71-75

768 69 1
                                    

Maryam S Indabawa😍😘: *NAJWA*


*BY MARYAM S INDABAWA*
*MANS*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da juriya Online writers*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻

DEDICATED TO *RASHIDA ABDULLAHI KARDAM*
*AUNTY RASH*

PAGE *71-75*

Mami ta ce,
" *Najwa* mane dalili nayin tsarki."

"Shima Malam min yace, dalilin tsarki dan ingantuwar Sallah shine,
Manzon Allah (SAW) Yace, "Sallah bata karbowa ba tare da anyi tsarki ba."  Musulimu da turmizu da ibn maja suka rawaito shi.

Wata fadar Annabin ma, yace, "Mabudin Sallah shine tsarki. Abu dawud, turmuzi su suka rawaito su.

Manzo Allah na kuma cewa, "Tsarki yanki ne na imani, kuma sharadi ne na cikar sallah." Musulimu ne ya rawaito.

"Na'am! To wanda ya kiyaye tsarki yana da falala."
"Eh yana da falala domin yana daga cikin wadan da Allah yake so."

Allah madaukakin sarki yana cewa,
Lallai Allah na son masu tuba, kuma yana son masu tsarki."

"Masha Allahu!"
Dady ya fada dan duk tambayoyin da Mami ke yi mata na tsaye yana ji.

Lokacin Hamma Salim ya sauko, kallon su yayi. Ya ce,
"Mami nifa yunwa nake ji."

Mami ta Ce,
"To ai mu ku muke jira ko?"

Suka nufi wajen cin abincin nasu. Tuwon shikafa Mami tayi miyar agushi da taji naman kasuwa sai kamshi ke tashi.

A katon faranti ta saka musu tuwon sannan ta zuba miyar a wani tangaran me zurfi.

Hannu suka wanke sannan sukayi Bismillah suka  fara cin abincin gaba dayan su a mazubi daya.

Abin gwanin sha'awa. Suna gamawa *Najwa* ta kwashe kayan takai kitchen.

Falo ta dawo ta zauna suna hira. Karfe tara duk suka haye sama kowa yayi dakin sa.

*Najwa* ce ta cirewa Basma kaya, tasa mata kayan bacci sannan tasa tayo alwala.

Basma ta ce,
"Adda wai saboda me muke yin alwala kafin mu kwanta."
Murmushi *Najwah* tayi.

"Saboda kariya daga shaidanu, sannan alwala tana kan kare zunubai. Kankare zunibai shine kamar kin taba abinda Allah ya hana to duk lokacin da kike yin alwala zununin da kika kwasa wajen taba wa, in dai kika wanke hanu a lokacin alwala kina wanke zunubin da kika kwasa  shi. Haka nan baki. In kinyo Abinda Allah ya hana in kinje kurkure shi to kina wake zunuban da ya dauka. 

To haka yake har ki gama alwala kina wanke zunuban da kika kwasa ne. Kinga ko dan haka ai yana da kyau muna alwala me kyau sannan kuma a koda yaushe ko?"

"Eh Adda!"
"Sannan akwai lokacin da Manzon Allah (SWA) yake cewa sahaban sa,
"Shin in fada muku wani abu. Wanda in har kayi shi Zaka samu lada sannan kuma kan karar zunibi ne."
Suka amsa da eh suna son sani.
sai ya ce,
"Duk wanda ya aikata alawala a lokacin da rai bata so, to tabbasa Allah zai yafe masa zunuban sa koda sukai kumfar kogi ne."
Kinga Alwala kam abar rikewa ce."

"Adda mene a lokacin da rai bata so."

*Najwa* tayi murmushi ta ce,
"Kamar da sanyi in ana muku muku to kuma kayi alwala. To wannan irin wadan nan  lokaci sune zakayi abinda rai bata so."

Kai Basma ta ke gyadawa.
"Kin gane."

"Eh na gane Adda."
"To kwanta da hannun dama."

"Adda shima dan me in zamu kwanta kike sani kwanciya da dama."
"Saboda Manzon Allah ko me zaiyi da dama yake, shaidan la'ananen Allah ne ke yin abu da hagu, kuma duk wanda yayi abu da hagu da gangan to Allah yayi hani da haka. Dan haka akwai hadinsin da Annabi yake cewa, in zamuci abu muci da dama haka nan in zamu sha ruwa shima musha da dama.

NAJWA Complete ✔Where stories live. Discover now