chapter Eight

96 7 2
                                    

🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

       *BOOK TWO*

.

_______________________________

        *CHAPTER Eight*

________🎓Haris ɗan wani babban attajiri ne ɗan siyasa, yanzu haka yana riƙe da kujeran Minister, shi ɗaya ne ɗa wajen iyayen sa duk da iyayen Familyn su ɗaya ne kuma babban Family ne dasu

Ya taso cikin gata sosai, babu abinda yarasa a rayuwan sa, wannan dalilin ne yasa yake taka duk wanda yaso yakuma hukunta duk wanda yake ƙi, sabida yana da ɗaurin gindin mahaifin sa don ko kaɗan baya ganin laifin sa

Haris yana da son mata da yawa sannan kuma yana da farin jinin ƴan matan, su da kansu ƴan matan suke kawo kansu wajen sa don yayi amfani dasu yabiya su kuɗi, duk da sau da dama suna kawo kukan su akan ya taimaka ya aure su amma shi a ganin sa babu macen da ta'isa yaso ta, shi dai kawai ya san mata a wajen sa su biya masa buƙata ne yajefar dasu don basu da wani Amfani

Ana cikin haka kwatsam yazo giftawa ta hanyar makarantar su Halwa yakusa bige ta, tun a lokacin da yaganta yakamu da tsananin kaunar ta har yana jin koda zai yi aure to babu shakka ita zai aura, duk da alokacin mafi rinjaye na zuciyarsa sha'awar ta ce, amma kuma ita kaɗai ce yake iya mata kallon wacce zata iya kasancewa matar sa anan gaba

Sai dai abinda be sani ba Halwa ta mutu a ƙaunar Nura a lokacin, duk da alokacin yaso yanuna mata kuɗi da gadara, amma da yaga yarinyan tana da taurin kai babu yanda zai yi yasame ta sai yakoma yana bin ta talalama

Sai kuma tsautsayi yagifta a ranan da Halwa tamare shi, wannan dalilin ne yaɗau alwashin sai yayi mata abinda baza ta taɓa mantawa dashi ba, domin kuwa tunda yake babu wanda yataɓa taɓa masa lafiyan jiki

A lokacin babu abinda be sani akanta ba, har soyayyar da suke yi da Nura ya san komi sabida yana da yaran da suke bibiyan masa ita

Abu na farko da yasoma yi shine neman Nura, har gida aka kawo masa Nura kuma yafaɗa masa buƙatarsa, a lokacin Nura be amince ba sai da yaji kuɗi Miliyan uku da yayi masa alkawarin zai basa in dai zai sadaukar masa da budurcin Halwa, shi a ganin sa idan har yakawar da sha'awar Halwa aransa to tabbas duk wani soyayya da yake mata zai gushe, wannan dalilin ne yasaka yanemi aikata mata fyaɗe bayan ya nemi taimako wajen Nura

Shi kuma Nura babu musu ya amince, a ganin sa idan har yasadaukar da budurcin Halwa akan wannan zunzurutun kuɗin be faɗi ba, kuma hakan yana ganin dama ce tazo mishi da zai yi kuɗi batare da yasha wahala ba, sannan yarigada ya saka ma ransa shi zai auri Halwa ɗin yarufa mata asiri tunda SHINE SILA, kuma shine zai ɗau alhakin duk abinda zai same ta don yarage girman laifin sa

BARRISTER IBRAHIM KHALILHikayelerin yaşadığı yer. Şimdi keşfedin