chapter Eighteen

72 6 3
                                    

🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

       *BOOK TWO*

.

_______________________________

        *CHAPTER Eighteen*

________🎓 Lokacin Ummi taci gaba da sallan ta, sai Larai ne tayi mata magana

"Halwa wai lafiya kukan me kike yi?"

Shiru Halwa tayi taci gaba da zubar da hawaye tare da haɗiye kukan nata

Larai ajiye yaron tayi lokacin yayi barci sai takoma shimfiɗar ta takwanta, babu jimawa kuwa barci yaɗauke ta, to bata san dai ya aka ƙare ba sai washe gari da suka tashi da safe

Lokacin yaron sai ɓaɓɓaka kuka yake yi amma Ummi na gani bata ce Halwa taba shi Nono ba, sai ma ɗaukar sa da tayi tana rarrashin sa, sannan takalli Larai da tasaki baki tana kallon su

"Yauwa Larai ke nake ta jira, don Allah kije yanzu ki amso min madaran sa wajen Sister A'ishah, naji ta shiru bata kawo min ba gashi kuma yana ta kuka".

Larai tace "to".

Sannan tanufi ƙofa tafice

"Itama kuma a lokacin Halwa ta gama cire kayan ta ta ɗaura zani tanufi Toilet don yin wanka

"Halwa kiyi wankan nan da kyau don Allah, yanzu zan zo idan Larai ta dawo sai in taimaka miki".

Gyaɗa kanta tayi tabuɗe Toilet tashige batare da ta furta komi ba.

Lokacin dasu Abba suka shigo asibitin a time ɗin ne kuma ƴan sanda suka zo, don haka basu shigo ɗakin ba sai da suka gama da Police ɗin, sun zo yin bincike akan harbin Khalil da aka yi

Bayan duk sun yi abinda yadace sai Dad dasu Brr. Tahir suka bi su can Station ɗin kamar yanda suka buƙata

Abba ne kaɗai yashigo ɗakin

Halwa na zaune saman gado tana shan tea, sai Ummi dake zaune kan kujera riƙe da jaririn tana sake bashi madara

Sallaman Abba ne yasaka duk suka ɗago kai suna kallon sa sannan suka amsa

Shigowa yayi ciki yana kallon Ummi fuskar sa da tsananin mamaki

"Ina kwana Abba". Halwa tafaɗa kanta a ƙasa

"Lafiya lau ƴa ta ya jikin naki?"

"Alhmadulillah".

"Masha Allah haka ake so Allah yaƙara lafiya".

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now