ALIYU GADANGA..!

1.8K 120 0
                                    

*ALIYU GADANGA..!*
   _(The Story of yuong soldier man)_

Wattpad:Janafnancy12
*Hakkin mallaka:Janaf*

*DEDICATED TO MY MOMMAH...,HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*

_Special gift to my Real Dota RAHMA😘 Ladingo yar mutan Niger_

*Intelligent writer's asso*✏

_*Special Thanks to Hussain80k😝 and HassanATK...Sakallahu Filjannah Dudes😘*_

*NOT EDITED*💥

*Chapter4*

   ""Kwanan Suwaiba biyu a Asibitin kafin asallamota tadawo gida,Bala yayi Namijin kokari akan Suwaiba domin Duk Abunda uba ke ma da,da Abunda miji zai ma matarsa sai da yayimata shi,mallam lawal da matarsa Fati suma sunyi namijin kokari kan Suwaiba,Fatima nan take wuni sai dare take komawa gida,ita zata sanyama Suwaiba ruwan wanka ta juyemata,kafin tazo tayima Aliyu wanka wanda Sunan da bala ya sanyamai kenan,Suwaiba bata nemi komai tarasa ba na bangaren rayuwa,bangaren yar"uwa kuwa Fatima ta koremata dukkan kishirruwan su.

Kwanan Bala uku agarin Gombe yakoma Kaduna bakin aikinsa,Ranar suna tana zagayowa aka Yankama Aliyu raguna guda biyu,makota da yan"uwan Fatima dana mallam lawal sunzo tayasu murna,dayake suma din yan Asalin Yan gombe ne,Anyi Abun cikin Mutumci da jin dadi,Suwaiba tacigaba da kula da kanta tare da Danta,duk da mutanen anguwa sunata zunde cewa tazo anguwan da ciki ta haifeshi batare da nuna alamun tana da Aure ba,domin ada sun zata Bala ne mijinta,ammh sai daga baya suka Fahimci cewa yayantane ba mijinta ba,duk da haka Suwaiba ta toshe kunnanta bataji bata gani,ta dauki nasihan dan"uwanta daya cemata ta maida hankalinta wajen kula da kanta da Abunda ta haifa.

  Aliyu nada Shekara uku aduniya babu inda baya zuwa yayi wayau haryafara Tafiya,alokacin ne kuma Bala yayi Aure da matarsa Umaima yar kadunane Haifaffiyar Kabala ce,mahaifinta shima tsohon dan siyasa ne,tunda shine tsohon mataimakin gwamna a gwannatin data sauka,Akwai girmamawa tsakaninsa da Bala,tun mahaifisu na raye yasan mallam,tunda yace sunyi karatu wajensa,to shigowar Bala harkan Siyasa ne,yasa suka sanjuna,kuma shida kanshi yayimai tayin Auren diyarsa tasa Umaimah,anyi biki lafiya amarya tatare agidanshi dake Anguwan Dosa,gidan yana da girma wanda Bala yadau tsawon lokaci yana ginashi,bayan Aurensu da wata biyu ya dauketa yakaita gombe don ta gana da Kanwarsa Suwaiba,hakika Umaima ta tsausayama Suwaiba ganin inda takoma da rayuwa daga ita sai Da"nta Aliyu wanda yana girma wayonsa da kwazonsa da Karfinsa tare da kamaninsa da mahaifinsa suna kara bayyana,awannan zuwan ne Bala ya sanya Aliyu awata mkranta da"a ke kira MATRIC INTERNATIONAL SCHOOL GOMBE..,Mkrantace mai tsada domin sai ya'yan wane da wane,kowani kusa agwannati ko yan siyasa,Cikin nasara da hazaka Aliyu yafara karatunsa Koda akayimai interview Malaman mkarantan sunyi mamakin kaifin basiran yaron,duk da ance baitaba hallartan mkranta,ammh dayake Suwaiba bata wasa zama take dashi takoyamai Dak da iya Abunda tasani na boko dana Arabi,Nursery 2 aka sanyasa saboda yadda sukaga yaron da kaifin kwakwakwa,kafin Aliyu ya rufe shekara sunansa yayi Tambari a mkranatar nan saboda yadda Allah yayima yaron baiwan karatu Shiganshi Shashen primary yasa sunanshi yakara fitowa domin koda yakeda kankantar shekaru ana zuwa dashi gasan mkranta.

   Watan Umaima tara ta haifo santalelen Danta mai kama da ubansa sak,Ranar suna yaro yaci sunan HAISAM,wanda tsakaninsa da Aliyu shekaru hudu ne,bayan shi tazo tayi yan biyu, MARDIYA DA MADINA,Daganan bata kara haihuwa ba, haihuwar Haisam dai Suwaiba bata samu zuwa Kaduna ba saboda mkranatar Aliyu,sai haihuwar yan biyu ne taje kaduna saboda lokacin su Aliyu sun samu hutun mkaranta,sati daya sukayi akaduna kafin Su dawo gombe,Suwaiba tasan yarda take da Aliyu,tun yana yaro,yana da kiriniya da kuma son wasa,ammh bata bari yana Fita,sai dai in zai fita wajene ya zauna wajen mallam lawal,kokuma Fatima tatafi dashi gida,ammh kuma baya zama,da fari ta sanyashi a islamiya anan anguwan ammh sai yaran mkranta suka fara kyamatarsa da kokarim kiransa da wanda bai da uba,Kullum da kuka yake dawowa,yana fadama Suwaiba Abun na damunta,tana tsoron kada su sanyama yaronta wani banzan Tunani,sai kawai ta cireshi ita takoma malamarsa tunda daidai gwargwardo tana da ilimin Addinin harda na boko,sai takoma tana koyar dashi agida,tun yana yaronsa Suwaiba ta fahimci Danta yana da bala"in zuciya gashi tun yana karaminsa yake da bala"in karfi kamar doki,shiyasa take binsa ahankali,Abu dayane yake cimata tuwo a kwayar irin sunan da yan anguwa suka sanyama Danta wai DA'N MACE,tun Abun bai damunta harYafara damunta,shiko Aliyu tun yana dukan yara in sun kirashi da sunan haryakura yafara amsawa,saboda ya yarda shi din Da'n mace ne,ammh kuma macen ta bambamta da sauran mata saboda jajircewanta akan Rayuwar Dan"ta.

ALIYU GADANGAWhere stories live. Discover now