Part 44

45 4 0
                                    

🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

*\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''

.

*CHAPTER 44*

Lokacin da Khalil yazo har su Mom sun fito da ita parlour, babu ɓata lokaci yariƙe ta suka fito waje inda motan sa yake, Mom tace mishi "yakai ta asibiti" amma ita Saleeman tace "tana da maganin ta a agida" don haka gida kawai yanufa

Suna zuwa yayi parcking yafito yabuɗe mata motan yariƙo ta tafito, duk da a halin ciwo take amma sosai taji daɗin kusancin sa gare ta, har wani sanyi take ji aranta tana jin kamar ciwon na son tafiya

Tana jingine da jikin sa har suka isa parlour yataimaka mata tazauna sannan yakalle ta cike da tausayi yace

"Ina kika ajiye maganin in ɗauko miki?"

Cikin muryan marasa lafiya tace "yana cikin trolly na Wanda nazo dashi daga gida".

Gyaɗa kai kawai yayi yanufi ɗakin nata, yana shiga yasoma wurwurga idanu, can yahangi akwatunan da yayi mata guda shida, sai yamaida idanun sa kan wani babba kalan sa daban, yana da tabbacin shine wanda take nufi

Wajen yanufa yabuɗe, duk abubuwan amfanin ta ne da tazo dashi daga gida, yana soma bincika wa yaga ledan maganin, ɗauka yayi yanufi parlour'n

Zama yayi gefen ta yabuɗe tare da nuna mata alamun tayi masa bayani, nuna masa waɗanda zata sha ɗin tayi yaciro yamiƙa mata sannan yatashi yaje yaɗauko ruwa a Fridge yabata

Har tagama sha yana ta kallon ta kamar wanda zai haɗiye ta, hakan yasa taji kunya tana sad da kanta ƙasa, be san sanda yasaki guntun murmushi ba yamiƙe tsaye yanufi kichen ita kuma tabi bayan sa da kallo cike da tsananin ƙaunarsa a ranta

Be wani jima ba yadawo riƙe da Cup a hannun sa, miƙa mata yayi yana tsaye a kanta, ita kuma tasaka hannu ta'amsa tana kallon abinda ke ciki, Tea ne yahaɗo mata, be ce mata komi ba sai dai kallon ta da yake yi har tashanye tatashi da ninyan kai Cup ɗin

"No kawo cup ɗin, je ki kwanta idan an kira sallah zan tashe ki".

Babu musu tanufi ɗakin ta tashige, shi kuma bayan ya kai Cup ɗin kichen yadawo yanufi ɗakin sa, ɗakin karatun sa yashige (Library) yasoma binciken abinda yakawo sa, har aka kira sallan azahar yatashi yagabatar yakoma yaci gaba da aikin sa, yana tune da Saleema sai dai yaƙi tashin ta ne saboda bata daɗe ba aka kira sallan, don haka yabari zuwa sallan Asar yatashe ta

Sai da aka kira sallah yafito yashiga Toilet yaɗauro alwala, fitowa yayi yana warware hannun rigan sa da yanannaɗe wajen yin alwalan, yafito daga ɗakin nasa yashiga ɗakin Saleema, yana shiga ya'isa bakin gadon yatsaya yana kallon ta, barcin ta take yi cikin kwanciyan hankali, sai dai yanda take fitar da numfashi da ƙarfi hakan zai sa kagane ba lafiya ba

BARRISTER IBRAHIM KHALILTempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang