chapter Thirteen

90 3 2
                                    

🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

       *BOOK TWO*

.

_______________________________

        *CHAPTER Thirteen*

________🎓 *AFTER THREE MONTHS*

"Wai jikin ne Sister?" Halwa tafaɗa lokacin da take zama gefen gadon

Numfashi Saleema taja tana sake jan bargon da tarufe jikin ta dashi a lokaci ɗaya tana bata amsa

"Wlh kuwa sis, gaba ɗaya bana jin daɗi yau, dama tunda naga a kwana biyun nan jikina ya soma kumbura na san akwai matsala".

Cike da tausayin ta Halwa tace "eyya ko dai in Kira Ya Khalil mu je asibiti, don bana son wlh ciwon ki yatashi da tsananin nan".

Ɗan guntun murmushi Saleema tasaki tana kallon ta cike da nuna jarumta tace "kar ki damu babu abinda zai faru, bari dai insha magani na sai in kwanta in ɗan samu barci insha Allahu zan ji daɗi domin barcin nake buƙata a yanzu".

"Tom bari in ɗauko miki Maganin".

Dasauri tamiƙe tazagaya side ɗin gadon tabuɗe drower taɗauko mata, tanufi Fridge tahaɗo mata da ruwa sannan tadawo tazauna

"Tashi kisha". Tayi maganar tana ajiye goran ruwan da maganin ajikin ta

Sai da tataimaka mata tatashi zaune kafin tabuɗe mata maganin taba ta tasha ta'ajiye ruwan a ƙasa

"Ki ɗan tsaya yanarke tukun sai ki kwanta".

Murmushi Saleema tayi tace "to Nagode sis, Ina jin daɗin kula dani da kike yi Allah yabiya ki da mafifin cin alkhairin sa.."

"Ya isa don Allah duk abinda zan miki be kai kwatankwacin taimakon da kikai min ba, kar ki damu sister insha Allahu Allah zai yaye miki duk wani damuwar ki, Allah maji roƙon bawan sa ne kuma yana jin mu".

Cikin jindaɗin maganar ta Saleema tace "Sister to ki je ki ƙarisa assignment ɗin naki mana ko kin gama ne?"

Gajeren tsaki Halwa taja tana shafa gefen fuskarta tace "wlh na kasa ƴar uwa, duk wani searching da zan yi ban samu abinda nake so ba, na dai ƙoƙarta nayi biyu a cikin biyar ɗin, kuma gashi Lecturer ɗin nan yace mana shine Test ɗin mu na rasa ya zan yi".

Saleema tace "to ki kai ma Yaya Barrister mana zai taimaka miki, tun farko ma na manta wlh da shi kika kai ma wa".

Halwa dai batace komi ba illa jinjina zancen da take yi aranta, ba wai kai mishin bane bata so kusancin su ne ko kaɗan bata so..

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now