6

24 1 0
                                    

*****"Lafiya naga kina ɗingisa ƙafa?

Cewar Sadiq yana amsar kayan hannun ta.

"Wallahi wani ne ya taka min ƙafa...

"Ya taka miki ƙafa?

Ameer yayi saurin tarar numfashin ta.

Tace, "Ehh".

Mota ya buɗe yana zaunar da ita tare da ƙafar ganin yarda ta yatsan da aka taka wurin ya ɗan kumbura.

"Shi kuwa wannan wanne ɗan kut***ba ne da baya gani, baya lura tsabar renin hankali".

"Kuma kamar yana sane".

"Ke kuma baki mare shi ba?

Sadiq tsayawa kawai yayi yana kallan sa. Ehh lalle Ameer daman haka yake?

"Muje ki nuna min shi na ci kut***sa ko shi waye dan uban sa. Dan uwar sa baya shi da hankali ne? Kalli fa ƙafar ki fa".

"Ameer dan Allah mu tafi".

"Sai de uwar mu tafi".

Ya faɗa yana kama hannun ta, dan ta kai shi ciki. Ita kuma taki tashi.

Sadiq yace, "Dan Allah kayi haƙuri wuce muje mu tafi, ai ba wani serious issue ne ba".

"Uhm".

Ya yasa ƙafar ta a cikin motar ya buga murfin da ƙarfi sannan ya shiga gaba ya zauna yana cigaba da zazzaga masifa yayin da Sadiq da Zarah ido ne kawai na su.

"To wai ke uban me ya hana ki kau ɗa masa mari?

"Mari kuma?

Ta faɗa tana ɗan zare ido.

"Eh mari uban waye ce ya taki ki".

Har suke je yana banbami yana ƙuncin rai daƙyar ya sa yayi shiru ya dena mita. Inda suka bar shi anan duka dawo suka same shi sai de yanzu kuma yayi shirin tafiya masallaci ne jira kawai yake ayi kiran magrib ya wuce still de aikin yake yi. Buɗe gate ɗin da aka yi ne kamar a fusge da ƙarfi yasa shi kallan gate ɗin Ameer ne.

"Me ya faru?

Ya tambayi zuciyarsa amsar da bashi da ita, har ya rufe gate ɗin ya dawo kusa da shi be dena kallan sa ba. Ganin su Zarah sun fito tana rakin ƙafar da yanzu ta sake tashi dan ba ƙaramin take mata ƙafa yayi ba da takalmin. Shi kuma Sadiq yana riƙe da ita suka ƙara so suka zauna a kujerar kusa da Deeni. Shi kuma Sadiq yaje ya ɗauko wata kujerar suka shi a tsakiya.

"Me ya faru?

"Wani ɗan renin hankali ne ya taka ni".

Ta faɗa idan ta na zubar da hawaye.

Ameer yace, "Dalla Malama rufe wa mutane baki, da baki waskawa shege mari ba kina wani ɗan renin hankali".

Deeni yace, "Me ya faru?

Ameer yace, "Wani ya taka ta, kuma ta zo mu je na ci uwar sa taƙi yarda shima Ya Sadiq ya biye mata".

"Shine duk wannan ɗacin ran?

"Yaaaa".

Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya kalli ƙafar ya kalli Sadiq ya maida kallan sa ga Zarah ya ƙura mata kallo kamar wanda yake san ganin wani abu a jikin ta. Ya juya ya kalli Ameer sannan yayi murmushi.

Yace, "Ameer".

"Na'am".

"To ai har haƙuri ta bashi".

"Yaya ya za'a yi ta bashi haƙuri? Mutum ya maka laifi kuma sannan ka bashi haƙuri?

"Anyi haka ko ba'a yi ba Zarah?

ZARAHADDEEN Where stories live. Discover now