164

660 50 0
                                    

*NAJWA*

BY *Maryam S Indabawa*
*Mans*

Dedicated to *Rashida A Kardam*
*Anty Rash*

*Allah dafa miki. Allah karawa Mama lafiya da nisan kwana. Ameen*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da juriya online writers*

*Allah kara mana hakuri da juriya.*
*Ameen*

*Gidan aminci da karamci. Allah kara basira Ameen*

Page
*164*


*Na gaida ku yan kungiyar HAJOW Allah ya kare mana ku gaba daya.  Allah kara mana hakuri da juriya da son junan mu. Ina alfahari daku.*

*Maman mu maganin kukan mu Hajiya Nafisa jinjina ban girma gareki. Allah Ubangiji yasa kifi haka, Allah tasare mana ke da yan uwan mu.*






Bayan ya dawo Mami ta tafi gidan dan ta kimtsa.

Acan tayo musu abinci, Sannan suka taho tare dasu Bara'atu.

Shi kuma yayi wanka ya shirya ya dawo kusa da Najwa yana kallon ta.

Komai da yake yi karfin hali ne amman jikin sa babu gwari ko kadan.

Duniyar tai masa zafi ya rasa abinyi, tsoro yake ji tsoro ba kadan ba ma.

Yana son Najwa, ya fada ya kara fada Najwa ita ce Rayuwar sa.

Son Najwa shine jinin jikin sa. Zai iya sadaukar da komai dan samun farin cikin Najwa.

Kai be ki ya bata rayuwar sa ba ma. Najwa duniya ce, duniyar sa me zaman kan ta.

Samun mace kamar Najwa ba abune mai sauki ba, ya tabbata ya rasa Najwa bazai samu wacce zata maye gurbin sa ba.

Yana rasa kalmar da zai mata bayanin irin son da yake mata, amman yana jin dadi in ya nuna mata son da yake mata a rayuwar auren su.

Ya tabbata tana yadda, Ya tabbata yana sata farin ciki ya mantar da ita duk wani abu wanda yasan komai manta shin take a lokacin shi kadai take gani da tinawa tare da bashi kwarin gwiwa wajen isar da sakon da yake son isar wa.

Yana son Kalar soyayyar da Najwa ke nuna masa, ya tabbata ba kowa yake samun kwatan abinda yake samu ba.

Ya tabbatar da shima Najwa na son sa. Be son bacin ran ta ko kadan farin cikin ta shine abin son sa a koda yaushe.

Yarinya yar albarka me daraja da girma a gunsa.

Ai inda sai namiji ya daga kafa matar sa zata shiga Aljanna to ya tabbata kafar sa a dage zata kasan ce kullum dam Najwa ta samu Aljanna madaukaki ya ta daban.

Yana son Najwa yana kaunar ta, be taba jin son ta ya ragu ba sai daduwa da yake.

Amman duk lokacin da ya kama wacce tai wannan abin bazai taba barin ta haka ba.

To wai mema Najwa baiwar Allah tayi da har za'a salwantar da rayuwar ta.

Kai ya dafe, idon sa yayi jajir zuciyar sa tai zafi sai tafasa take.

Ahaka Mami ta dawo ta same shi. Tare suke Talle da Bara'atu har da Baba.
Duk sai da suka tausayawa Najwa. Kowa Addu'a yake Allah tashi kafadun ta.

Suna bawa Najib hakuri kan ya karbi kaddarar da Allah ya saukar masa.

Su Talle kamar suyi musu kuka, dan Najwa ba sawa ba cire wa koda suka zo gidan ta anan suka kara tabbatar da Najib yayi dacen mata.

Komai ta debo su, komai ta gano su zata bawa me zasu ce da Najwa in ba addu'a ba.

NAJWA Complete ✔Where stories live. Discover now