Part 30

44 3 0
                                    

🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️ ~What'sapp Number 07065334256~

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''

.

     *CHAPTER 30*

Washe gari ƙarfe 07:15am. Saleema tagama shirin ta na zuwa school, tana shirin ɗaukan jakan ta taji cikin ta yasoma murɗa mata, dasauri tariƙe tana runtse idanun ta, lokacin ne Halwa tafito daga Toilet tana kallon ta, ganin tana riƙe da ciki taƙi jirgawa yasa tamatso kusa da ita cikin sanyin murya take tambayan ta "ko wani abun na damun ta?" Murmushi Saleema taƙaƙalo tare da girgiza mata kai, sai dai har alokacin tana riƙe da cikin nata ne, hannu tasanya taɗau jakan kafin takalle ta tace

"Ni natafi school sai na daw.."

Bata ƙarisa maganar ba tadurƙushe nan ƙasa tana faɗin

"Wayyo cikina wayyo Allana".

A ruɗe Halwa tabi ta ƙasan tana kiran sunan ta tare da tambayan ta abinda ke damunta, ganin tasoma kuka sosai tana sake riƙe cikin ta yasaka tamiƙe dasauri tafita, ɗakin Ummi tashiga dasauri, tana tsaye kuwa itama tagama shirin ta nazuwa Hospital kasancewar ita ɗin Nurse ce, taburmo ɗakin tana kiran sunan ta, Ummi kallon ta tayi tace

"Lafiya Halwa meke faruwa?"

Cikin rawan murya kamar zatayi kuka tace "Saleema ce babu lafiya".

"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un". Ummi tafaɗa cikin tashin hankali kafin tanufo wajen ta tana faɗin

"Tana ina? Ina take?"

"Tana ɗaki".

Atare suka isa ɗakin lokacin gaba ɗaya Saleema tafita hayyacin ta sai kuka take yi, ga duk kan alamu tana jin jiki sosai, riƙo ta Ummi tayi tana kiran sunan ta tare da tambayan ta "Ina ke mata ciwo?" Duk hankalin Ummi atashe yake tarasa ma me zatayi

Halwa tace "Ummi ko za'a kira Abba akaita asibiti?".

Sai alokacin tunanin hakan ma yazo ma Ummi, tayi saurin cicciɓan ta Halwa tatayata suka fito da ita, suna fita waje Drever yazo da gudu yabuɗe musu mota suka saka ta, Ummi tashiga baya kusa da Saleema, ita kuma Halwa tashiga gaba tare da drever suka tafi, sai acikin motan Ummi ta'ari wayan drevern takira Abba tasanar masa.

Lokacin da suka isa asibitin tuni an amshe ta kasancewar ba yau suka saba zuwa ba, kuma dama tana da Doctorn da yake duba ta na musamman acikin asibitin, ana shiga da ita Abba shima ya'iso duk hankalin sa atashe, Halwa yanda taga su Ummi sun tashi hankalin su sosai itama sai taji duk ta damu, haka tazauna waje ɗaya tatakure tana tuna ɗan zaman da sukayi daga jiya zuwa yau, sosai tafahimci ita ɗin yarinya ce me tausayi da son mutane, sannan kuma ta fahimci akwai ƙauna sosai a tsakanin ta da iyayenta, take taji hawaye ya zubo mata tayi saurin saka hannu tana sharewa.

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now