page 14

97 7 0
                                    

🤳🏻

⏳🕹⏳🕹⏳🕹
нalιn dana ѕнιga...
⏳🕹⏳🕹⏳🕹

~Labarin gaske ne~

© ᴬYˢᴴᴬ ᴹᴬᶜᴴᴵᴷᴬ

w̲̅a̲̅t̲̅t̲̅p̲̅a̲̅d̲̅~a̲̅y̲̅s̲̅h̲̅a̲̅m̲̅a̲̅c̲̅h̲̅i̲̅k̲̅a̲̅ 1984

*_Not edited_*


💘 *14* 💘

بسم الله الرحمن الر حيم



Muhammad ya shigemin rayuws ya cusa kanshi gareni tun ina ƙi ina basar dashi da nuna mishi tsana har dai nasake na fara sauraronshi musamman dana kula da duk irin tsana da wulaƙancin da nake mishi baya fishi in zaizo yau na zagi Uwashi na zagi Ubanshi ba zai hana mishi dawowa gobe ba kai har marinshi na taɓa yi n akutuntumishi ashar amma ko a jikinshi, wannan bai hana kiran wayata ba cikin dare, washe gari da farar safiya wayarshi ce tatasheni, da yamma yana ƙofar gidanmu kaini wani lokacin nacinshi da rashin zuciyarshi har mamaki suke bani.

Abinda ya rinƙa jan hankalina gareshi muryar da yake mafani da ita wajen yi min magana, muryar da yake amfani da ita ce as Ibaraheem..

Koya yai min magana da ita nakan natsu n amaida hankalin agaba ɗaya zuwa gareshi, sai da ya kaiga inya kira muna magana ko alama bana son muyi sallama balle na daina jin dadaɗar muryar dana ƙwallafa rai akanta.

Na dawo makaranta abinci kawai naci natafi gidan Anti Lubah, muna fira wayar Muhammad ta shigo, wayar na hannunta ta miƙo tana faɗin gafa mera dil.. naki, n aƙarba ina dariya na ce ba dai Real one ɗin ba..

Na amsa wayar da sallama bai amsa mani ba sai cewa yayi I love you Asi, nai shiru kamar koda yaushe kalmar ta shigeni yadda ya dace na maida martani sai dai matsalar wannan Muhammad ne bawai wanda nake tsammani ba Ibraheem.

Baki ce komai ba Asi? Ya katse shirun da mukayi yaci gaba da cews wai menen aibuna Asiyah?

Abu da yawa na faɗa ahankali, yace waike bakiyi afuwane?

Nai guntun murmushi na ce da banayi dako gaisuwa bata haɗamu ba balle ta kaiga musayar magana, nasan da wannan amma ni matsalata dake kin kasa sakin jiki dani, kamar ya kenan? Na tambayeshi, nasha faɗa miki ina ƙaunarki amma ban taɓa jin martanin kalmar daga gareki ba.

Na ɗan rintse ido na ce abinda kawai kake son ji daga gareni kenan? Ƙwarai ya faɗa.

Nai ƙasa da murya tare da tausasata kwarai na ce ina sonka Ibraheem...

Dukan da Anti Lubah taimin ya hanani jin farkon maganar shi sai ƙarshen inda naji , haba Asiyah Muhammad ne fa, na yatsina fuska na ce na sani...zai sake magana na katseshi kayi haƙuri ina tare da Anti Lubah kanemeni anjima, banjira daga gareshi ba na kashe wayar.

Na kalli Anti Lubah dake bayanin wulaƙanci dai bai da kyau, na ce wai kema ganinki wulaƙanci nake mishi? Na girgiza kai na ce da zan mishi wulaƙanci wallahi ko'a hanya muka haɗu ba zai nuna ya sanni ba...


Da daddare ina ɗakina ina duba testbook saboda akwai gwajin da zamuyi washe gari, wayar Muhammad ta shigo na amsa da sallama...yai saurin tare maganar da zanyi da cewa na damu dake sosai Asi ina sonki da yawa.

Nai ƴar dariya na ce na daɗe ina sanar da kai ina ƙaunarka Ibraheem, yai tsaki yace Muhammad ne fa, nima nai tsakin na ce na sani, yai shiru lokaci kaɗan ya nisa yace wai meyake damunki ne Asiyah?

Kai zan tambaya Muhammad, toni dai dan Allah ki daina kirana Ibraheem, akan me? Na tambayeshi, hakanan dan bana son sunan, nayi dariya ƙasa-ƙasa na ce to saika kyaleni in baka son na kiraka dashi, danni harshena da zuciyata sunanshi kawau suka sani, shi suka aminta dashi danya zamo makusancinsu abokin rayuwarsu.

HALIN DANA SHIGA...Nơi câu chuyện tồn tại. Hãy khám phá bây giờ