ABDUL-MALEEK (BOBO)

由 BilynAbdull

203K 11.3K 90

Labarin mai nuni da muhimmancin biyayya ga iyaye, gujema son zuciya, soyayya, zuminci, tare da cakwakiya tsak... 更多

1
2
3
4
5
6
7
8
9
10
11
31
12
13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
26
27
28
29
30
32
33
34
35
36
37
38
39
40
41
42
43
44
45
46
47
48
49
50
51
52
53

25

3.4K 199 2
由 BilynAbdull

              💖ABDUL-MALEEK!!💖
                             (BOBO)

             Bilyn Abdull ce

Pg 26

Rahma tarungume Safna cikeda farinciki, itama rungumeta tayi Dan tayi kewar 'Yar k'anwarta abokiyar fad'anta, I miss you my lovely aunty.
    Miss u too my lili na.
     Safna tad'agota daga jikinta tana fad'in 'Yar lukutar ummi kinfa k'ara lukucewa, mi angon naki yake baki haka?.
    Rahma tarufe fuskarta saboda jin kunya, kai aunty Dan ALLAH ki bari.
   To na bari Safna tafad'a tana kama hannunta sukai cikin falon.
    Rahma ta kalli mazaunin Bobo wayam, Nawal ta kalla data maida hankalin akan game, baby ina papa?.
    Nawal tad'ago tana dariya, yashiga d'akinsa momy..... Tsayawa tayi tana kallon Safna, saikuma ta kalli Rahma, momy wacece wannan?.
    Aunty ce babyna.
Nawal ta taso ta rungume Safna, oyoyo aunty na.
   Itama safna rungumeta tayi tana fad'in oyoyo babyn mom.
   Bayan  sun zauna Safna sai bin Nawal da kallo takeyi, gani take kamar tasan yarinyar.
   Rahma tadire tiren kayan motsa baki agaban safna, tana fad'in wlhy aunty banyi zaton ganinkibafa.
   'Yar dariya safna tayi ta ce, ''saikuma gani kin ganni.
  Zama tayi sukafara hira, kamar basu bane sukeshan fad'a ada.
    Sun shagala sosai akan firar idon Safna ya sauka akan hoton Bobo, wani k'ululu cikinta yabada, batagama dawowa daidaiba Bobo yafito daga d'akinsa.
   Ah bak'uwa mukayi agidan??.
  
Afirgice safna tad'ago tana kallonsa, fad'uwar gaba, bugun zuciya, murd'awar ciki, duk suka k'ara samunta alokaci guda, yanda take raba ido akan Bobo sai kawai ya d'aure fuska.
   Itama Rahma kallonta takeyi ita atunaninta Safna taji kunyane akan abinda ta aikata abaya.
      Safna taduk'e k'anta bisa cinyarta danjin falon yana juya mata, jikinta sai rawa yakeyi, lallai ta tabbata kuka rahamane tunda gashi ita yau takasayinsa.
   Bobo yana zaune saman kujera yad'ora k'afa d'aya kan d'aya, dagashi har Rahma idanunsu nakan Safna, Nawal ma tana mak'ale abayan Rahma tana lek'en Safna, bobo yakalli Rahma, dama tanada wani ciwone?.
   Kai Rahma ta girgiza masa ta CE, ''amma dai ban saniba ko bayan nabar gidan.
   Lumshe idanunsa yayi ya ce, "bata ruwa tasha, Rahma ta tsiyayama Safna ruwa a Kofi tabata, jikin Safna na Rawa takar6a ta shanye duka tamik'ama Rahma kofin, k'ara mata bobo yasake fad'a.
  K'ara mata takumayi, aii ko ta shanyeshi tas.
   Rahma takalli Safna kamar zatayi kuka, aunty ki kwanta kihuta, kiringa fad'in _innalillahi wa'inna ilaihirraji'un_ zaki samu nutsuwa insha ALLAHU.
    BABU musu Safna tabi shawarar Rahma ta kwanta, dukda ayanzu jitake babu Wanda tatsana aduniya sama da Rahma d'in, jitake tamkar tatashi ta shak'eta ta mutu, talumshe idanu tana ambatar innalillahi..... Danjin zuciyarta tana shirin fashewa.

