page 12

95 8 0
                                    

🤳🏻

⏳🕹⏳🕹⏳🕹
нalιn dana ѕнιga...
⏳🕹⏳🕹⏳🕹

~Labarin gaske ne~

© ᴬYˢᴴᴬ ᴹᴬᶜᴴᴵᴷᴬ

w̲̅a̲̅t̲̅t̲̅p̲̅a̲̅d̲̅~a̲̅y̲̅s̲̅h̲̅a̲̅m̲̅a̲̅c̲̅h̲̅i̲̅k̲̅a̲̅ 1984

*_Not edited_*

*S͢A͢D͢A͢U͢K͢A͢R͢ WA G͢A͢R͢E͢K͢U*...

*ᴷᴴᴬᴰᴵᶻᴬ ᵁˢᴹᴬᴺ*
*ᴺᴬᴮᴵᴸᴬ ˢᵁᴸᴬᴵᴹᴬᴺ*
*Ɗᴬᴵᵞᵞᴵᴮᴬ ᴵᴰᴿᴵˢ*
*ᴴᴬᵁᵂᴬ ᴬᴸᴵᵞᵁ ᴿᴬᴮᴬᴴ*
*ᶠᴬᵁᶻᴵᵞᵞᴬ ᴰᴬᵁᴰᴬ*


💘 *12* 💘


بسم الله الرحمن الر حيم








Mun kusa mintina goma tsaye muna kallon juna, azuciyata ina raya abubuwa da dama, ji nake kamar naje na rufeshi da duka naita ƙudunduma mashi ashar, zagi na rashin mutunci irin wanda shi da kanshi sai yaji ya tsaneni ( To amma ko nayi hakan ribar me zanci, illa ce dai sun riga sunyi mani).

A hankali na ɗauke ido kanshi na samu waje na zauna nai ƙasa da kai, ya samu waje ya zauna kusa dani, ban kalleshi ba shima bai tankani ba, shiru na ɗan tsayin lokaci, daga bisani naji fitar numfashinshi tare da tashin muryarshi...

Kiyi haƙuri Asiyah, na tada kai na kalleshi na ce haƙuri?

Akan me Muhammad, na san mun zalunceki mun shiga haƙƙinki mun haifar maki da damuwa da tashin hankali, amma ina son ki yarda akan wallahi ba laifina bane...

Ƴar dariya nayi na ce na tambayeka mana Muhammad, ya ɗaga kai da faɗin ina jinki, na ce dan Allah taya kake sarrafa muryarka wajen magana dani as Ibraheem?

Yai ɗan shiru ynaa kallon ƙasa daga bisani ya ɗago ya ce natsuwa nake na cire wasa araina sai na tausasa muryata nayi ƙasa da ita sosai.

Na runtse ido da ƙarfi cikin takaici da yarda da abinda yace na ce daure ka gwada min yanda kakeyi, kamar ba zaiyi ba sai kuma can ya ɗauko waya daga aljihu ya kai kunnenshi...

Nan naga ya natsu ya maida hankalinshi gaba ɗaya kan wayar bayan ya ɗora yatsunshi biyu akai sannan ya fara magana ahankali cikin tausa murya...

Ina sonki Asi, irin son da ban taɓa tsammanin anaiwa wani rai ba, na zamo wawa sakarai akan ƙaunarki,. *halin dana shiga* mai girmane adalilin sonki, na kan jini atakure aƙuntace hankalina baya kwanciya har sai na furta maki ina sonki ina ƙaunarki ina muraɗin kasancewa tare dake.

Da zaki taimakeni Asi da na roƙi arzikin ki dawo da alaƙar soyayyarki gareni karki duba girman laifina agareki...ina sonki da yawa ni Muhammad ki taimaka kar ƙaunarki tiamin illah...

Na bishi da kallon tsana inda na ƙara gasganta lallai shi ne dai, ba tare dana tankashi ba na tsallakeshi na shige guda zuciyata ta ƙara cika da tsanarshi, a yanzu kam na ƙara yarda Muhammad shi ne Ibraheem, haƙiƙa ayanzu na tabbata son da nai gaibu naiwa, na so iska na so babu kai anzalunceni da yawa an taɓa zuciyata.

<<<<<<<<<<<<<<<<<<

Duk yarda na so na cire son Ibraheem azuciyata na kasa, duk yanda naso na yarda babu shi ɗin nakan so na yarda a duk lokacin danai ƙoƙarin na amince babushi sai zuciyata ta bijiro min da batun mutumin nan mai baƙaƙen kaya sai gaba ɗaya nabi na sukurkuce.

Wata matsifa shi kanshi mai baƙaƙen kayan na yarda bashi bane Ibraheem amma zuciyata ta afu akan matsanincin ƙaunarshi domin ni shi aka dangantamin da cewar shi ne, dan haka ne dai nasakankance akan koshi waye shi na baiwa soyayyata da zuciyata kai dama kaina gaba ɗaya.



HALIN DANA SHIGA...Where stories live. Discover now