Part 17

37 6 0
                                    

🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''

.

      *CHAPTER 17*

      *WASHE GARI*
         *NIGERIA*

Da sallaman ta tashigo gidan, Mama dake zaune tana gyaran lagwani ta'amsa mata tare da faɗin

"A'a maraba da Zainaba"

"Mama ina wuni?"

"Lafiya lau, ya Umman taki?"

"Tana lafiya, tace in gaishe ki".

"Ina amsawa, ya wajen su Zaituna, ina fata kina leƙata?".

Murmushi Zainab tayi tace

"Eh Mama ina zuwa sosai".

"To madallah haka akeso, kishiga ƙawar taki na ciki ai, bata jindaɗi ne".

"Eyya Allah yasawaƙe, ai bani da labari".

Mama tace "ameen, ai zazzaɓi ne kuma jiya da dare ne ma jikin yamatsanta mata".

Cike da tausayin ƙawartan tasake cewa

"Mama Allah yasawaƙe bari in shiga wajen ta".

"Ameen Zainab".

Zainab na shiga taga Halwa saman gado ta kwanta tajuya ma ƙofa baya, ƙarisawa tayi kusa da ita tazauna a gefen katifan tana faɗin

"Halwa ya jikin naki?"

Halwa da tarufe idanunta batare da tamotsa ba tace

"Dasauƙi".

"Allah yabaki lafiya, shine kuma baki kiran awaya kin sanar dani ba? Yanzu da ba don naji Umma tana maganan saka ranan ki jiya ba shikenan bazaki faɗa min ba? Abin yaban mamaki ai ince kina cikin wannan farin ciki nasan da tuni kin garzayo kin fesa min".

Duk wannan surutun da Zainab take yi Halwa taƙi cewa komi illa jinta da take yi, hannu Zainab ɗin tasaka tataɓa wuyan Halwan tana cewa

"Wai jikin yayi tsanani ne haka da bazaki tashi muyi magana ba?"

Ahankali Halwa tabuɗe idanunta tatashi zaune tana kallon Zainab ɗin, cikin kasala tace

"Wani magana zamuyi?"

Zainab kallon yanda duk tayi wani yaushi idanuwanta sukayi luhu-luhu suka yi ja tayi tace

"Ƙawata me ke damunki ne? Kinga yanda kika koma? Ke da ciwo baya hana ki walwalan ki amma yanzu duk kin wani iri kamar kin daɗe kina ciwo?"

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now