BABI NA GOMA SHA TARA

1.8K 143 4
                                    


                    🥀NOOR IMAN🥀

*Fatima Muhammad Gurin*
            •Gureenjo6763 on Wattpad•

*'Yar Mutan Adamawa*

💫ANNUR WRITERS ASSOCIATION
(Home of peace, honor, charity and super writers)

*dedicated to MUKARU DA JUNA group thank yhu so very much🥰🥰*

                         *019*

Da tsananin mamaki Abba ke kallon baba, wani irin uba ne wannan? Wani irin ubane ze so 'yarshi ta auri mashayi bayan ya san outcomes na zaman aurenta? Ya yarda ze bada 'yarshi ba bincike ba komai? Yanzu kai be ma san me ze iya cewa akan baba ba, Da kyar ya iya had'a "Toh Toh zamu duba In zamu iya had'a komai kan juma'an" baba yace "a'a ba se kun had'a komai ba ma na hutace ku har sadaki ni zan biya mishi" Abba yayi saurin cewa "A'a wannan kam ze biya amma sauran abubuwan se a hankali ze mata ka san yanayin rayuwan", godiya baba ya d'inga yi kaman wadda aka ce an baiwa kujerar Makkah alhalin jin daad'in ya rabu da kaya yake yi kuma yayi alkawarin wannan karon ta kashe auren wallahi se ta bar mishi gida.

Cike da tausayin iman Abba ya tafi, se yaji wani sonta a matsayin 'ya ya shige shi kai koda ace rabuwa sukayi da Abdul, ba fata yake yi ba baze ta'ba barinta ta dawo gidan nan ba ze ci gaba da riketa har Allah yasa ta samu wani mijin kuma.

******

Tun 8pm suka fara presentation d'in amma sam hankalinshi kwata kwata baya kan abinda akeyi tunani kawai yake ko me Abba yake tattaunawa da baba? Ko ya yarda ya bada auren? "Dr. Abdulraheem Ahmad Malabo do yhu have anything to say?" Da sauri ya mike yana cewa "yes sure" kan ya tattari abinda ze yi presenting ya fita ya farayi cikin had'add'iyar turancinshi.

******

Tunda ta farka daga alluran take kwance kawai ita kad'ai ta san abinda take sakawa a zuciyarta, Allah ya gani tayi iya hakurin da zata iya yi, ta gaji hakanan, so ta yanke shawaran ana sallamanta daga asibitin nan bazata jira wani auren tozarcin da baba ze mata ba, zata tafi chan inda ba wanda ya santa tayi irin rayuwar da zata ji daad'i, ta'ba kafanta da akayi ne yasata maida hankali kan wadda ya ta'ban.

Murmushi tayi kan ta d'auke idanunta tana mikewa zaune tace "zarah kin dawo?" Zarah tace "yes sarkin tunani na dawo, meyasa kike son takura kanki da tunani ne? Ko kin manta duk abinda ya faru da bawa Allah ya riga ya rubuta tun kan a hallice shi? Ki d'auki matsalanki a matsayin ba komai ba zakiga ya wuce". Iman tace "kayyah zarah kowa haka yake cemin ze wuce ze wuce amma banga alamu ba".

Zarah tace "chuppp ze wuce in shaa Allahu" zama tayi ta d'iba mata abincin da ta kawo a plate tare da gyara zama da kyau tace "haa open your mouth" dariya iman ta saka tana cewa "ke me haka se kace wata baby? Come on bani zan iya ci da kaina" zarah tace bata san zancen ba ai bata da lafiya se ta bata cokali take ta kokarin sawa a bakinta yayin da ita kuma take ta kawar da kai tana sa hannu cikin dariya suke tayi seda zarah taga iman tayi dariya sossai kan ta mikamata chokalin tana murmushi.

Kar'ba tayi ta fara ci zarah na ta bata labarin ban dariya, yawanci duk akan 'yan gidansu da yadda take musu rigima da fad'an ummu In an ta'bo Anty hamna da fad'an Abdul da hamna, da yadda suke kawo kara kullum musamman hamna se dariya iman keyi musamman yadda zarahn ke yi da fuska duk irin labarin da zatayi se tayi expiration d'in so childish.

A haka iman ta cinye abincin plate d'in tas ba tare da ta lura ba, dafa kafad'an zarah tayi tace "thank yhu zarah, kin ragemin damuwana sossai, In Ina tare dake har mantawa nake da wani damuwa" zarah tana murmushi tace "you are welcome dear, bari inzo In tafi yau nayi dare a waje" Iman tace "Eyyah de karki tafi plz ki kwana dani yau" zarah tace "Da ummu zata yarda da nafi kowa farin ciki amma bata yarda in kwana a ko Ina".

NOOR IMANWhere stories live. Discover now