👩👩👧👧WASU MATAN 👩👩👧👧
@2021
~Mallakar Zeesardaunerh~💜🖤
Story and Writting
by
Zainab Sardaunerh
🔔📚
JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚
{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa}_
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo
⚜️©J.A.W📚🖌️
Assalamu Alaikum sunana Ummu Maleek
Muna siyarda kayayyaki masu kyau da inganci
munada maganin Ni’ima macce duk rashin ni’imarta Insha allahu rabbi zataji ni’ima tamkar korama ±💃💃💃💃
Muna da maganin infection ko wanne iri duk nacin infection Insha allahu rabbi kikayi amfani dashi zai rabu dake
munadasu Tsumin kala kala Munada gumbar nonon rakumin munadata dabino
Akwai mallakar miji masu zamu🔥🔥wanda inki kayi amfani dashi mijinki ko dutsene shi saiya tanka
Munada Emergency thghting duk yadda kika kai da budewa zaki hade tsaf Insha allah’ akwai hips Elargenment akwai breast Elargenment
Munada kayayyakin mata kala da iri masu zafi🔥🔥tamkar boom😻😻sha yanzu magani yanzu
Duk abinda kake da bukata zaka iya nemana ta👉07037112549
©️♤♡ Zeesardaunerh
Page 93~~94
Suman tsaye yayi yana kallonta ba tare da ya mayar mata da martanin runguma ba.Ita kuma bata damu ba domin tasan dole ne ya shiga shock amma sai ta fuske kamar batasan yanayin da ya shiga ba.
Kiss ta sakar masa a kumatu da kuma lips dinsa tare da jan hannunsa tana cewa..
"Muje ciki ka watsa ruwa nasan ka kwaso gajiya"
da "umh" ya bita domin yama kasa magana jin yake makogwaronsa a bushe, ga sarawar da kansa ke yi masa ga kuma mamakin Gimbiyarsa na neman kashesa.
Direct taja sa izuwa dakinsa, suka shiga ta zaunar dashi kan gadon tana cire masa talkami da safa,da kyar ta bari yashiga toilet domin wasa ruwa ji take wani abu na fisgarta tabbas tayi missing dinsa ba kadan ba.
Da kyar yaja kafafunsa ya wuce toilet aransa kuwa tunani ne kala_kala.
Bayan ya fito ne ya saka riga da wando mara nauyi,yana ciki n saka turare ta shigo cikin dakin, dago kansa yayi ya kalleta idanunsu suka shiga cikin na juna wani irin abu yaga yana fitowa daga cikin idanunta izuwa nasa,da sauri ya kauce yana karanta "Auzubikalimatullahi tammati min sharri ma khalaqa"
Hannunsa ta kamo tana cewa "ur dinner is ready yayana"ta idar da kalmar cikin salo mai jan hankali.
Bin bayanta yayi zuwa madai-daicin dining dinsu,sarving dinsa ta fara yi a plate dama ta saka nata tun dazu kafin tasa magani ciki.
Ita da shi duk wani iri suke ji har ta manta rabon da ta girka masa abinci yaci duk da wannan ba ita ta girka ba amma ko girkin ta mance rabon da a yishi gidan sai dai na siye.
Tun bayan aurensu da wattani ta daina girki ganin cewa ta mallakesa yadda takeso sai abinda tace,shi kansa baya son yaga tana aiki,wanke-wanke da shara duk shi yake yi.
Ba irin tunanin da baiyi ba a cikin ransa wani sashe na zuciyarsa na ce masa Maryama ta shiryu ya yinda wani sashen ya ki yarda haka kawai maryama bazata sauya lokaci guda ba tabbass akwai dalili! taya zai san wannan dalilin yana bukatar sanin miye ya sauya Gimbiyarsa! anya wannan sauyin na Allah da annabi ne ko kuma zancen da abokaninsa ke fada gaskiya ne? kai ina!! duk rashin hankali na Maryama bazata aikata shirka ba.
Bismillah yayi sannan ya fara cin abincin tabbas wannan kamshin yana takurasa amma ya kasa gaya mata hakan.
Haka suka raya wannan daren cikin soyayya da farin ciki mussamman Maryama ko shi kansa ba dutse bane yayi missing din matarsa.
BAYAN SATI GUDA
ALEEYA
Girki Agla ke kokarin daurawa inna Saude ta hana ta tana cewa ta barshi kawai itace zata girka tawuce taje tayi wanka bata musa ba ta wuce dabi'arta ce bata jayayya da wad'anda suka girmeta musamman ma wacce ta kewa kallon uwa wato Inna Saude duk da cewa Al'amurran da suka faru a yau sun matukar daure mata kai but ba tanka ba kuma bata tambaya ba domin bata kokkofi game da harkokin mutane iya nata idanu ne kawai.
