Part 20

46 3 0
                                    

🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''

.

     *CHAPTER 20*

Tana kwance saman katifan ta daga ita sai farar doguwar riga irin me taushin nan da zanen flowers ajikin rigan, kanta babu ɗankwali sai gashinta da yawargaje yazubo mata har kafaɗunta, littafi ne a hannunta tana karanta wa tajiyo sallaman ƙawarta daga waje, amsa mata tayi sannan tashigo takalle ta tana faɗin

"Ƙawata hutawa kike yi ne?"

Tashi zaune Halwa tayi tana yatsina fuska tace

"Uhm hutu kuma? Karatu dai nake yi".

"Yayi makaranciya, kinga ni wlh ban ma bi ta karatun ba don bani da lokaci yanzu, ina Mama naji kamar ke kaɗai ce gidan?"

"Eh Yaya Nura ya kai ta kasuwa".

"Kai ƙawata wlh baki ga yanda kika sauya ba, wai meye sirrin ne ni naga kamar kina ƙara wani haske ne da kyawu kamar bakijin dawan garin? Ko dai yaya Nura ne?" Zainab tafaɗi hakan tana ƙare mata kallo tare da dariya

Murmushi Halwa tayi, sosai itama take ganin sauyi daga gare ta, tayi wani haske fayau duk da ita ɗin ba fara bace, gashi kuma ko ina nata yaciko gunun sha'awa

"Hmm ke dai ban son tsegumi me kikeson cewa akan Yaya Nura?"

Dariya Zainab tayi tace

"A'a babu komi, kawai dai ina tunanin ko har yafara sauya kulawan sa ne daga gare ki tunda yaga kin kusa zama mallakin sa, kin gane dai irin uhm uhmmm.."

Dukan ta Halwa tayi a cinya tana cewa

"Banson sharri shegiya ke babu abinda kika iya sai saka idanu, yanzu me kikazo yi ne don nasan ba banza takawo ki ba?".

Waro ido Zainab tayi tace

"To me kike nufi? Ko nace miki wani abu nazo amsa wajen ki? Kinga ni tare da Safna muke zamuje gidan aunty Zaituna, shine nace bari in shigo ko zamuje tare sai gashi Mama ma bata nan".

Halwa tace "wato da Safna ma kuke taƙi shigowa? Lallai kam zataci uban ta wlh dani take zancen".

Zainab tace "ni fa bana faɗa miki bane kije kuyi halin naku".

"Ai kibar ni da ita zamu haɗu ne wlh, kuma kisanar da ita hakan".

"Baki da ƙafa ne? Kifito kije kisame ta mana". Zainab tafaɗi hakan tana nufan ƙofa zata fice

Gyara zaman ta Halwa tayi taɗau littafinta tana faɗin

"Banda lokacin ku yanzu, sai mun haɗe a school".

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now