Part 40

40 6 1
                                    

🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''

_*NANA FARUK* wannan shafin naki ne ke kaɗai, Allah yabar ƙauna🥰_

.

    *CHAPTER 40*

  Turo ƙofan Mom tayi tashigo cikin ɗakin, Nazeefa dake zaune tsakiyan gado ta tanƙwashe ƙafafun ta tana faman tunani taɗago kai tana kallon Mom ɗin, ita kuma ƙarisowa tayi tazauna gefen gadon tana kallon ta tace

"Meke damunki Nazeefa?"

Nazeefa kallon Mom tayi tace "babu komi Momy".

"Ban yarda ba ki faɗa min gaskiya idan da akwai abinda ke damun ki, gaba ɗaya na lura dake tun da daɗewa kina cikin damuwa, kullum cikin tunani kike kuma kinƙi kifaɗa min abinda ke damun ki, bana son in ganki cikin damuwa hakan na damuna coz Ina jinki tamkar ƴata ta cikina ne".

Sunkuyar da kanta ƙasa tayi tana jin hawaye na son zubo mata, idan da tana da daman faɗa mata abunda ke damun ta da tuni tadaɗe da sanar mata, sai dai kashhh baza ta taɓa iya faɗa mata gaskiyan abinda ke cin zuciyarta ba

Dafa bayanta Mom ɗin tayi tace "ki sanar dani kinji Nazeefa zan miki duk abinda kike buƙata idan har ina da halin yi, bazan taɓa barin hawayen ki yazuba ba zan kasance me share miki hawayen ki".

Wani irin sanyi Nazeefa taji acikin ranta tare da wani irin ƙaunar Mom na sake shiga zuciyarta, sai dai baza ta taɓa iya faɗa mata ciwon son ɗanta ne yakamata ba, "to taya?" Hawayen da taji suna son zubo mata ne tayi saurin mayarwa tana ɗago kai takalli Mom cikin sanyin murya tace

"Momy babu abinda ke damuna, idan har akwai kece ta farko da zan faɗa miki sabida na ɗauke ki tamkar ke kika zuƙuna kika haife ni, ki yarda dani Momy babu abinda ke damuna".

Shiru Mom tayi tana kallon ta, sai dai ko kaɗan bata yarda babu abinda ke damun ta ba bcoz ko wanene yaga halin da take ciki dole yatabbatar wa kansa tana cikin tsananin damuwa, sosai take mamakin abinda ke damunta har takasa bayyana mata, amma kuma tayi wa kanta alƙawari sai ta gano ko me ke damun ta kuma sai ta share mata hawaye da iznin Allah, ajiyan zuciya tasauke kafin tace

"To shikenan na yarda dake, amma duk abinda ke damun ki kiyi gaggawar sanar dani ki dena ɓoyewa kinji?"

Gyaɗa kanta Nazeefa tayi sai kuma tace "insha Allahu Momy".

"Ok tashi ki cire kayan makarantan akwai inda zaki raka Ni".

Amsa mata tayi tana tashi tare da saukowa daga kan gadon, itama Mom tashi tayi tafice a ɗakin, sauya kayan ta tayi tasanya doguwar rigan abaya Blue Black, sannan sai tayi Rolling da ɗankwalin abayan, komai bata shafa a fuskarta ba illa flat shoes da tasanya a ƙafafuwan ta, sosai tayi kyau white skin ɗin ta sai sheƙi yake yi kasancewar ta samu hutu har wani ƙiba tayi tare da ƙara girma, fita tayi ta'iske Mom a parlour suka fice, motar Mom ɗin suka hau drever yatuƙa su suka bar gidan.

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now