Bobo dai tuni yad'auke kai daga kallon Safna, ya maida hankalinsa ga TV.
    Bayan kamar minti15 Safna tad'anji Nutsuwa tazo mata, tabud'e ido tareda tashi.
   Rahma tai saurin fad'in aunty Yaya jikin?.
    Murmushi Safna tayi Wanda yafi kuka ciwo, da sauk'i kuyi hak'uri na rud'aku, juwace nakeji dama tun ina hanya.
    Sannu Rahma tashiga jero mata, Dan ita tayarda da zancen na Safna 100%.
        Bobo kam azuciyarsa ya ce, " juwar kuma bata tashiba saida kika ganni?, shifa Sam bai yarda da maganartaba, Dan haka yacigaba da kallonsa batareda yak'ara kallon ko inda sukeba.
    Safna kam tafad'i hakane saboda tunowa da maganar malaminta, dayace kota had'uda bobo karta nuna masa komai harsaitaje wajensa yabata wani sirri, da wannan tunanin tad'anji sanyi aranta, shiyyasa ta tashi ta zabga wannan k'aryar.
   Takai kallonta ga bobo daya maida hankali kan latsa wayarsa, muryarta na rawa ta ce, "ina yini.
   Lfy, kawai ya ce, " yamaida Kansa ga waya.

Falon yay shiru nawasu 'yan mintuna, safna dai satar kallon Bobo takeyi, sai yanzu yak'ara tabbatarwa da k'yak'yk'yawane ajin farko, Ashe ranar kallon tsoro sukayi masa, lallai ALLAH yayi halitta awajennan masha ALLAH, sai sambatun k'yawun bobo takeyi ita kad'ai zuciyarta.
        Rahma kam tayi shiru tana tunanin halin da safna tashiga yanzun nan, kome ke damun 'Yar uwar tata?.
         Bobo yamik'e Dan ganin kallon k'urillar da safna take masa, yakalli Rahma bara nad'an kwanta kafin sallar la'asar, kitadani idan lokaci yayi.
   To. Rahman tafad'a kanta ak'asa.
   Shikuma yanufi d'akinsa, harya shige safna tanabinsa da kallo.

Nawal ma tamik'e momy zanje wajen papa.
   A'a Nawal kibar papa ya huta kinga ya ce, "barci zaiyi, Nawal ta kwa6e fuska tana shirin yin kuka, momy nimafa barcin zanyi.
   Tokije d'akinmu ki kwanta, kamar gsk tanufi d'akin Rahma, dataga basa kallonta saita gudu d'akira, papan ta.
    Safna ta ce, " wannan yarinyarfa ina kuma samota?.
      d'an murmushi Rahma tayi, aunty yarinyarsa ce wadda matarsa tarasu tabari.
    Baki safna ta ta6e shine kekuma aka jajibo aka kawomiki?, kedai sakaraice wlhy, kina 'Yar yarinyarki har anfara kiranki da suna momy mtsoooow, nibansan randa kanji zai wayeba wlhy, danice agidannan wlhy saidai yasan Inda zaikai 'yarsa.
    Itadai Rahma batace komaiba, saima wasa da zoben hannunta datakeyi, amma har zuciyarta bataji dad'in maganar 'Yar uwartaba, aganinta aii d'a na kowane, kuma shida gidansa tahanashi ajiye Wanda yakeso?, itafa har zuciyarta tana k'aunar Nawal, kuma yanda zata rik'e 'ya'yan cikinta haka zata rik'e Nawal.

    Yana zaune abakin gado yana danna laptop Nawal tashigo.
   Lah papa bakayi barciba?.
     Bobo yad'ago yana kallon d'iyar tasa, banyi barciba babyna ya akayi?.
   Na cema momy zanzo wajenka, shine ta ce, " a'a wai nabarka kagaji zakayi barci naje d'akinmmu na kwanta.
   To miyasa bakije kin kwantaba?.
  Ai bata ganniba nikuma na gudo nan, ammafa karka gaya mata.
  Murmushi yayi Dan ganin yanda Nawal tazaro idanu saikace wata babba, to shikenan bazan fad'aba yanzu ya za'ayi?.
   Ta ce, "papa barci zanyi.
  To zoki kwanta, kan gadon tahawo ta kwanta, kwantar da kanta tayi kan k'afarsa daya tankwanshe, tana kallon rubutun dayakeyi a laptop suna labari, dahaka barci ya d'auketa, yagyara mata kwanciya dankar wuyanta yay sanyi.

