"Ina zuwa.!"
Ta dafa Najwa ta mikee.

Karasawa wajen tayi da murmushi akan fuskar ta.

Shi murmushin yake,
"Naga alamar an fara yin nasara ko?"

Murmushi tayi, ta ce,
"Sosai ma!"

"Masha Allah! Nagode!"
"Ba komai."

Kasa kasa yayi da muryar sa ya ce,
"Zan iya gani ta."

Kai ta girgiza masa. Ta ce,
"Ka ganta can."

Ta nuno masa ita da yake ta juya musu baya.
"Amman yanzu baza ta yadda ku hadu ba sai dai nan da kwana biyu. Ga number ta zan baka ka karasa sauran kafin ku hadu."

Murmushi yayi ya ce,
"Nagode."

Wayar sa ya dauki ya amshi Number Zahra da ta Najwa.

Sun jima Zahra na fada masa halaiyar Najwa wanda duk suka dada nasa sin ta da kaunar ta.

Ba abibda ya fado masa sai Summy wacce ba abibda ta iya bare ladabi da biyayya.

Abinda ya dade yana kwadayi sai gashi Allah ya jarabace shi da Sumaiyya.

Ya godewa Allah da ya jure zama da ita. Gashi Nan Allah yaso shi da rahama zai samu wacce yake da burin da kwadayin aura.

Sai gab da magariba ya tafi yana me kara godiya ga Zahra.

Wajen Najwa tayi suka koma daki duk jikin ta a sanyeye.

Zahara ce ke dada mata kwarin gwiwa na yabon halaiyar sa da dabi'un sa.

Da haka har Najwa ta fara samun nutsuwa da shi.

Shi kuwa tib da ya tafi kasa tsaye bare zaune yau gashi ga Najwa.

Ranar kwanan yayi yana sallah. Da asuba kuwa ya kira Khaleel ya fada masa. Haka ma Mami itama da asuba ya kira ta ya shaida mata.

Mami shiru tayi, tana tunanin har yaushe yayi da yake son kara wani auren.

Auren da befi shekara da watanni ba. Haka shima Khaleel ya ke sakawa a cikin ransa.

Da asuba taan tashi, yaji wayar ta na kara dubawa tayi.

Sakon ne wanda aka turo guda biyu dayan tin wajen karge hudun dare ne.

Sako ne akan zallah kaunar da ake mata ta jima tana juta kalaman sannan ta duba dayan da ya ce,

"Ta tashi tayi sallah. Lokacin karfe biyu da rabi."
Ta rasa abinda ya hau kanta har ta kasa tashi yin sallahr da ta saba.

Wani sakon ne ya shigi yana fadin ta tashi tayi sallahar asua.

Mikewa tayi da sauri. Taan tashin Zahra. Bandaki ta shiga ta yi wanka sannan ta tada sallah.

Tana idar wa ta hada musu abin kara da exam din safe ce dasu.

Suna gamawa suka shirya suka wuce hall din exam.

Karfe sha biyu suka fito a Exam wannan yasa suka shige library anyin karatu.

Acan ma sai da taga sakonnin sa har guda biyu dana barka da safiya dana addu'a Allah basu sa'ar jarbawa.

Murmushi tayi dan addu'ar ta mata.

Be kira ta ba amman dai a ranar ya mata text yafi goma.

Ya kira Zahra yaki ya Najwa take sannan ya ce me suke bukata.

Sam Zahra ta ce basa bukatar komai.

Duk yadda yayi ya kawo musu abu kin yadda tayi.

Lokacin da ya dauka ya koma aiki yayi amman sam yace shi sai yasamu haduwa da Najwa zai koma.

Gobe zasu gama exam din su dan haka, Zahra ta d ya kamata yaxo yau su hadu da Najwa.

Da yake basuyi paper ba yau yasa tin safe suka gama da karatun jarabawar gobe.

Kwallaiya take tsarawa Najwa dake fitowa daga bandaki daure da towel ta tsaya kallon ta.
ta ce,

"Ina kuma zuwa haka? Ko Mustapha ne zai zo?"

Murmushi Zahra tayi, ta ce,
"Kamar kin sani kuma zamu fita yi sauri ki shirya."

Baku ta tabe ta goge jikinta ta shafa mai.

Wani material suka dauka baki da ja, wanda akai musu dinkin doguwar riga me AShape.

Ba karamin kyau dinkin yayi ba. Ita suka saka sai dankunne baki da sarka da abin hannu.

Jajajyen mayafi da takalmi Zahra ta dauko mu.




*INDABAWA*

NAJWA Complete ✔Where stories live. Discover now