya ganinan, nashiga ke wayene fa" ta fad'a tana sosa kanta.

Wacce ta kira da Iyan ce ta k'araso inda take tare da kama kunnenta tace " wai ba naci kije ki anso magani ba, wannan sintirin bayin ya isa haka"

"nifa iya ba abimda ke damuna, cikina qalau gareshi" ta fad'a tana turo baki.

Iya ta sake janyota tace "ni da d'ina dake, taurin kai, maza ki wuce kije ki anso maganin, saura kuma, ki tsaya tsokanar da kika saba"

"yo ni ai dai bana tsokana, ai kema kinsani dai, kawai 'yan gulma ne sukai yawa a gari, shiyasa"

"to naji, ke kuma, wacce bata gulma ko, ungo nan, maza ki fice ki karbo, kuma ki dawo da wuri" ta k'arasa tare da mik'a mata kud'in maganin.

"naji" ta fad'a tana me ficewa daga gidan.

Tafe take tana 'yan wak'ok'inta, kamar ance d'aga kanki ki kalle gabanki, ta hango wata mak'ociyarsu, wacce taje siyan abu ta rik'e mata canji , wai ai naira goma ta bata, alhalin ashirin tabata, daman matar tasaba yi musu haka, runto ne da ita. ai kam ta k'arasa da sauri tasha gabanta tace " ah Ramansu audu unguwa zaki?"

Cikin washe hak'ora tace " eh ,kinga sauri nake zanje na kawai mutane a dashinsu"

"ahh cab ai kam, ya kamata kiyi sauri kar azo ana ta jiranki, kinga nikam zan karb'o maganin zawo wajen kuluwa"

"to se kin dawo, maza kije"

"to, se na dawo" ta fad'a tana me kallon ledar dake hannun Raman.

Kamar daga sama ta hango kare zaune gefe yana bacci, sanin halin Ramai bata san kare ko kad'an, ya sata yin k'wafa tare da nufar wajensa.

Kud'in da Iya ta bata, ta cire daga soken da tai, ta matsa dai_dai hancinsa ta samai, jin k'anshin kud'i a hancinsa ya sashe farkawa, mik'ewa yai ya fara laluban inda ze gansu. ita kam tana kallan Ramai, taga inda zatai, ganin ta shige wani layi ya sata, shino karan zuwa layin. ai kam da gudu ya d'eba yabi inda ta shunamai.

Ita kam Ramai hankali kwance ke tafiyarta, tana 'yar wak'a a hankali. kamar daga sama taga kare yayo kanta, haba me zatai, cikin sauri ta d'eba da gudu dan tsira, se dai kash ance sauri ya haifi nawa, da Ramai tasan me ze faru da ita da bata d'eba da guduba, domin wani k'atan dutsene da batasan dashiba, ya kadata, ji kake tif, ta fad'i k'asa.

  Ganin har a lokacin karen be daina biyo taba, ya sata k'ok'arain tashi, ai kam k'afarta tace k'aras, cike da sauti ta saki wata irin k'ara, shikam goga kare be tsayaba, saida yazo daf da ita sannan ya tsaya, ledar dake hannunta ya nufa, ganin halin da take ciki, da kuma azabar da takesha, bata san sanda tasakar mai ledar ba, ai kam ya d'auka a baki yajuya a binsa.

Dije ce ta fito daga ma b'uyar data b'uya tana ta narka uwar dariyarta, "oh su Ramai anji wuya" ta fad'a tana k'ara ke cewa da dariya. seda tai mai isarta sannan ta sa lallab'a ta kai wajen karen, yana zaune da leda a bakinsa, shi be yagaba, kuma be yarba, ganin hakan yasata sakin nunfashi tare da furta " kai, alhamdulillah, har naji dad'i wllh, wai daka yaga, ya zanyi, in bari nai sauri dai, kar ka yaga"

A hankali ta sa lallab'a wajensa, cikin hikima da rashin tsoro, ta fara k'ok'arin ciro ledar, ai kam ya mik'e tsaye tare da jujjuya kai. ganin hakan yasa ta ciro, kud'in Iya na siyan magani ta cu namai a hanci, ai kam ya juyo b'arinta, tare da sakin ledar, itam Dije buri ya cika, ta sakar mai kud'in ta d'au ledar ta juya abinta zuwa gida, da tunanin k'aryar da zata shir gawa iyanta.

