9

47 5 15
                                    

https://whatsapp.com/channel/0029Va67gTqL2ATyyE577803
*Ko da So....*

*9*

*Book 2*

Tafe suke a mota kowa da abinda yake tunani aransa, dukan sitiyarin Dr ya yi da sauri ta kalle shi, duk ya haɗa gumu, cikin tsoro ta ce Dr baka da lafiya ne, faka motar ya yi yana wuci, so yake ya yi magana anma yasan ko me yace ba zai zama abu mai daɗi ba, fita yayi daga motar tare da fara bugun ƙirjin sa a hankali, muryar Hafsa ke masa yawo a kunne lokacin da take faɗa masa wai Tariq ita yake so, tsoro da tashin hankali duk ya cika shi yaga tashin hankali a idanun ta lokacin da Tariq ɗin ya faɗi kardai son Tariq ɗin take, kishi da tsoron rasa Hafsan duk sun cika shi. A nitse ta fito daga motar ta zagaya zuwa inda yake cikin muryar ta mai sanyi ta ce " Dr baka da lafiya ne ko kishin ne?" Kallon ta ya yi da mamaki "ki shi kuma ni na ce miki ina kishi" murmushi ta yi "Haba Dr Amaduna Hafsan taka fa ba yarin bace ai na daɗe da karantar ka, yanzu dai mai ke damun ka?" Cikin raunannyiyar murya yace tsoro ne, wallahi hankali na ya kasa kwanciya kar inje in rasa ki ga wancan mutumin"

Numfashi ta furzar kan ta fe "Haba Dr ai kaima kasan ni ta ka ce, sannan ko maza sun ƙare bazan auri minin Bilkisu ba wallahi ko da ace kai da kake type of Man da nake so bazan ma ji ɗarsuwan son ka araina ba sabida kai nata ne bare Tariq wanda He is not the kind of man I envisioned as my partner" shiru Dr ya yi kan ya ce but ɗazu mai yasa kika rikice dan ya faɗi, reaction ɗin ki over him ya tsorata ni sosai fa" murmushi tayi ɗan gajere kafin ta ce "Given our close friendship with his wife , with whom he has children, I could never wish for her to lose her partner and have their children become orphans. Absolutely not."

Maimakon ya bata amsa sai cewa ya yi " to yaushe zan turo?" tambayar ta zo mata lokacin da bata tsanmata ba, kallon ta yake cike da zargi da alamu so yake ya karanci reaction ɗin ta yayi ƙorafi, murmushi ta yi kan ta ce " yo in ta nine ai ko yanzu Dr ka turo a ɗaura mana aure ko dan kar ƴan matan Faculty suyi nasarar kwace mun kai, anma ka bari ina zuwa gida zamuyi magana da Abba in yaso sai in faɗa ma randa ya ce" murmushi ya yi cike da jin daɗi har naji sa'ida a raina wallahi, batun ƴan matan Faculty kuma ai kaf ciki babu mace guri na keɗin ke kaɗai nake gani" murmushi ta yi karfa kasa in nutse a gun nan dan daɗi, yanzu dai zaka iya tuƙa motar ko kuwa in tuƙamu" murmushin shima ya yi ah zan iya ai tuni naji ƙarfi da kwarin gwiwa sun cika ni da jin ni ɗin Nimber one ne aran abar sona"

Buɗe mata motar ya yi ta shiga sannan ya kuna zagayowa ya shiga ɓangaren mai tuƙi kan ya ja motar yabar gurin, a ƙofar gidan su Hafsa ma sun jima suna hira kafin suyi sallama ya tafi. Kai tsaye gidan su ya wuce fuskarsa cike da annashuwa duk wanda suka haɗu da shi sai ya fahinci farin cikin da yake ciki, tamkar sun san da zuwan sa kusan ƙannen sa huɗu ne a falon biyu mata biyu maza suma sunzo, da sauri Kalil ɗan ƙanin sa na biyu ya taso da gudu yana ga Uncle ga Uncle, ya yi caraf ya cafe yaron yana dariya "my Darling shine kunzo haka baka sa an kirani ba, yaron ya yi, tun ɗazu nake cewa Hajiya Kaka tasa Dady ya kiraka tace wai a ƙyaleka in taganka ranta ɓaci yake" murmushi ya yi kafin ya ƙarasa jikin Hajiya Kaka wadda ke kishin giɗe gaidata ya fara yi taƙi amsaws tare da rufe idanu tamkar mai bacci murmushi ya yi tare da faɗin oh wannan rayuwa zamanin nan da ban mamaki mata sun dena gudun kishiya duk dan naƙi ƙaro miki kishiya kike kike wannan abin wai" da sauri ta buɗe idanun ta cike da mamaki yayin da ƴan uwan Dr da Ummin su suka kwalalo idanu cike da mamaki wai yau yaya Ahmad ke maganar aure wanda tun Mutuwar matar sa ko fahinta ya yi maganar aure zaks masa yanzu zai bata rai.

Kamo hannun Hajiya Kaka ya yi badai kishiya kike so ba shikenan karki damu ni Ahmadu na yanke shawarar cika miki burin ki fatana kar ki zo kishi kuma yasa ki sai ina rabon faɗa tsakanin ku, dariya ta yi cike da murna da saurin zama yayin da ƴan uwansa suka yo gun da sauri inda Ummi ta kuma zubo musu ido, juyowa ya yi ya dubi ƙanne nasa alamun mene haka suka sa dariya, "iyayan tsugwididi ku fita batun manya ne, Khairiyya ce cikin shagaba tace yaya .... "Madan a fice ace mace da auren ta ta ƙi dena shagwaɓa, maza ayi waje" ƙin fita da sukai ne yasa shi cewa wallahi narasa randa kuka rainani haka," Umar ne ya matso yaya a ina take," Kallon Ummi ya yi yadda take kallon sa yasan amsa take jira.

Ko da soWhere stories live. Discover now