127

630 61 0
                                    

*NAJWA*

🌐  *HAJOW*  🌐

*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻

By *MARYAM  S  INDABAWA*
*MANS*

DEDICATED TO *RASHIDA A KARDAM*
*AUNTY RASH*

*ALLAH YA SAKA MIKI DA GIDAN ALJANNA.*
*AMEEN*

PAGE *127*

Soyayya tsakanin Najib da Najwa tayi nisa inda a tsakanin su ba wanda yake boyewa dan uwan sa halin da yake ciki.

Sosai Najwa ta saba da shi, son sa kuma ya shige ta sosai.

Abinda ya hana Najwa  soyayya tin farko shine.

Najwa bata iya soyayya ba. In ta tashi sa mutum a ran ta gab  aaa daya take son shi. Haka nan in bata so bata taba iya nuna masa tana son sa.

Wannan yasa take tsoron soyayya dan bata san wanda ke son ta tsakani da Allah ba.

Duk yadda Najib ya so, yaje Katsina hana shi tayi dan ya ce,
"Aikin sa da kula da Antyn fa."

Ba yadda ya iya, sai dai kullim cikin waya suke.

Momy kuwa har mamakin Najwa take, Dan ma Najwa akwai kunya bata taba yin waya a gaban ta.

Mami kan ta, tasan da batun Najib haka shima yasan ta dan suna gaisawa a waya.

Batun Sumaiyya kuwa yayi gaba dan in har ba ita take bukatar sa ba bata sauraron sa.

Shi kuwa ba ruwan sa duk nauyin ta dake kansa yana sauke mata.

Dan kullum Mami da Dady cikin masa fadan rike iyali yake.

Wannan yasa ko zai mata wani sai ya fasa.

Cikin ikon Allah su Najwa an koma makaranta, Sun koma second semester level three.

Satin da suka koma kuwa ya dira a katsina ba tare da ya fada mata ba.

Dan ya kasa jure rashin ganin ta.
Da yamma sun fito daga lectures sa kawai ganin sa sukai.

Mamaki dauke a fuskar su suke kallon sa.

Zahra kuwa sai cewa, tayi,
"Daman kin san da zuwan sa ne?"

"Ina fa?"
Suka karasa gun sa.

Har kasa suka durkusa suma gaida shi.

Amsawa yayi yana me kafe Najwa da idanu.

Dan ta kara kyau ta kara haske. Da ido tai masa alama da Zahra.

Murmushi yayi, ya ce,
"Zahra me kike bawa Baby na ta kara kyau haka."

Dariya Zahra tayi, ta ce,
"Ai ta dan rame ma dan kaji."

"Dan Allah fa. Gaskiya ne Allah yayiwa Dady da Momy albarka da kula min da Baby na da suke "

Dariya Zahra tayi, ta ce,
"Ameen!"

"Tashi mu koma can."
Najwa ta fada tana kallon sa.

Kallon ta yayi shima, wannan yasa tayi kasa da kai da sauri.

Gaba tayi suka biyo bayan ta. Zama sukai Zahra, tayi hostel.

Kallon ta yayi, ya ce,
"Baby na kasa jurewa sauka ta kenann."

Ido ta zare, ta ce,
"Sannu amman baka huta ba. Kaci abinci ba."

"Najwa ganin ki shine gaba da su. Na ganki na ji dadi sosai."

Murmushi tayi, ta ce,
"Sannu to, ya gajiya."

"Gajiya ta ganki ta gudu."
"Da gaske."

"Eh man. Sannu toh. Yau naga me maka tausa, ka baro Antyna a can."

NAJWA Complete ✔Opowieści tętniące życiem. Odkryj je teraz