Part 35

38 3 2
                                    

🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''

.

     *CHAPTER 35*

    Dad da Mom da Nazeefa ne zaune saman dainnig table suna yin luncing, baka jin ƙaran komi sai Spoons, ita Nazeefa kanta na ƙasa daƙyar take cakalan abincin, don har yau bata saba dasu ba, gwara-gwara Mom in suna tare su biyu.

Sameer ne yashigo cikin parlour'n yanufo su yana faɗin "wow nazo a sa'a domin yunwan nima nake ji".

Mom da taɗago kai tana kallon sa tace "ba daga gida kake bane?"

"Eh naje wajen Friend ɗina ne, kuma daga nan muka wuce Hospital  shine nabiyo ta nan".

Gyaɗa kai kawai Mom tayi tamayar da hankalin ta ga abincin ta

"My Dad barka da rana". Sameer ɗin yafaɗa yana dafa glass table ɗin da hannayen sa

Dad kaɗa masa kansa kawai yayi sakamakon ya sanya abinci a baki

sai lokacin Nazeefa taɗago kanta tace "sannu da zuwa Yaya".

Sameer ɗaura hannun sa yayi akanta yana kallon ta yace  "Yauwa ƙanwa ta, abinci kike ci ne haka babu tayi?"

Murmushi Nazeefa tayi tana Sad da kai ƙasa, zama yayi gefen ta kana yace

"To nima yi saving ɗina in tayaku".

Plate tajawo tasoma saving ɗin shi

Dad yace "Sameer yau wai ya naji wayan Ibrahim be shiga lafiya dai? Kuma ban gansa ba kwana biyu".

Ɗago kai yayi Sameer yana kallon sa yace "Dad wlh ban sani ba, nima dai tun yesterday rabona dashi kuma bamuyi waya ba".

"Ok ƙara try Numban sa kaji yanzu".

"Ok Dad".

Wayan sa yaɗauka yasoma kiran Khalil, ringing ɗaya tashiga but babu answer, sai da yayi two missed calls kafin Dad yace masa "yaƙyale sa haka". Abincin su sukaci gaba da ci, kamar 5mint kuma sai ga wayan tana ringing, Khalil ɗin ne yakira, ɗauka Sameer yayi zai miƙa ma Dad sai yace masa

"Ɗauka kawai kace masa ina kiran sa yanzu yazo yasame Ni".

"Ok Dad".

Peaking call ɗin yayi yace "Hello ɗan ƙanina".

Khalil dake zaune bakin gado daga shi sai gajeren wando yaɓata fuska yana cewa "Bro bana so fa nace maka".

Ɗan dariya Sameer yayi kana yace "ok na daina, kazo Dad na Kiran ka".

BARRISTER IBRAHIM KHALILحيث تعيش القصص. اكتشف الآن