BABI NA GOMA SHA BIYAR

1.8K 163 5
                                    


                  🥀NOOR IMAN🥀

*Fatima Muhammad Gurin*
            •Gureenjo6763 on Wattpad•

*'Yar Mutan Adamawa*

💫ANNUR WRITERS ASSOCIATION
(Home of peace, honor, charity and super writers)

                       *015*

"Yanzu ke dama iman kina da saurayi irin wannan shine kike d'aga hankalinki akan maganan mahaifinki?" Cewar mama tana kallon noor iman, cikin jin kunya noor tace "Ai na fad'a mishi abinda baba yace mama" cikin jin daad'i tace "masha Allah, na san in sunje babanku baze sa bukin da nisa ba kiyi ki warke mu je In fara gyara ki 'yata" murmushi kawai noor tayi tana girgiza kai.

Wayanta ta janyo ta kunna data bata cikin wasu groups dayawa haka bata da contacts dayawa ta tabbatar a whatsapp d'inma In ba hammad na nan bane ba me d'ebe mata kewa d'an gwara zarah, ganin sako a cikin group d'insu na school ne yasa ta shiga ciki don ganin me aka turo, wani irin fad'uwa gabanta yayi "Doctor malabo ze yi test gobe?" Ta furta a fili cike da damuwa.

Toh ya zatayi bari doctor yazo ita kam zata ce a sallameta ta warke In tayi missing test d'innan da matsala, karan shigowan wani sakon ya sata maida hankali kan wayan zarah ce "me mara lafiya ke yi whatsapp a irin wannan time d'in?" 'Bata fuska tayi tare da yin typing "zarah kinga abinda na gani a group? Yayanki fah test ze yi gobe ban san ya zanyi ba".

Zarah tace "haba dae?😳" noor ji tayi idonta ya cika da hawaye se take ganin kaman da gayya yayi hakan zarah tace "kar ki d'aga hankalinki plz besty, yanzu rubuta mishi sako zakiyi na baki da lafiya kan In shiga school d'in se in biyo In kar'ba se In ba class rep ya bashi watakila In kin warke ya miki make up" noor de cikin sanyin jiki tace "Ohk na gode da shawaranki zarah bari yanzu In rubuta".

Kallon mama tayi tace "dan Allah mama Ina son yin rubutu a paper ya za'ayi?" Mama tace "toooh babanki yacemin ze zo kan ya wuce gida bari In ce mishi ya sayo miki foolscap d'in da biro" godiya noor tayi mama ta kirashi da kyar ya yarda ze sayo, bayan ya kawo ta natsu ta rubuta letter d'in cikin kyakyawan handwriting d'inta bayan ta gama ta nad'e ta Adana.

Wata nurse ce ta shigo ta yi mata wasu allurai nan take bacci ya kwashe ta.

*****

"Wato ni zaka nunawa iyakata ko Muhammad? Akan yarinyar da bata da tarbiya da kamun kai kake neman yi min jayayya? Toh yayi kyau, Ina so ka bud'e kunnenka da kyau ka jini har abada kana ji? Har abada ni mahaifiyarka ban amince ka auri yarinyar nan ba ko bayan raina ka aureta ban yafe maka ba, itama yarinyar In asiri ta maka zan je har gidansu in nuna mata kaina ta ganni da kyau wallahi na fi karfin asirinta bade zuri'ata ba".

Hammad ya ce "mom kiyi hakuri plz wallahi zan rabu da ita ba se kinje gidansu ba, abinda yasa har yanzun ma ban rabu da ita ba bata da lafiya ne tana asibiti ba zan iya gayamata cikin situation d'in da take ba, In shaa..." katse shi tayi "na hutace ka zan gayamata da kaina" cikin sanyin murya yace "dan Allah m..." "tashi ka fice ka bani wuri" mikewa yayi jiki a sanyaye ya fice.

Dole ba yadda ya iya yau In ya shiga wurinta ya fad'a mata tayi hakuri ta nemi wani shi kam an mishi iyaka da ita.

*********

Cikin nishad'i yayi test d'inshi ya gama, test d'in da ya basu wahala magana d'aya kayi out, sannan ya kama masu satan amsa dayawa waenda ya yi cancelling test d'in nasu, bayan ya fita ne class rep ya bishi har office ya bashi letter d'in iman akan she is sick bata samu zuwa rubuta test d'in ba, kar'ba kawai yayi ya wuce abinshi.

Kurawa handwriting d'inta ido yayi yana kallo na mintuna kan ya fara karanta lettern, tayi sakon ne cikin hankali ba hayaniya sam wadda hakan ya sashi jin ba daad'in test d'in da yayi da gayya amma shi a ganinshi hakan ne kad'ai hanyar da ze samu don yi mata tambayoyi akan rayuwanta, bud'e briefcase d'inshi yayi ya Adana lettern kan ya hau duba tests d'in da yayin yana cikin dubawa kuma se aka kirashi zasuyi meeting, mikewa yayi ya wuce d'akin taron.

NOOR IMANWhere stories live. Discover now