CHAPTER 68

3.4K 225 21
                                    

Inda mamaki na kashe mutum da yau yazeed ya mutu ganin yadda ya Tatar da matan nasa kasa boye farin cikinsa yayi hakan yasa ya sunbaci goshin s
Duka biyunsu saide ya lura akwai wani Abu a idon zakiyya wadda ya kasa gane alkhairi ne ko tsiya fatansa dai Allah yasa zaman lafiyan ya dore.

Su safwan ne suka rugo a guje Suna fadin daddy saura mu tare da juya masa gefen kumatun nasu. Janye jikinsa yayi Daga na matan nashi kamin ya tsuguna ya rungumesu tare da sumbatarsu. Sallama Mashkur da lukman sukayi hakan yasa minal janyo hijab dinta dake hannun kujera yayin da zakiyya tayi kitchen domin a can tabar hijab dinta. Aiko sai gata da zumbulelen hijabi.

Sakan baki yazeed yayi Dan bai gaskata abinda yake gani ba. Mashkur ne yace uhm su mai iyali manya.
Safwan ne ya lura da gaba daya hankalin shi baya Kansu gashi ya saki baki. Inda yake kalla yaji kamin yayi dariya kasa kasa yasa Hannu ya rufewa yazeed bakin tareda fadin daddy kuda zai Shiga bakin ka. Sai lokacin yazeed ya kallesu tare da Cewa muje muci abinci ko.

A tare su minal suka Shirya Komai yayinda zaliha da lukman Keta rafkawa juna harara. Min ta lura da haka.

Zakiyya ce ta fara zuba abincin. Ta zubawa su sahir da yazeed the next one Mashkur ne minal tace aunty kawo kawai. Zakiyya tace barshi in zuba. Murmushi minal tayi tace ai yanzu ma kinyi kokari kallon yazeed tayi tace kasan Cewa yau aunty zakiyya ce tayi mana girki? Yace haba shiyasa naji kamshin ya chanja. Kuce zakiyyan nawa chef ce. Kallon minal yayi da alamu maganar ta tabata kishin ya motsa yayi da zakiyya ke murmushi minal ko taci gaba da zuba abincin. Taci gaba da cewa nikam ina yiwa Allah godiya daya hada ni da mata Wanda babu yasu ga kyau ga iya girki. Nikam ban Masan wace tafi wacce ba.

Murmushi dukansu biyu su kayi. Abincin yakai baki ba laifi yayi dadi amma yasan babu macen da zata kara da minal dinshi wajen dafa abinci.
Ajiyan zuciya ya sauke yace Ashe haka dama adalcin keda wahala Idan ka yaba daya sai ka yaba dayan? Wannan shine adalci a magana. Hmm Toh faa Gaskiya da aiki a gaba na.

Minal tana isowa kan zaliha dake gefen lukman Wanda Keta dangwalarta Dan ya gano ba abinda ta tsana Kamar tsokana Dan haka ya mayar da ita abin wasa. Tace kash na manta bamu kira mom ba. Bari kawai nakai mata daki zally zuba naki ki zuba na habibin ki.

Wani kallo ta aika mata kallon Idan na kamaki Allah ya jikan ki.
Gwaliyo ta mata kamin ta dale sama abinta. Zubawa zaliha tayi badan ranta yaso ba yayi da lukman ya kashe mata ido. Aiko ta kara cika amma ba yanda ta iya sai yake takeyi.

Yazeed ma ya gano dalilin minal na yin hakan. Cinye abincinsa yayi yayi wa zakiyya alamun ta sameshi a daki.

Bayan mintuna sai gata zaunar da ita yayi a bakin gado yace my zakiyya agaskiya Nayi farincikin yadda na dawo na samu gidana yau gashi kinyi Shiga ta addini kin zama mata ta gari bakisan yadda nakeji a zuciyata ba wallahi. Na rokeki da Allah karki canja halinnan. Matsowa yayi zai sumbaceta ta kauce. Kallon yayi da alaman lafiya? Mikewa tayi tace bana sallah. Kamin ta fice. Jinjina kai yayi yace tooh? Anya kuwa?

Zakiyya ko tana fita dakinta ta fada gado ta soma kuka aranta tana fadin ka yafeni yazeed amma inaso in manta dakai. Inaso in daina sanka shiyasa bazan yarda mu dinga karfafa alakarmu ba ka yafemin. Rayuwar auren mu na Dan wani lokaci ne.

Koda minal ta dawo bata kalli Inda su zally suke ba Dan tasan sakamakon. Dakin yazeed ta nufa har ta tura kofar sai wani tunani yazo mata what if yana tare da zakiyya ne. Memakon tayi knocking Dan rashin wayo sai ta leka ganinshi tayi yana shan magani hakan yasa ta Shiga tare da warcewa da Sauri. Duba sunan maganin tayi taga bata gane ba hakan yasa ta fara karanta uses dinsa kokarin kwacewa yazeed yayi amma ya makara domin ta karanta kuma ta gane Cewa maganin rage karfin libido ne. Ranta ne ya back idonta ya kada yayi ja. Cillo masa maganin tayi tare da fadin me wannan? Kace maka me wannan ? Tuni hawaye ya fara zubowa tace haba ya yazeed me kake shirin wulla mu ciki yanzu da ace mom ne taga wannan me zata dauka? Ace kanada mata biyu amma kanashan maganin rage sha'awa. Ka taba zuwa wurina na hanaka hakkinka ne? Daga murya tayi tace NACE KA TABA ZUWA WAJENA KA NUNA KANADA BUKATA NA HANAKA? Me kakeso ka nunawa duniya yakai mijina? Shin bamukai ka kusancemu bane? abin tausayi yazeed ya Koma dan yaji kunya yadda kasan da uwarsa na masa fada. Ya matso ya riko hannunta idanunsa sun cicciko yace ba haka bane na dauka bakisan wannan abin bane ni kuma banason na kawo miki shi lokaci daya kar Nayi gaggawa. Harararsa tayi tace a da ba amma banda yanzu domin kan mage ya wa.....

KURUCIYAR MINALWhere stories live. Discover now