chapter fifteen

72 4 3
                                    

🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

_Wannan shafin naki ne *NANA ALIYU* ki more kiji daɗin ki ke kaɗai bance wani yataya ki ba, na gode da ƙaunar ki gare ni._

       *BOOK TWO*

.

_______________________________

        *CHAPTER Fifteen*

________🎓 *TWO DAYS*

Yau agajiye yadawo aiki, bayan yayi parcking motan sa yafito riƙe da briafcase ɗin sa da Suit ɗin sa da yacire, rufe motan yayi yanufi cikin gidan cikin tafiyan sa me burge wa, duk da kuwa a yanzu ɗin salon tafiyan ya sauya yana yi ne kamar me tsoron taka ƙasa, nan kuwa duk cikin gajiya ne

Tura ƙofan yayi kafin yayi sallama wanda a dai-dai laɓɓan sa yatsaya

Babu kowa cikin parlour'n don haka kai tsaye ɗakin sa yanufa, sai da ya'ajiye komi na hannun sa sannan yazauna yasoma zare Combat ɗin ƙafafun sa da Socks, bayan ya gama sai yaɓalle bottles ɗin rigan sa gaba ɗaya singlate ɗin jikin sa ya bayyana, be cire rigan ba sai yagishingiɗa akan pilow yana lumshe idanun sa

Tsawon mintuna biyar yaɗauka kafin yamiƙe yanufi parlour riƙe da wayan sa a hannu yana latsa wa

Har alokacin babu kowa a parlour'n don haka kansa tsaye yanufi kan dainning, har ya zauna kuma sai yamiƙe yanufi ɗakin Saleema

Ƙofar a buɗe yake ba'a rufe duka ba, har ya saka hannu zai sake tura wa yashige sai yaji maganar Halwa wanda yasaka dole ya ɗan dakata yana sauraron su

"Ki dena ma maganar Haris a yanzu, yanzu na rigada na cire wannan burin a raina, Ni ce Mahaifiyar Husna kuma na baki ita har abada wlh, kin san kuma be da iko da ita tunda dai ba aure aka ɗaura mana dashi ba, musulunci ya yarda idan an haifi yarinya ba da aure ba uwa ke da alhakin riƙe ta".

Rungume ta Saleema tayi cike da farin ciki tace "gaskiya na gode ƴar uwata, kin bar burin ki akaina duk sabida ki faranta min bansan da me zan saka miki ba, Allah yabiya ki.."

Katse ta Halwa tayi da faɗin "Ni fa nace miki bana son godiya, idan na baki Husna ba ke ne zaki gode min ba, Ni ce zan gode miki, don haka ki dena min godiya don Allah".

Sakin ta Saleema tayi tana murmushi tace "ai bazan dena miki godiya ba wlh, kin bani Husna sannan kina shirin haifa min wani ɗan, idan ban miki godiya ba me zan miki?"

Halwa tashi tsaye tayi tana yamutsa fuskarta tace "kinga Ni bani da lokacin wannan yanzu, bari inje inyi wanka in shirya in tai school, tunda yau Pepper ɗaya zan yi insha Allahu zan biya gida nagaishe da Ummi".

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now