PAGE__57

194 7 1
                                    

_Page 57_

*TUKUICIN SO💞*

*NA*

*BILLY S FARI💎*

Saida ya tsaya kan hanya ya yi mata sayayyar kayan maƙulashe masu tarin yawa sannan ya ɗauki hanyar zuwa gida da ita yana faɗin,

"Madam wai ya akayi yau baki je da motar ki ba"

"Mota ta ko kuma ta Abba"

"To ai ni ke nasani da ita ba Abba ba"

"Duk da ni kasani da ita, ba yawa bace tasa ce kuma ya amshi abussa"

Da wani irin shock ya juyo yana kallonta cike da mamakin jin abunda ta faɗa kafin yace,

"Kina nufin mashin kika hawo ko napep?"

"Yeah, mashin na hawo" wani irin wawan burki ya taka ALLAH ya tsare babu kowa a gabansa ya juyo yana kallon ta,

"Janan mashin fa kika ce?, Kin san yanda na tsani naga macce akan mashin kuwa?"

"Sorry hubby ai lalura ce, kuma ai kamawa tayi shiyasa"

"To meya hana ki hau napep?"

"Ban samu ba gaskiya, ga time ya yi shiyasa na hau"

"To gaskiya daga yau karki sake hawa mashin bana so, thank God kin gama school ɗin kuma kin kusa zama mallakina, ba don haka ba duk ƙaddara tasa kika sake hawa to wlh sai na kulle mai mashin ɗin" ya ƙare zancen in a serious talk tare da tada motar suka ci gaba da tafiya tana hango tsantsar kishi daga cikin idanuwan sa,

"Am sorry hubbyn ruh hakan bazata sake faruwa ba, na tabbatar maka da hakan"

Ba tare daya kalle taba ya ce,

"Better, if not zaki ja nayi ta kulle mazajen mutane ta yanda ko sun ganki a kan hanya baza suyi marmarin ɗaukar ki ba" ƴar dariya ta yi haɗe da cewa,

"In sha ALLAH hakan ma baza ta faru ba, an dena daga yau"

"Prayerd so" ya faɗa yana ɗan sakin fuska tare da juyowa ya kalleta ta lumshe idanuwa ta saukar akansa, murmushi ya saki haɗe da cigaba da riƙon ba tare daya sake cewa komai ba, sun jima a haka kafin ta ɗan muskuta ta gyara zaman mayafin ta tana jinginar da kanta a jikin glass ɗin motar dake gefenta, har lokacin shi take kallo yanda yake driven cike da gwanewa,

"Thank you so much fore everything hubbyn ruh, bansan dame zan biya ka tarin soyayyar da kake yi mani ba domin duk abunda zan baka ko zanyi bazai iya biyan ta ba"

"Kike gani?, Ai ni tun tuni kin biya ni tunda kika amsa tayin soyayya ta, tukuici kaɗai ne ya rage ki ƙara mani dashi, shi kuma na barshi har sai munyi aure"

"ALLAH ya nuna mana"

"Amin ya rabbi"

"Amm.. sorry to ask you, ɗazu kace har lefe su Baffa sun wuce dashi, yanzu kuma ga wani ka nuna mani, hakan na nufin lefe biyu kenan kayi..." Tun kafin ta rufe baki ya kwashe da dariya tunowa da yanda kayan suke da kuma irin dariyar da Jabir ya yi ɗazu, girgiza kai ya yi haɗe da cewa,

"Sorry Janan, ki ɗauka kayan da su Baffa suka kai tsaraba ce dana yo maki daga ƙauye bawai lefe ba, kaya ne da ƴan uwana suka haɗa mani daga ƙauye in ƙara a lefe na a matsayin tasu gudummawar, shiyasa nayi amfani dasu a matsayina na mm mai dabino kamar yanda suka sani na kai maki su a matsayin lefen ki, kuma ina fatar zaki karɓe su hannu biyu" ya ƙare zancen yana dariya,

Dariyar itama ta shiga yi duk da bata ga yanda kayan suke ba, sai da tayi mai isar ta kamar yanda yake yi shima don ita dariyar tasa ma ke ƙara sakata yin wata dariyar sannan ta ɗago kai haɗe da cewa,

TUKUICIN SOWhere stories live. Discover now