Afalo kam safna da Rahma suna hira, dukda safna dauriya kawai takeyi, Dan zuciyarta na cikeda tsanar Rahma, dakuma haushin tashin bobo Afalon, Dan bata gaji da ganinsaba.
   Tamik'a mata sak'on ummi gashi inji ummi.
   Rahma takar6a ta na dubawa, miye kuma ummina tabani?, safna ta ta6e Baki ta ce, " zata kiraki tamiki bayani, kinga bari nawuce, safna tafad'a tana mik'ewa.
   Kai auntuna tun yanzu?, Rahma tai maganar tamkar zatayi kuka.
    Kenifa banason iyayi, dama kika samu Nazo shine zakimin Ta6ara.
    Sanin halinta yasa Rahma tai saurin fad'in yi hak'uri aunty Safna wlhy nayi kewarkune sosai. Dan ALLAH yaushe zaki dawo?.
      Kallonta kawai safna takeyi, zuciyarta na raya mata yarinya karkiyi farincikin sake zuwana, Dan waywayowata gidannan ba alkairi bane ba agarekj, bazan ta6a barmiki bobo ba, abayama kuskurene da rashin sani, amma ayanzu kam sai Inda k'arfina ya k'are, bobo nawane nikad'ai.....
...
  Ta6ata Rahma tayi aunty mikike tunani haka?.
    Ajiyar zuciya Safna ta sauke, ta k'ak'aro murmushi, karki damu zandawo kwannann.
    Cikeda farinciki Rahma tarungume safna.
    Kayan kwalliya ta had'a mata hadda wasu k'ananun kaya masu k'yau da aka saka mata alefe, safna takar6a ko godiya babu ta tafi.
    Har bakin mota tarakata, saida taga fitarta sannan tadawo ciki.
   Batanemi su Bobo ba tahau gyaran gidan, da shirin girkin dare.

Safna kam tana fita saitaji hawaye sunabin kumatunta, abinda takesonyi tun d'azu amma sukak'i zuwa, gangarawa tayi gefen titi tasamu guri tai farking, kifa kanta tayi a sitiyari tanata rabzar kuka tamkar ranta zai fita, sai surutai takeyi kamar Sabuwar kamu.
    Wlhy Rahma bazan barmiki Shiba, wlhy saidai idan ki mutu na mallakesa, kota halin k'ak'a saina rabaki dashi, idan ban samesaba mutuwa zanyi, Rahma miyasa zakimin haka ki auri abinda nafiso fiyeda komai arayuwata?, wlhy saikin barmin bobona, saikin barmin.....tasaki wani wahalallen kuka.

(Ni bilynku na ce, "kaga wani salo, Safna kinyi sake Rahma ta dafe.)

    Cikin matsanancin kuka Safna ta kira basira ta zayyane mata komai, ita kanta tarazana sosai danjin labarin, safna ta ce, "baseera miye mafita?, kibani shawara, wlhy kwakwalwata na gab da tarwatsewa nashiga uku baseera namutu.
   Kinga safna ki kwantar da hankalinki, gobe idan ALLAH yakaimu zamu koma wajen malam.
    Baseera muje yanzu please.
   A'a kiyi hak'urin goben, wlhy yau Abbana yana gida, kuma yasan banida lectures d'in yamma, baza'a barni na fitoba, kiyi hak'irin giben saimuje da sassafe.
    Shikenan safna tafad'a jiki a sanyaye.
    Motar taja tanufi gidan, Dan kukan datayi yad'an rage mata wani abun.
      ......
     Rahma tagama komai tak'ara saka turaren wuta, jin kwala kiran sallar la'asar yasata nufar d'akin bobo danta tadashi, kwankwasa k'ofar tayi dukda tasan yana barci, bata jira amsaba tashiga da sallama.
   Hakan tayi dai dai dafitowar bobo daga wanka, yana d'aure da fad'in tawul ita k'ugu zuwa guywa, hannunsa rik'e da k'arami ya ratayo a wuyansa.
   Da sauri Rahma tajuya zata fita tana fad'in ashema ka tashi.
   Eh natashi, ina zaki? Kizo kid'auki yarinyarki gatanan tamin barci ad'aki.
   Rahma tajuyo kanta ak'asa, Ashe nan tazo?, nazata tana d'akina?.
   A'a tana nan dama ta ce, "karna gaya miki gudowa tayi.
   Murmushi kawai Rahma tayi tad'auki Nawal tafice abinta.
   d'an murmushi yayi danganin yanda take Sinne kai da had'e hanya, yasan danta gansa babu kayane.