Ciken d'aga murya ta shiga rafka sallama. Iya da ke zaune, kan sallaya tana lazumi tai gyaran murya, jin iyanta tai gyaran murya tasan lazumi take, ai kam tasaki wani murmushi tare da furta " kai amma , naji dad'i, sosai Iya alqur'an kin burgeni" tana gama fad'a tai d'akinta, wanda ke d'auke da ya gulgular katifa k'arama, se tabarma itama ta tsufa, se k'ullun kayan ta dake gefan katifar, d'akin ko shara babu, ita kanta katifar tunda aka tashi kanta ba'a gyara taba.

Zama tai kan katifar ta tura k'yauren d'akin nata tace " uhhm ko ya su Ramai, an tashi" ta k'arasa da saken wata shegiyar dariya.

Zaninta ta kwance ta fito da ledar da ta k'ulle, ta shiga zazzagewa a k'asa, se da taga ba komi a ledar sannan ta shiga har had'asu dan lissa fawa.

Cike da farin ciki ta d'ago daga k'irgen da take tace "kai cab, su Ramai an iya adashi, kanbu naira dubu ashirin da biyar, ashe kina tarawa mutane kud'i da yawa, na san kema ba a banza kike tarin nan ba, to wllh alqur'an ni ma se na d'ebe rabona"

Se da ta lissafa dubu bakwai cif, sannan ta bud'e jakar kayan ta, ta zazzage su, ta sami wani d'an kwali ta d'aure a ciki, ta sa shi can k'asa, ta mai da kayan ta rufe jakar. sannan ta k'ara lissafa dubu biyu tace "wannan na JUMMAI ne" k'awarta ce, ita ce abokiyar tsokanarta, da wasanta, tun suna yara tare auka taso, sedai ita gidan su Jummai suna da d'an rufin asiri, kuma ya fi na su Dije kyau da kyan gani.

Ragowar ta had'a tasake lissa fawa taga dubu goma sha shida ne, sannan ta mai da ledar ta bud'e k'yauran a hankali ta sa lallab'a ta fice daga gidan.

Bata zarce ko ina ba se gidansu k'awarta Jummai, tana shiga ta tarar da maman su zaune tana cin abinci, cikin nutsuwa ta shiga gaida ta, tare da tambayar Jummai.

Maman su Jummai tai murmushi ta ce "tana d'aka, tana baccin da ta saba"

Ba ta bata amsa ba, ta shige d'akin, tare da wani murmushin mugunta.

Cikin bacci Jummai taji wani irin zafi ya shigeta, zunb'ur ta mik'e tare da sosa wajen.

" dalla malama ki tashi, kin zo kin wani jab'e a waje d'aya"

Sai a sannan Jummai ta lura da ita tace "ai kin banza, amma dai ai ba a kanki na jab'e ba, kuma Allah ya isa na wannan dukan da akamin"

Cikin sauri Dije tace "yarinya wllh kinwa kanki, badai ni kikawa Allah ya isa ba?"

Sanin halin Dije, na in tasa mo musu abu, kuma tace baza ta bayarba, ta zauna ne ya sata saurin mik'ewa daga zaunen ta diro k'asa tace "haba k'awalliya roman jab'a, ai ba mayi haka da keva, ni ce fa, Jummanki"

"ke kika sani, in ma roman b'era ne oho, ki taso muje waje a kwai labari, yarinya"

"to amma banci abinci ba fa" Jummai ta fad'a.

  "ke dai ki bar abincin nan, kizo kije harkar arzik'e yarinya"

Ko gyalenta bata d'au kaba, suka fice.  se da suka zaga baya wajen wata bishiya sannan suka yada zango. Dije ce ta kalle Jummai tace " yarinya kinsan me na samo?"

Jummai ta gyad'a kai tar da fad'in " yo ni ina zan sani, se kin fad'a ai"

 
   Dije tace " hmm! yarinya arzik'i na samo mana, nan ta kwashe komi ta ga yamata"

Ha ba wa me Jummai zatai inba dariya ba, nan kwa tashiga k'yak'yatawa kafin tace "kai amma alqur'an kin iya rashin mutunci Dije, yanzu ya zatai da kud'in mutane?"

"oh mata, ita ta sani, yadda takewa mutane suji ba dad'i ita ma yau se taji, ke inaga fa har karyewa tayi, dan baki ga yadda ta fad'iba ji kike wani tiim" ta kk'arasa tana dariya.

  Jummai tace "kai amma su Ramai anji jiki, Allah sarki" itama ta k'arasa tana saken tata dariyar.

Dije tace " yarinya ga naki kason" ta ciro dubu biyun da ta ware ta mik'a mata.

