chapter Sixteen

76 5 3
                                    

🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

       *BOOK TWO*

.

_______________________________

        *CHAPTER Sixteen*

________🎓 Ɗakin Saleema tashiga nan taganta tana nannaɗe dadduma alamun ta idar da Sallah

"Oyoyo Maman Baby". Saleeman tafaɗa tana kallon ta fuskar ta cike da fara'a

Murmushi Halwa tayi taƙariso tazauna kan sofa tana faɗin "washh na gaji da yawa".

Ajiye dadduman tayi tazo tazauna kusa da ita

"Lallai kam ki ce zan yi tausa yau kar Baby yayi fushi damu".

Dariya Halwa tayi

"To ya jarabawan yayi sauƙi dai ko?"

Halwa tace " alhmadulillah komi normal ƴar uwa".

Saleema tace "masha Allah haka nake son ji, ya Baby be dai takura miki ba ko?".

Miƙe wa Halwa tayi tana bata amsa "to ga dai shi nan duk yabi ya ishe ni ya hana Ni saƙat yau".

Saleema marairaice fuska tayi tace "eyya sister Baki bashi abinci bane, i know kin bar shi da yunwa, muje yanzu ki bashi kar yasoma kuka".

"Ai kya bari nayi sallah ko?" Halwa tace tana dariya

Kafin tanufi hanyan ƙofa

Saleema ma miƙe wa tayi tabi bayan ta, suka fito tare Saleema tana faɗin

"Kiyi sauri sister Plz".

Halwa bata ce mata komi ba illa dariya da take mata tashige ɗakin ta, ajiye jakan ta tayi tacire Hijabin ta tashiga Toilet, alwala taɗauro tafito tashimfiɗa sallaya tamaida Hijabin ta tayi sallah, tana idar wa tazare Hijab ɗin tafita parlour

Lokacin Khalil ya shigo suna zaune shi da Saleema kan Two sitter, yayinda shi kuma yake latsa wayan sa

Ƙariso wa wajen tayi tana shirin zama Saleema tayi saurin cewa

"Sister je ki ɗibo abincin mana".

Yamutsa fuska Halwa tayi tazauna sannan tace "wlh bana jin yunwa fa, kuma ban ce miki kukan yunwa yake min ba".

Saleema kallon Khalil tayi tace "kana ji ko Ya Barrister, wlh sis sai ta haifa mana yaro ramamme ko kaɗan bata son bashi abinci".

Khalil be ɗaga kai ba bare yayi magana ba

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now