Part 28

38 3 0
                                    

🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''

.

      *CHAPTER 28*

     Ringing tune ɗin wayan sa ne yadawo dashi cikin nutsuwar sa, ahankali yasaka hannun sa yaɗau wayan yana duba wanda ke kiran sa, sai kuma yayi peacking call ɗin yana karawa a kunne, shiru yayi don haka Brr. Tahir yace

"Ya man meke faruwa ne wai? Nafita nazo na tarar da missed calls ɗin ka, I'm so surprised da naga kiran ka har 5missed call, ina fata lafiya dai?"

Numfashi Khalil yasauke a hankali kana yace

"Brr. Tahir yau fa daƙyar nasha hannun wasu mutane".

"Subhanallah.. wasu mutane kenan? Me kayi musu?" Brr. Tahir ɗin yafaɗa cike da firgici

"Hmm wasu mutane kasani in banda mutanen da muke Shari'a dasu, kasan da cewa kwanaki nafaɗa maka suna bibiyana but duk da haka ban yi tunanin abun ya kai hakan ba, nafita zuwa wajen Mr. Abdullah, lokacin nafito daga gidan sa sai natsaya nan Resturent inci abinci, bayan nafito nagan su sun biyo ni, wlh naji tsoro sosai coz suna ɗauke da bindiga, daƙyar nasha ina faɗa maka, ƙarshe dai can nabaro motan sai dai na'aika drever yaɗauko min".

Brr. Tahir yace "innalillahi wa'inna ilaihi raji'un.. Ib ina tsoron fa mutanen nan su cutar da kai, why not mu sanar da Police👮? sannan yakamata kabar gidan nan zuwa lokacin da za'a gama, hankalina be kwanta ba maybe su biyo ka har gida".

Shiru Khalil yayi naɗan wasu sakonni kafin yace

"Nima hakan ne araina, but nariga da nayi ma DPO magana, yace "zai turo yaran sa suyi gadina".

Ajiyan zuciya me ƙarfi Brr. Tahir yasauke kana yace

"But duk da haka dai hankalina be kwanta ba wlh".

Murmushi Khalil yayi yace "babu abinda zai faru sai alkhairi, insha Allahu gobe komi zai wuce".

"Hakane.. Allah yakaimu to".

"Ameen" Khalil ya'amsa masa

Daga nan sai da suka daɗe suna tattaunawa akan aikin nasu kafin suyi sallama, ya'ajiye wayan yana sakin ajiyan zuciya, kana yaɗan kwantar da kan sa saman pilow yana rufe idanun sa, fuskar ta ne yabayyana acikin ƙwayan idanun nasa, dasauri yabuɗe yana jin zuciyar sa na bugawa

"Meyasaka yarinyan taƙi ɓace masa?" Yatambayi kan sa yana dafe kan sa dake sara masa a hankali

Tun da yadawo gida yake tunanin ta, da zaran yarufe idanun sa kuma fuskar ta yake hangowa, kuma sosai yake ganin tsananin damuwa a fuskar nata, afili yafurta

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now