Part 13

55 3 0
                                    

🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📚*
'''{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

         *⚜{{F.W.A📚}}*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''

.

     *CHAPTER 13*

*WASHE GARI*

ƙarfe 02:45pm. Drever'n Brr. Ibrahim Khalil yatafi kai shi airport, suna isa ba ɓata lokaci jirgin su yaɗaga dasu zuwa ƙasan Egypt.

_Sai muce Allah yaba da sa'a BARRISTER_🤒

....... ....... ........ .....
Kuka take yi sosai kamar ranta zai fita, tun sanda yafice gidan tazauna anan palow take ta rizgan kuka, sosai take cikin damuwa abubuwan duk sun haɗe mata, har yau takasa samun mafita, ta kasa samun nasara akan abinda aka saka ta, gashi yanzu mutanen nan sun sako ta gaba, sosai suke mata barazana, gefe ɗaya kuma zuciyarta ta azalzale ta da ƙaunar mutumin da besan tana yi ba, haka kawai take jin baƙin cikin tafiyan nan nasa, shikenan bazata sake ganin sa ba sai sanda yadawo? kuma batasan ranan dawowarsa ba, sai kuma tasake fashewa da kuka tuno mahaifiyar ta da tayi, yanzu da waɗannan mugayen basu ɗauke taba da tuni takoma gida, acan zata zauna har yadawo, "take tatuna sanda yakira ta yana zaune a palow tazo tazuƙuna gaban sa, sai da yagama latsa wayan sa kafin yaɗago kai yakalle ta yace

"Gobe zan yi tafiya, zaki iya komawa gida har sanda zan dawo, kiriƙe wannan ko zaki buƙaci wani abun".

Yamiƙo mata wasu maƙudan kuɗi, ahankali tasaka hannu ta'amsa tana jin zuciyarta babu daɗi, godiya tayi masa, sannan yabata umarnin "tafiya"

Shiru tayi tana ajiyan zuciya, rufe idanuwanta tayi tana sauraron bugun zuciyarta

"Meyasaka ban faɗamasa halin da nake ciki ba da yatambaye ni zuwa gida? Wataƙil yataimake ni, ya zanyi da waɗannan mutanen".

Take tasake tuno wayan da sukayi yanzu fitan shi, mutumin da yake kiran ta, shine dai yasake kiran ta yana tambayan ta, "ance zai yi tafiya, ko tasan ina zashi?"

Runtse idanunta tayi wasu hawaye na sulmiyo mata tuna amsan da tabashi

"A'a bansani ba, bansan ma zai yi tafiya ba".

Mutumin be ce mata komi ba sai yakashe wayan, da alamun kamar wani abun ne yataso shiyasaka yakatse kiran batare da sun gama magana ba, sake runtse idanun ta tayi zuciyarta na ci gaba da bugawa, tasani dole zai sake kira, amma batasan me zai biyo baya ba idan har sukasan ya tafi?

"Wataƙil ma su zo da kansu suyi binciken abinda suke nema".

Tafaɗi hakan afili tana buɗe idanuwanta, ɗaura kan ta saman kujera tayi tarufe idanunta tana ci gaba da tunani kamar yanda yazame mata jiki yanzu.

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now