Tana falo yafito sanye cikin blue d'in wando da jar Riga, yayi k'yau sosai, Dan dama bobo akwai gayu gakuma tsafta, uwa uba k'yawun haiba.
   Yad'an kalli Rahma, bara naje masallaci, daga nan zan wuce gidansu Ammi.
   To ALLAH yatsare. Saika dawo.
   Amin yafad'a akan la66ansa, yafita yanamaijin dad'in addu'arta gareshi.
   Rahma tayi shiru tana mamakin yanda bobo kan sakata cikin al'amuransa ayanzu, komiye dalilin hakan?.

.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
     Safna tadanna uban hon, babu shiri baba mai gadi yabud'e mata gate, aguje tashiga gidan, tai farking, handbag d'inta kawai tad'auka tayi cikin gida, anan tabar kayan da Rahma ta bata, ALLAH yasota ma ummi na d'aki babu kowa afalon.
   Ta fad'a saman gadonta tana kuka, wlhy saina raba wannan auren, Dan bobo nawane nikad'ai, bazan ta6a zuba ido ina kallonsa amatsayin mijin k'anwataba, saina mallakesa kota halin k'ak'a, konawa zan kashe kuma koyaya iyayenmu zasu d'auki lamarin itadai saita mallaki bobo.
    Haka taita kuka har aka kira magriba, dama batayi sallar la'asarba, kuma da alama magribar ma babu niyya.
    Ummi takalli agogo waini ina safna tamak'alene har yanzu shiru?.
   Talatu mai aiki ta ce, "Hajiya aita dawo tun d'azu.
    Kai talatu da gsk?.
   Wlhy kuwa Hajiya.
Hankalin ummi ya kwanta takoma d'aki dama ko lazimi bata kammalaba tafito.

.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
     Bobo kam koda yay sallar la'asar saiya nufi gidansu, bayan sun gaisa da maigadi yashige ciki.
   Yakashe motar yafito, cikin kasaitarsa yanufi cikin gidan, afalo yatarar da khursiyya da khairiyya suna kokawa akan gyale.
    Tsaki yayi yana daka musu tsawa, kai dallah miye haka?.
   Da sauri suka nutsu.
   Ya ce, " Ku wad'anne irin shashashune?, kun kirma amma kunacin k'asa.
  Yaya gyalenefa na ajiye zansaka gobe idan zamuje gidanka, shine ta d'auka wai zata fitadashi yanzu......
   Karya take Yaya...
Katsesu yayi suduka, kumun shiru dallah, hannu yamik'a yakar6i gyalen, batareda yak'ara tankasuba ya haye saman Appa.
   Saida yaje k'arshen benen sannan yajuyo ya ce, "idan kun gadama kucigaba da fad'an harna sakko, yay shige warsa.

Khursiyya ta tura baki baba, hankalinki ya kwanta ya kwace duka, tobake kika jaba cewar khairiyya.
     Kardai Ku fasa, kuyi tayi harya dawo kune zakuci dukan banza tunda kunsan halinsa sarai, Ammi ce mai maganar tana fitowa daga kicin, Ashe duk abinda sukeyi tana jinsu.
    d'akinsu suka koma, kowa tana zum6ura baki gaba, Ammi ta girgiza kai tana nufar saman Appa itama............

繼續閱讀

You'll Also Like

1.9M 122K 73
# Scribe _ Aster_Rain # Start Date [ 5.1.2021] # End Date [ 26.5.2021] # Total Chapters _ [52 ]- Extra [15 ] Complete # Cv photo credit to orginal...
363K 14.2K 42
ကိုယ်ဟာ ကြိုးဝိုင်းထဲမှာ ကိုယ့်ကိုစိန်ခေါ်လာသမျှကောင်တွေအကုန် ထိုးရဲတယ် သတ်ရဲတယ် ကိုယ်နိုင်မယ်ဆိုတဲ့ယုံကြည်မှုရှိတယ် ကိုယ်မလုပ်ရဲတာဘာမှမရှိဘူးလို့ထင...
569K 30.3K 61
📌 fic ပါ အကြောင်းအရာများသည် သာသာ့စိတ်ကူးကမ္ဘာလေးအား ဖန်တီးထားခြင်းသာ 📌 ဆယ်ကျော်သက် အချစ်တွေက မတည်မြဲနိုင်ဘူးတဲ့...အဲ့စကားပြောတဲ့ စောက်ပါးစပ်တွေ ပိတ...