Wanka tayi da wani sabulu mai kamshi da Inna Saude ta bata wanda tunda take bata taba wanka da irin sa ba in ba gidan mama kareema taje ba sai dai goga_goga wani lokacin ma sai dai omo, ko da ta fito inna Saude ta bincika komatsan tufafinta ta samo mata wata riga da zane da kallabi wad'anda basu sha jiki ba na sallar bara ta fito mata da mayafi cikin kayan Salamatu duk tasan abu ne mai wuya.
Vasilin ta shafa sannan ta saka tufafin duk da cewa tanason kamshi sosai fiye da sammani amma bata saka turaren ba zuciyarta na ayyana mata cewa akwai inda Inna ke son aikanta shiyasa ta sakata yin wannan shirin haka.
Tana zaune cikin dakin nasu Inna Saude ta shigo kallo daya ta mata taga ba laifi tayi kyau sosai duk da kuwa fuskarta bata ga powder ba, sai vasilin din da ta murzawa pink lips d'inta kad'an, "wuce mu tafi"
cewar Inna Saude tana juyawa domin fita daga dakin.
Dauko daya daga cikin hijab dinta tayi ta saka wanda ya d'an zarta guiwarta,hakika taga mayafin da Inna Saude ta ijiye mata amma bazata iya fita dashi ba .
Bayan Inna Saude ta bi bayan ta saka talkaminta flat wad'anda Inna Saude tabata mamaki na sake cikata.
Tabbas yau Innarmu(sunnan da suke kiranta da shi) na cikin farin ciki wanda batasan dalilinsa ba.
Gidan Inna Laure aminiyar Inna Saude ta ga sun nufa zuciyarta ta d'an buga domin tasan cewa matar bata kaunarta ko miskala zarratin wani lokacin ma suna d'an samun sabani ita da Inna saude saboda ita.
Inna Laure ta kasance mai bakar zuciya ga bakin kishi ya yin da Inna Saude ta kasance bakin kishi kawai gareta sai kuma son kud'i wanda halinsu ne dukansu da'ace Agla hannun Inna laure take azabar da zataci sai tafi uban ta Inna Saude.
Da mota a kusa da gidan amma Agla bata lura ba tana chan wurin tunanin yaushe rabonta ta taka ko da kofar wannan gidan.
Da sallama suka shiga cikin gidan dakin Inna Laure suka nufa yayin da Aleeya ta yi tsaye a waje, gaisawa suka yi Inna na fadamata cewa..
"ga Aleeyar nan ki kirawo Fa'iza ta tafi da ita kinsan ba sanin kan gidan naku tayi ba ni kuma bai kamata na tafi zogo-zogo dani ba"
dariya mai kama da yake Inna laure tayi duk da cewa ranta ba dad'i tana kwala kiran sunan Fa'iza
Da d'an gudu Fa'iza tazo wacce sa'ar Salamatu ce ta shiga dakin,bana jin abun da suke cewa sai ga yarinyar ta fito tare da Inna Saude.
Dubanta Inna Saude tayi ya yin da ta matso dai-dai kunnenta ta na cewa..
"nasan halin ki baki kaucewa maganata da kuma ta Bappanki don haka kar ki kuskura naji kin yi wani abu wanda ba dai-dai ba ki je ciki zaki hadu da wanda zaki aura"
Shiru Aleeya tayi tana sauraren Inna a ziciyarta kuma tana mamakin wadannan zantukan da kuma wani zancen wanda kunnuwanta keji kamar almara.
Fa'iza ce ta dubeta tana cewa "Adda muje ciki"
Bin Fa'iza take harzuwa wani dakin wanda da'alama dakin Hindatu ne domin ya banbanta da duka dakunan gidan har tv plasma da kuma fridge akwai ciki,kallo daya ta yiwa dakin ta fuskanci hakan.
Da sallama suka shiga cikin dakin ya yin da sallamarta tayi ta cikin nusuwa kuma sautinta bai fita sosai ba,wani kamshin turare ya bugi hancinta mai dad'in kamshi har a zuciyarta turaren ya yi mata sosai, a tunaninta turaren da Hindatu ke amfani dashi (Hindatu ta kasance yaya a gurin Fa'iza,itace diyar Inna Laure ta fari )
Zaunawa tayi bisa kujerun dake cikin dakin madai-daita ya yin da kanta yake kasa,ita fa bata lura da waye a cikin dakin ba a tunaninta babu kowa,idan kuma hakane me yasa Inna Saude ta turo ta nan da kuma waye zata hadu?
Ahankali ta dago manyan idanunta masu dauke da zara-zaran eyelashes ta kalli kujerar dake gabanta caraf idanuwanta suka sauka cikin na.........🖊️🖊️🖊️
Zeesardaunerh ce
( Y'ar karamar su babbar su👧🥰🤩)
# comment
# like
# share
comment and vote d'inku shike Karamin kafin guiwar typing💋