"kai amma alqur'an kin burgeni" Jummai ta fad'a tana washe baki.

Dije tace " kinsan yanzu me za ayi, tashi zakiyi muje mu sa lallab'a mu maida mata da ragowar kud'in ta"

Jummai ta gwalo ido tace " kai-kai, wlllh ki bari in an fito dandali da daddare ma mayar, ni dai yasin tsoro na keji"

Dije ta kalle ta ayatsine tace " ai ni wllh daman dad'ina daki, rashin wayewa, sam bakya fahimtar abu, amma tunda kince haka shikkenan mubari anjiman a je"

"Allah ba haka bane Dije, kinsan halin Raman nan wllh, bata da kirki, kuma kinsan Baba yaji abinda mukai zane mu zeyi ko, ya hanamu fita ko ina"

"ehh to da wannan dan wannan, Allah ya kaimu anjiman" Dije ta fad'a.

Haka suka rabo akan da dare in an fito dandali se su maidawa Ramai kud'in ta.

 
Bari mukoma wajen Ramai kuma

Bayan karen ya juyawarsa, Ramai ce kwance shajaran, se faman sauke nunfashi take a hankali, kamar daga sama wasu samari suka 'bullo daga lungun, hango mutum kwance da sukai yasa su saurin k'arasawa dan ganin me ke faruwa, ganin mace kwance yasa su nema temaka mata, d'aya daga cikin su ne yace " nifa inaga kawai mu nemo mata 'yan uwanta se su kaita gida"

Wanda yake kamar shine babbansu yace " haka ne, to waza mu kira yanzu?" ya tambaya yana me kallon su.

Wanda yace a nemo matan ne yace " ga wani gida nan, mu shiga mu sanar dasu abinda ke faruwa"

Dukkan su, sunyi na'am da shawarar sa, hakan yasa su yin sallama, a k'ofar gidan, ba a wani dad'eba aka amsa musu, naan wata mata ta fito, take suka shai da mata abbinda suka gani, koda ta matsa kusa da matar se taga ashe Ramai ce, "ikon Allah, me yafaru da ita" ta fad'a, tare da bayya na mamakinta. kallon su tai tace " ai na masanta, mun gode sosai, kunji"

'Daya daga cikin su ne yace "ah bakomi" nan suka mik'e zuwa inda suka nufa. Ita kam komawa tai cikin gidan, ta sanar da sauran abinda ke faruwa da Ramai, nan suka fito aka ciccib'eta zuwa ciki, se da suka kwara mata ruwa sannan ta farfad'o tare da sakin wata shegiyar k'ara. nan dai aka bata ruwa tasha, sannan aka kira me gyara, dan su Ramai anyi karaya, aikam ansha artabu wajen gyaran, se da komi ya lafa sannan aka sabu machine (d'an achaba) aka sata a baya tare da wata suka nufi hanyar gidan ta, koda Ramai ta lura da ba jakar kud'inta nan da nan ta tuna da abinda ya faru, sanda ta sakarwa karen nan jakar kud'in , take kwa ta saki wani kuka, tar da fad'in "na siga uku ni Ramai, wllh sun yasheni, aljanune, wayyo kud'in mutane, na ga takaina" (hhhh!, ni kam nace "aljanun mutane ba" ).

Haka wad'anda suka kawota, sukai ta bata baki, akan tai hak'uri, ta mik'a komi ga Allah, tare da fatan bayyana 'barayin, dan su sam sunce ba wani kare da ze mata sata, kawai mutane ne 'barayi, nan dai aka bar Ramai da d'anta Audu, nata rarrashi, wanda shima be dad'e da dawowa ba, dan yaje gona.

'Bangaren su Dije kuwa ana ta shirye_shiryen zuwa dandali, dan sun ce sosai zasu rak'ashe war su, sabida yau wasai suke jin kansu.

 
Dare nayi Dije ta ziyarci gidan su Jummai, tana zuwa suka nufi dandali, yau ba su tsaya wani yin wasa sosai, dan basu bawa wasan nasu mahimmanci ba, domin suna da abinda suka tsara, basu fi minti ashirin ba suka yiwa gidan Ramai tsinke.

Allah kwa ya basu sa'a dan basu tarar da mutane a gidan ba, illah wata kanwarta da take jinyar Raman, kamar wa 'yanda abin ariziki ya kai su, cikin girmamawa suka shiga gaida su, da kuma yi mata sannu.

