126

592 61 0
                                    

*NAJWA*

🌐  *HAJOW*  🌐

*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻

By *MARYAM  S  INDABAWA*
*MANS*

DEDICATED TO *RASHIDA A KARDAM*
*AUNTY RASH*

*ALLAH YA SAKA MIKI DA GIDAN ALJANNA.*
*AMEEN*

PAGE *126*

Sai da yai wanka yai sallah sannan ya kira Najwa.

Dagawa tayi cikin sallama da murya me dadi.

Amsawa yayi yana saukar da ajiyar zuciya.

"Hamma kaje lafiya?"
Sunan da ta kira shi dashi ne ya tuno masa da Najwa kanwar sa.

Murmushi yayi, ya ce,
"Lafiya lou Alhamdulilah ya kuka je gida kuma."

"Lafiya lou wallahi. Amman dai kaci abinci ko?"

Murmushin jin dadi yayi na kular da take dashi.
"Ban ci ba yanzu dai. Zanje madam ta bani."

Shiru tayi, a ranta kuma ta ce,
"Madam kuma ba Mama ba."

A fili kuwa murmushi tayi, ta ce,
"Ka gaishe min da ita."

Mamaki amsar ta, da ta bashi yayi, ya ce,
"Bakya kishi nane?"

Murnushi tayi, ta ce,
"Kishin ka shine naso abinda kake so. Ko so kake na tada maka da hankali."

Kai ya jinjina, a ransa ya ce,
"Alhamdulilah wannan ita ce matar aure ta rufin asiri."

"Haka ne Najwa in na dawo mayi magana."
"To shikenan sai anjima ka gaida su Mami da kowa."

"Zasu ji insha Allahu."
Mikewa yayi ya fita falo ransa cike da farin ciki.

Mami ya sama zaune a falo.

Gefen ta ya zauna ya ce,
"Mami Najwa na gaishe ki."

"Ina amsawa a ina ka ganta."
Murmushi yayi, ya ce,

"Mami yarinyar da nace miki na gani."
Kai ta girgiza ta ce,

"Najib wai aure kake son ka kara."
Murmushi yayi ya ce,

"Mami kin san dai Najwa na fara so kuma har yau tana raina."

"Haka ne Najib nima ina son ta tinda kana sonta. Kuma tin ban ganta ba naji sonta ya shige ni. Allah yasa albarka a ciki."

"Ameen Mami na."
Ya rumgumeta yana jijiga ta.

Su Talle ne suka shigo, Talle ta ce,
"Haba Yaya sakar mana Mamin mu kar ka balla mana ita."

Harara ta yayi ya ce,
"Zo kuji labari me dadi."

Talle uwar yan son labari ta karaso wajen da sauri, ta  ce,
"Bani mu sha."

Kai ya dungure mata ya mike ya ce,
"Na ki din."

"Dan Allah Yaya!"
"To Najwa na gaishe ku."

"Yaya Yaushe kaga Najwan?"
"Ke ba wannan Najwan ba."

Dariya tayi, ta ce,
"Wacce toh?"

"Matar da zan aura."
"Dan Allah fa?"

Ta fada da karfi. Bangaren sa yayi yana cewa,
"Tambayi Mami kisha labari."

Kallon Mami tayi, ta ce,
"Wai Mami yaushe Yaya Najib ya fara soyayya?"

Dariya mami tayi ta basu labarin haduwar sa da Najwa tin daga farko har haduwar da sukayi yanxu.

NAJWA Complete ✔जहाँ कहानियाँ रहती हैं। अभी खोजें