chapter Five

114 6 3
                                    

🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

       *BOOK TWO*

.

_______________________________

        *CHAPTER Five*

________🎓Rayuwan Khalil da Saleema rayuwa ce da suke yin ta cikin jindaɗin juna da nuna ƙauna da kulawa, zuwa yanzu komi yana tafiyan musu dai-dai

Gefe ɗaya kuma ciwon Saleema na zuwa mata jefi-jefi, duk da tana shan magani amma wataran haka zata tashi da tsananin ciwo har asibiti Khalil yake kai ta, sai kuma daga baya ciwon nata yalafa

Yanzun ma kwana biyu kenan bata jindaɗi sai dai ba sosai ba tana yin duk aiyukan ta tare da taimakon Khalil, idan yana gida shi yake taimaka mata da rainon Husna, girki kuma hanata yayi sai dai yayi musu Take-away, idan tatashi kuma da ƙwarin jiki sai tayi musu girkin

........ ........ ....... ........

Yau tun safe da Khalil yatafi aiki bayan ta gama gyaran gidan tayi ma Husna wanka itama tayi, sun shirya cikin farar atamfa me zanen ja da ruwan goro, ɗinkin riga da skert akayi mata sai akayi ma Husna doguwar riga dai-dai ita, duk kwalliyan da akayi iri ɗaya akai musu a rigan

Fitowa Parlour tayi da Husna a hannun ta ta'ajiye ta saman carpet, ita kuma tahaye kan 3sitter takwanta, yau sosai jikin ta yamatsa mata ga sanyi da take ji sosai duk da kuwa ta kashe AC da Fan ɗin parlour'n

A hankali ciwon yaci gaba da cin ta, hakan yasa tamiƙe takoma ɗaki tahaye kan gado taƙudundune da bargo, nan da nan tasoma rawan ɗari.

Wajen awanni biyu da shigan ta Khalil yadawo gidan, da sallama yashigo cikin parlour'n, da Husna yasoma cin karo tayi wasan ta har ta gaji tasoma ƙananun kukan ta daga ƙarshe barci yaɗauke ta a dungure a wajen ta kofa kanta kamar wacce take sujjada

Dasauri yaƙariso yana ajiye briafcase ɗin sa yasaka zara-zaran hannayen sa yaɗauke ta, sannan ne yaga ashe barci take yi, murmushi yayi yana kallon fuskarta da tataɓe baki duk hawaye ya gama bushe mata a fuskar

Gaban sa ne yafaɗi sakamakon ganin yanda kamannin ta da Halwa yasake fitowa ainun, basu da maraba a yanzu ɗin

Shiru yayi yana ƙure ta da kyawawan idanun sa, ya ɗau tsawon mintuna 3 kafin yamiƙe yanufi ɗakin Saleema da ita a hannun sa, yana shiga yahangi Saleeman kan gado nannaɗe cikin bargo

Dasauri yanufi bakin gadon dan yasan babu lafiya, ajiye Husna yayi can ƙarshen gadon kafin yamatso kusa da Saleeman yana zama ya yaye bargon yana kiran sunan ta

Zafin da yabuge sa ne yayi saurin sake yaye bargon yana tallabo kanta, nan yaga fuskarta sharkaf da hawaye idanun ta kuma sun kaɗa sunyi jawur gunun tausayi, gaba ɗaya jikin ta rawa yake yi ga shegen zafi kamar tafashashshen ruwa, shi kanshi dauriya yayi wajen riƙe ta

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now