Ramai ta kalle Dije tace " Dije kinga abinda ya sameni ko, hmm nasha wuya, muna rabuwa fa dake, wllh bazan tab'a yafewa karen nan ba, har yanzu yana tashan Allah ya isa"

Dije tace "wllh koni da aka gayan wai kare ne ya biyo ki, ya sa kikaji ciwo, naji ba dadi, na dinga tsinewa wannan d'an banzan karen, alqur'an bazega haskeba sam"

Ramai tace "ai wllh Aallah ya isa na ni dai, har kud'in mutane ya d'auke, ni yanzu ban san ya zan bama"

Dije tace "haba Raman su audu, ki tuna akwai Allah fa, ze hore miki, kinji, kuma insha Allahu zaki gansu koda rabi ya bari ai kin rage asara"

Jummai tai saurin cafewa da cewa "wllh kam, ai tunda baki mutu bama ai an auna arziki"

"haka ne, na gode Allah, amma ai nasha jiki" Ramai ta fad'a. 

Nan dai suka cigaba da bata baki, kamar wasu mutanen arziki, sai da suka jima sannan suka ce zasu tafi, wanda a lokacin 'kanwar Raman bata d'akin, ganin hakan yasa Dije fito da 'kunshin kud'in ta fake idon Ramai ta jefa bayan gadon da take kai, kallon Jummai tai tace " tashi mu tafi, kada baba ya mana fad'a, kin san dai yace kar mu dad'e"

Jummai ta fake idon Ramai ta 'kifta mata ido tare da d'aga mata gira, itama sai ta d'aga mata hannu d'aya alamar komi yayi. nan dai suka yiwa su Ramai sallama, tare da mata fatan samun sauki

Suna fitowa suka kalle juna suka she'ke da dariya Dije tace " kai amma na d'an tausaya mata, Allah sarki Ramai, gaskiya kinji jiki"

Jummai tace "wllh ta ban tausayi, inama bame mata hakaba"

"dalla can ke dama wannan banzan tausayin naki, shi yake cutarki, shiyasa kike yawan kwafsa mana, ai seki kai mata naki, kinga inda rabon an rikeke, ance ki fito da sauran ka gaya musu, kuma wllh yarinya tace ninai komai, hmmm! kinsan sauran zan can ai"

Jummai ta kamo hannun ta tace "ke nifa da wasa nake mike"

"oho ke kika sani dai" Dije ta fad'a.

Nan dai suka suka cigaba da kyakyata dariyarsu, da zarar sun tuna yadda Ramai ki nishi tana ambatan "Allah ya isa ni dai" se su kwashe da dariya, a haka suka koma dan dali, nan ma sai da suka gama tsokane_tsokanensu, dan duk wacce suka gani da irin kwalliyar da tai se su she'ke da dariya, in kwa saurayi da buduruwa ne sai su kallesu su tafa su she'ke da dariya tare da fadin "wow ci ko ki da yawa a garin nan" sanin halin su ne yasa duk wacce suka tsokana bata biye musu, dan mutum se dai  yaji kunya, domin ta tas Dije ke musu, kuma ko agaban waye. da haka suka 'karasa gida, kowa ya shiga nasu gidan.

   ****     *****

'Bangaren ASHRAF kuwa, bayan ya gama cin abincinsa d'akinsa ya koma, ya hau danne_danne a laptop d'inshi, sai da yai kusan 30mnt, sannan yai shutdown d'inta, pillow naga ya d'auka ya koma kan sofa, yayi matashi dashi. ni kam nace "oh yau ba a gado za a kwana ba" can 'kasan zuciyar kuma,  cike yake fal da sa'ke_sa'ken yadda ze 'bullowa wannan sabon al'amarin. taya ma za ace kamar sa guda za a masa auren dole, ina sam baze yuwuba, da wannan tunin bacci 'barawo yai awon gaba dashi. to sai muce ASUBA TA GARI MALAM ASHRAF.


Washe gari da safe bayan sun gama break fast, Dad d'in su ne, ya soma da fad'in "Ashraf kaje kwa wajen yarin yar nan?"

Shafa kansa yai yace "no Dad, abubuwane sunmin yawa, ban samu time ba, amma zanje very soon"

"you shut-up, yanzu kai baka ji kunyar fad'a ba, wai aiki sunma yawa, da aikin da yin BIYAYYAH ga abinda na gin dayama wanne ya fi cancanta ka aikata? wllh Ashraf ka fita idona, kuma aure ne, ko ka naso ko baka so, sai an yishi, da izinin Allah. sannan na baka umarnin anjima kaje ka ganta, in ba haka ba, wllh sai nayi mugun sa'ba maka, kaje ko" ya 'karashe cikin zafin rai.

