chapter Six

107 7 3
                                    

🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

       *BOOK TWO*

.

_______________________________

        *CHAPTER Six*

________🎓 Wasa-wasa sai da Saleema tayi kwana biyar cur kafin tasoma samun sauƙi, sai kuma daga baya ciwo yazo mata rigigim, blending take tayi nan likitoci suka rufu akan ta

Halwa kuka Ummi kuka sun rigada sun cire rai ma Saleema zata iya rayuwa

Khalil shi kansa ya rasa inda zai saka kansa, tsananin tausayin matar sa gaba ɗaya ya cika sa, sosai yadamu da halin da take ciki

A ranan duk wani me tausayi dole yatausaya mata, ashe wai duk ɓari zatayi shine yaja mata hakan, sai da aka ƙara mata jini leda biyu sabida yanda tazubar da jinin ta wajen ɓari

Kwanan ta biyu kafin tafarfaɗo, sosai Saleema tayi jinya gaba ɗaya ta rame tayi baƙi sabida jinin da ake ƙara mata, kullum zuwa gaishe ta ake yi

Ita Halwa ma gaba ɗaya dena zuwa school tayi sai da tasoma samun sauƙi sannan ne Ummi tatakura mata tafara zuwa

Idan kuma tadawo nan take fara wuto wa sai dare takoma gida

Haka shima Khalil yake yi, duk da aiki yayi masa yawa amma kullum yana kan zuwa

Satin ta ɗaya aka sallame ta duk da ba wani warkewa tayi ba amma haka takoma gida tana jinya, Khalil shi ke kula da ita ko kaɗan baya gajiya, tausayin ta tsantsa ne a ransa

Haka rayuwa taci gaba da shuɗewa gashi yanzu har an shafe watanni uku da ciwon da Saleema tayi, yanzu komi ya koma normal sai dai ciwon da ba'a rasa ba wanda take fama dashi koda yaushe.


*________________________________*

Ƙarfe 03:20pm. Su Zainab da friends ɗin ta suka fito lectures

Tafiya suke yi suna hira ɗaya daga cikin su tana basu labarin gwaraman da akayi a anguwan su, sai dariya suke yi sabida yanda me basu labarin ta dage tana nuna yanda matar take ɗaukan mijin ta tana tiƙa sa da ƙasa

Daga bayan su can ɗan nesa kaɗan Halwa ce ke tafiya tana latsa wayan ta, tun daga inda take tana jiyo dariyan su sai dai hankalin ta baya kansu sai faman neman layin Drever take yi

Yau yayi late be zo ya ɗauke ta ba shiyasa take sake kiran sa taji inda yake, yana ɗagawa yace mata "gashi nan yanzu zai shigo school ɗin"

Tsayawa tayi a wajen har sanda tahango shi ya shigo cikin makarantan, sai tanufi wajen shi tana ɗaga masa hannu, shima ɗin ya ganta don haka yatsaya tahau yaja yayi reverse suka nufi bakin Gate

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now