"Najwa lafiya naji muryar ki haka ."
"Lafiya lou baccin da na tashi ne."

Yaji tane kawai, ba dan ya yadda ba. sallah ta tashi tayi, tana kan sallaya har karfe bakwai.

Da kyar ta tashi tai gyara bangaren. Dankali ta soyawa Najib sai farfesun da tayi jiya ta dumama masa.

Motar sa takai, hade da snacks din da yace ta ajiye masa.

Ruwan zafi ta shiga ta gasa jikin sa dashi. Tana fitowa tai shirya cikin wata farar atamfa me adon baki.

Riga da siket ne, sawa tayi, ba tare da tayiwa jikin ta komai ba ta koma kan gado ta kwanta.

Najib na shigowa bangaren Kamshi ya doki hancin sa. Kitchen ya duba yaga bata nan.

Sama ya hau, ba kowa a falo, dakin baccin ta ya shiga ya ganta kwance akan gado.

Karasawa yayi, ya dago ta, tana ganin sa ta mike, ta gaisar dashi.

Amsawa yayi yana mata kallon tuhuma.
"Najwa lafiya kike kuwa?"

"Hamma lafiya nake, me ka gani na gajine kawai."
"Sannu kin gaji ko? Bari zan na tayaki, kinji."
Ido ta lumshe kawai.

"Me kike bukata?"
Kai ta girgiza masa ta ce,
"Bana bukatar komai sai dai ka kular mana da kan ka. Allah bada sa'a Allah kai ka ya dawo dakai lafiya."

"Ameen! Baby na, na gode."
Ya mike, mikewa itama tayi, kallon ta yayi, ya ce,
"A'ah ki zauna."

"Nidai A'ah tafiyar ka kawai zan gani."
Murmushi yayi, ya ce,

"Muje toh!"
Hannun su sakale da na juna suka fito.

Suna fitowa yaga Sumaiyya a compound din su.

Duk da daga bakin kofar dakin ta, ta tsaya sai da taga a yadda suka shigo.

Dariyar mugunta tayi, ta karasa gun Najib da yake dagawa Najwa hannu, kamo shi tayi tana kwanciyya a jikin sa.

Mamaki ya tsaya yi, jansa take amman duk hankalin sa baya jikin sa.

A jikin mota ta jingina shi, ta wani danna masa kirjin ta.

Bakin sa ta fara lallba dan masa kiss da sauri Najwa ta shige ciki.

Zuciyar ta na bugawa, lallai Najib ita zai wa haka a gaban ta ai sa bari in sun kebe.

Tsaki tayi tai sama, ta kwanta, bacci ne ya dauke ta.

Karfe daya ta tashi, alwala tayi tai sallah.

Ba abinda taci, dan haka jikin ta duk ba karfi, ga abinda Sumaiyya tai a gaban ta, shi kuma ya biye mata.

Koda yake ai matar sa ce, Mtsxxx

Tsaki ta kuma yi, yau ko text batai masa ba bare waya.

Wayar ma ta kashe gaba daya. Najib kuwa yana can yana ta zumudi dan yau da dare Najwa zata amshi girki.

Najib na shiga mota yaga basket din Najwa a ciki,
"Allah sarki My Naj, Allah miki albarka."

A office da kayan ciki yai break haka ma da rana da su yayi lunch.
Ya nemeta amman wayar a kashe.

Duk kiran wayar da yai mata wayar a kashe yana mamakin me yasa wayar ta take a kashe bayan yasan ba rashin charge bane.

Waya ya kira me gadi akan ya duba yaga Najwa na nan lafiya.

Mai gadi yaje ya tabbatar ya shaida masa. Murmushi yayi ya ce,
"Najwa yau rigima ake ji kenan."

Ita kuwa tana tashi ta fara gyara sai kace wacce ta dade bata gyara gidan ba.

Ko ina sai da ta kal kaleshi, ta goge komai kyelli yake.

NAJWA Complete ✔Onde histórias criam vida. Descubra agora