Part 25

40 4 0
                                    

🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''

.

     *CHAPTER 25*

      *FEW DAYS*

"My dear kiyi sauri Kar kiyi late kuma?"

Halwa dake cikin ɗaki cikin sanyin murya tace "to Yaya ga ninan".

Fitowa tayi riƙe da Bairo a hannun ta tana kallon yayan nata, shima kallon ta yake yi cike da tausayin ta, gaba ɗaya duk ta rame sabida zazzaɓin da yasako ta agaba kwana biyu, tayi haske kallo ɗaya zakayi mata kagane sosai take cikin ciwo, itama Mama dake zaune kallon ta tayi tace

"Ni kuwa idan ba yazama dole bane Halwa a fasa zuwa makarantan nan mana, kinga yanda kika yi kuwa? Ba fa sauƙi kika ji ba?"

Kallon Maman tayi kawai tana marairaice fuska kamar zatayi kuka

Nura yace "Mama wannan jarabawan fa tana da muhimmanci tunda na fita ne, haka nan zata lallaɓa tayi har su kammala, kinga jiya ma taje tayi tadawo lafiya, zaki ga sauran ma kamar yanzu ne har an gama".

"Um um Nura, yau kaduba kagani sosai take jin jiki ko abinci ta kasa ci, ga wahalan da zataje tasha, me zai hana abari wani shekarar sai tarubuta".

Nura yace "kai Mama har shekara sai tayi ta zama agida? Kema kinsan halinta ba yarda zatayi ba".

Halwa tace "Mama ki dena maganar nan ma, kuma Ni haka nan zan je in zana jarabawa ta, sai dai in ciwon ya kwantar dani ne amma banga abinda zai hana ni zuwa ba".

Murmushi Nura yace "to kin ji dai".

Kaɗa kai Mama kawai tayi tace "ai shikenan Ni dama tausayin ki nake ji, yanzu ku hanzarta kutafi kar lokaci yaƙure".

Fita suka yi, A mashine ɗin Abokin Nuran yakai ta har cikin makaranta, yasauke ta a bakin ajin su.

Bayan kamar mintuna 20 aka zo raba musu pepper, lokacin ne kuma sosai jikin Halwa yayi tsanani, jikin ta sai kakkarwa yake yi zazzafan zazzaɓi yarufe ta, kasancewar mutum ɗaya-ɗaya ake zama a sit shiyasaka babu wanda ya lura da ita, tana can kusa da baya ajikin bango ta takure waje ɗaya, sai takifa kan ta a table tana hawaye, ita kan ta takasa jure yanayin da take ji, sai da Wani Malami yazo miƙa mata Pepper yakira sunan ta

"Halwa lafiyan ki lau kuwa? Za'a yi jarabawa kina kwance".

Ahankali taɗago kan ta tana ƙanƙame jikinta, face ɗin ta duk hawaye, kuma sai rawan ɗari take yi

"Subhanallah.. baki da lafiya ne?" Malam ɗin yafaɗa yana kallon ta

Gyaɗa masa kai tayi don takasa magana ma

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now