" naji, sorry dad, ba zan kuma ba, insha Allahu, kuma zan je"

"Da dai ya fima" mom  ta fad'a.

Ganin hakan yasa, ya mi'ke tare da d'aukan  mukullin motarsa yai waje.

Mom ta kalle Dad tace " kayi ha'kuri, halin son sai shi, na rasa ya zan mai, ko jiya sai da muka yi zan can , amma kamar wanda akaiwa zancan mutuwa, haka ya mi'ke yai d'aki, na rasa gane mishi, sam."

Dad yace "hmm! halin 'yan yau kenan, ka haifa baka haifi halin su ba, ana masa gata shi baya gani, Allah ya kyauta, amma aure kam ba fashi, da yardar Allah"

"ameen" mom ta fad'a.


Gidan su IMRAN ya nufa, saida suka gaisa da mom nasu sannan ya wuce part d'in Imran din.

Yana kwance yana sharar bacci, ganin hakan yasa shi yin tsaki tare da fadin "mutum bashi da ai kinyi se bacci"  filon dake kai ya shiga bubbugawa da 'karfe, firgit ya farka, dan dama shi mutum ne wanda ba me nauyin bacci bane.

"mits! wai ke wane irin mutum ne dan Allah" Imran ya fad'a yana me dallah mai harara.

"ban sani ba, dalla malam tashi, baccin ya isa haka" Ashraf ya fad'a.

Imran ya kalleshi tare da 'kara dallah mai hara ra yace "wai uban me zan ma ne, kazo ka dameni"

Ashraf yace "nima ban sani ba, amma wata k'ila inka tashi se na san abinda zaka min" yak'a rasa fad'a yana me jin gina da fuskar kujerar da ya zauna, tare da ciro wayarsa ya shiga daddan nawa.

Ganin hakan yasa Imran girgiza kai ya mik'e yan fad'in "ai kin banza, kawai azo a damu mutum, a hana shi sakat, me kama da aljanu kawai" yana 'karasawa ya fad'a ban d'aki, dan yasan halin Ashraf sarai, besan ace mai yana kama da aljanu.

Shikam ko kallon sa be yiba, se girgiza kansa dayai, ya cigaba da aikin danne _dannen sa.

Sai da ya dad'e a band'a kin, ba dan komi ba, sai dan ya 'batawa Ashraf rai, sanye da towel ya fito yana goge jikinsa, Ashraf dake kan waya ya d'ago ya kalleshi yace " ai na d'auka can za fata kake, ban za se kace mace"

Imran yai murmushi yace " waya sani, ba kaga na 'kara kyau, haske da she'ke ba."

"mits! kai ka sani, dallah ni yi ka shirya, ka rakane gun waccan abar" Ashraf ya fad'a, yana ya tsina baki, kamar wanda akawa dole.

Imran ya kalleshi yace " wace haka kuma?"

Ashraf yace "oho ku kuka sani, ni dai hurry up malam, ina da aikin yi da yawa aga bana."

Sanin halin Ashraf ne yasa be ce komi ba, dan yasan ko kwana za suyi ba ze gaya mai ko wace haka ba, bari in yaje yaga wace haka, da ba za a fad'i suna ba, sai dai "waccan".

Shaf_shaf ya shirya, tare da kallon Ashraf yace " i'm ok, can we go?"

Bece mishi 'kala ba, ya d'au car key d'in sa yai gaba. ganin hakan yasa Imran sakin wani 'kaya taccen murmushi, shima ya take masa baya.





********Dije ce zaune ga ban kawun ta yana ta faman mata fad'a, ya 'kara du banta yace " wllh na gaya miki, muddin ki ka bamu kunya, se nayi mugun sa'ba miki, shasha shar banza, kullum kina girma amma kina cin 'kasa"

Zun 'buro baki tai tace " kawu ni fa na gaya muku wllh ban son aure yanzu, haka kuren a lalatan rayuwa, kana gani laya ta gidan su mai 'kosai da aka mata auren sai yoyan fitsari take, sai kuma kuce zaku aurar da ni, dan kawai bakai ka haifan ba, wayyo baba ka dawo" ta 'karasa da saken wani d'an 'karamun ihu.

Kawu da ke kallon ta ya zuba salati kafin ya ce " yo daman in baki nuna halin naki ba, ai bake bace, kuma kisa ni, ba yoyo ba, ko mene se an miki auren, in anyi ki kashe kanki. kuma na gaya miki anjima zaizo, saura kiyi fitsarar take da kika saba."

Dije ta goge 'kwallar da ta zubu a kumatunta tace "amma sabida Allah kawo kun min adalci?"

"Ehh! lallai, ni kike cewa na miki adalci, tam shikkenan, kiyi abunda ranki keso, kada ki zama me BIYAYYAH akanmu"

Har ta bud'e baki zatai magana, Iya ta d'aga mata hannu da fad'in "a'a jikalle, kada kui haka da kawun naki, ni nasan baze miki abinda zai cutar da keba, kiyi ha'kuri, ki zama mai BIYAYYAH a gareshi, hakan sai ya sawa ran mahaifinki salama, yasan ya bar 'ya ta gari, kinji"

Ta zun'buro baki tace "naji, amma wllh in nima ya min ba dai_dai ba to zan rama, gwarama ku gaya mai, ba'a kawon wargi da raini"

Kawu ya 'bud'e baki zai magana, Iya ta katse shi da fad'in "bama abinda zai miki, jikalle"

"to ai shikkenan, angama, ni barin inje gidan su Jummai, kawu a gaida IYA, Iya ta gaida assha"

Tana 'karasa fad'a, ta arta a guje, dan tasan halin kawun nata, baya san wargi.

Kawu ya kalle Iya yace "kin ga ko, du ke kike d'aure mata gindi, shi yasa take abinda ta ga dama, gashi nan, a gabanki tana agaida ki"

Iya tai murmushi tace "to ya za'ai, yarinya ce ita, sai da lalla'bawa, ka dinga ha'kuri da ita kaji Auwalu"

"shikkenan, Allah ya kyauta. anjima shi yaron zaizo, dan Allah ki kula, kada ta'ki fita."

"ba matsala kada ka damu, ai zata, angama magana ai" Iya ta fad'a.

Nan suka ci gaba da hirar su, daga bisani yai wa Iya sallama, ya tafi.



Ita kam Dije na fita tai gidan su Jummai. Tana zaune a tsakar gida tana gyarawa mamansu kayan miya tai sallama. ajjiye wu'kar tai tace "ke lafiya na ganki haka?"

Dije ta zun'buro baki tace "ina fa, ina wannan saurayin da aka ce zaizo, wai na ganshi, shine zaizo yau, kawu ya sani a gaba yana ta fad'a, sai kace shi d'in d'an gwal ne"

Jummai tai murmushi tace "wllh ina ma ni ce ke, yarinya d'an birni fa, zaki koma can da zama, wllh kinyi sa'a"

"dalla ni yi min shiru, wllh dani yake zan can, Allah ya kawoshi lafiya"

"me zaki yi mai, Dije?" Jummai ta tambaya.

"oho! nima ban saniba, sai yazo kya gani" Dije ta bata amsa tana murgud'a mata baki.

Tofa Readers komi Dije za ta yiwa Ashraf......gadai su ASHRAF nan akan hanyar zuwa gidan su DIJE.....muje zuwa.

*Miss Gentle taku ce....*✍✍

Continue Reading

You'll Also Like

105K 9.1K 68
ဘာသာပြန်သူ - စွဲညို့အသင်း ရွှီမိသားစုရဲ့ တိသမီးက လက်ထပ်ပြီးတော့ ယန်ကျင်းကို ရောက်လာပါတယ်။ သုံးနှစ်ကြာပြီးနောက်မှာ သူ့ယောက်ျားက အောင်မြင်တဲ့ စာသင်သား...
106K 11K 120
"မှားယွင်းသော လက်ထပ်ခြင်းမှသည်.....ကောင်းမွန်သော အိမ်ထောင်သည်ဘဝဆီသို့...(၁)" ***MM Translation (Just for fun) "မွားယြင္းေသာ လက္ထပ္ျခင္းမွသည္.....ေကာင...
63.1K 6.6K 93
"မှားယွင်းသော လက်ထပ်ခြင်းမှသည်..... ကောင်းမွန်သော အိမ်ထောင်သည်ဘဝဆီသို့...(၂)" MM Translation (Just for fun) Chapter 41 in complete "မွားယြင္းေသာ လက္ထ...
1.8M 274K 82
Type - Web Novel (CN) Title - Tyrant Pampering Wife Diary (暴君宠婚日常) Author - To Know One Thousand In A Day /Yī rì zhī qiān/ (一日知千) Genre - Comedy, Rom...