💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Dedicated to
HAUWA A USMAN
JIDDARH
Page 99
'Cikin wannan halin datake ciki deeni ya km shigowa dakin fasukarsa dauke da wani irin maganadisun murmushi .ta koina ka kalleshi kasan yana 'cikin tsantsar farinciki da murna samun wayan nan kyawawan bbys din masu matukar kyawun da daukar hankali .
Ahankali yakarasa inda take zaune rungume da ya'yanta duka .
ya tsura mata rikitattun idanunshi yana kallonta da jin Wani irin mugun sonta da yaran yana tasoma masa .
Yanayin daya ganta ciki yasashi shan jinin jikinshi .
zama yayi kusa daita sosai har cinyoyinsu Na gugar juna ya amshi ta mace Daga hannuta ya daurata saman cinyarsa yana kallonta yana kallon fuskarta nablah dayaga gabadaya ta canza ta dawo wata iri . muryarsa a sanyaye ya Kira sunanta nabeelah ....bata amsa masa ba sai ma juyo da tayi inda yake zaune tayi masa kallon second 2 kana ta dauke idanunta Daga kanshi.
ta maidasu kan yaranta dake cinyarta .
,sautin muryarsa taji a matukar sanyaye fiyye da farkon shigowarsa dakin .. nablah kinga kyautar da Allah Yayi mana ko?
Adakike ta amsa masa da uhmmmm . gsky kin iya haihuwa.
arayuwata bantaba ganin macce data iya haihuwa kmr ki ba .
Gsky kinyi kokari sosai . nan ma tayi masa banza ta sharesa gabadaya ma taki cewa dashi komai .
yanzu mekike bukata akawo miki ?
muryarta can kasa kasa tace babu tare da kamo lips dinta Na kasa tana cizawa ahankali ahankali tana Dan jijjiga kafarta daya akasa .
Gabadaya deeni ya rude yarasa abinda ke masa dadi tunda ta haihu yarasa gane kanta sai wani shashsharesa take tana basar dashi da ciccin magani wanda yarasa dalilinta nayin hk . runtse rikitattun idanunshi Yayi sosai .
ciki Mutuwar jiki sakamakon tuno da kyawawan bbys dinsu data haifar masa masu tsananin kamadashi km yake tare dasu ahalin yanzu.
To me zai dameshi da duk abinda zatayi arayuwa tagama masa komai tunda tabashi abinda yafi so da kauna a rayuwarsa ta duniya . sumbar bby girl din yayi yana jin wata irin natsuwa ta daban tana ratsa kowane shashi Na gangar jikinshi sosai yake son yaransa Amman yafi jin kaunar mace fiyye da sauran acikin zuciyarsa .
Jikinasa cike da rauni soyayyarta yakamo tafin hannuta 'cikin nashi yasoma murzawa ahankali ahankali 'hade da shaukin kaunarta yace meke damunki nablah naga duk kinyi wani iri hk ?
Ki sanar da deeni abinda ke damunki banason ganinki 'cikin wannan damuwa da tashin hankalin please ...
yanzu kin zama wata bangare Na rayuwata da farincikina gabadaya sbd wannan kyawawan bbys din dakika bani ..
Kimin abinda wata matar takasa jura ta min arayuwa .
Kin bani kyautarsu alokacin danafi bukata . akan wayan nan yaran bbu abinda bazan iya miki Shi ba , matukar Bai shafi addanina ba .
ban ji dadin yadda naganki ba yanzu.
idan akwai wani abu dake damun zuciyarki ki fito ki sanar min.
ni km nayi miki alkwarin zan yi miki maganinsa kowani iri ne .. yakarasa fadar hk yana matse laulausar tafin hannunta 'cikin nashi yana jin yadda sonta ke fizgar zuciyarsa gareta ..
So take tayi mgn Amman maganar taki fitowa sakamakon wani yanayi data tsinci kanta ciki ,ita fa bbu abinda ke damunta s halin yanzu wanda ya wuce son rabata da ya'ya za'a yi.
ta lumshe shanyayyun idanunta kana ta budesu ahankali ta zubesu 'cikin nasa still takasa tabuka komai shima lumshe rikitattun idanunshi Yayi sannan yace Ok kingama ganin yaran zan maidasu kasa sbd masu zuwa ganin bby ..
take zuciyarta ta buga da matsanancin karfi har sai data taji zubowar gudan jini Daga kasanta . afrigice ta zare hannuta 'cikin nashi tana kallonsa a tsorace bakinta da alamun son yin mgn .
kanshi ya girgiza mata yana kokarin mikewa tsaye .
Muryarta cike da inn inna ta fizgo mgn da kyar tace nifa.. nifa ..ban bada ya' yana.
what ? Bai San sanda yakoma ya zauna ba .yana kallonta da matukar mamaki .
Wallahi wallahi deeni idan duniya zata taru akaina idan sama da kasa zata hade idan za'a yi ruwan jini deeni bazan iya bada ya'ya nan ba.
kai ni daya Daga cikinsu ma bazan iya bayarwa ba ballanantana duka .
deeni koda duniya zata kini ciki kuwa har da mahaifana dakai deeni koda zan dawo kwanan akan bola Ina tsince tsince in ciyar da kaina da ya'ya Na ,bazan iya bada ya'yan nan ba wlh. duk da Allah yasani bansan waye mahaifinsu ba Amman Ina ji ajikina mahaifinsu ba wulakantacce mutun bane duba Ga yanayin ya'ya.
take gaban deeni ya fadi rassss rassss rassss yashiga bugawa da karfi karfi .zuciyarsa tashiga tsalle da kururuwa neman dauki da agaji .
muryarta ahankali 'cikin sanyi jiki tacigaba da mgn tunda Na kalli fuskar ya'yan nan narasa meyasa naji Ina mugun kaunarsa wanda bansan dalili ba narasa meyasa tun sanda Na daura idanuna akansu kawai naji bazan iya rabuwa dasu ba .
takarasa mgnr tana fashe masa da wani irin matsanancin kuka me cin rai da Daga hankalin .
Jikinta Na matsanancin rawa ta kwantar da yaran daya byn daya akan gadon.
da kyar ta sauko Daga kan gadon datake ta zube masa a gabansa ta dinga kuka Dan Allah deeni karku rabani da ya'yana Ina son su ko zan rasa raina bazan iya rayuwa bbu su ba.
Wallahi bazan iya rabuwa da yarana ba aduk yanayin da suke Wallahi azim bazan iya rayuwa bbu su ba ni Ina son su a Haka .
kuka take sosai tana rokonsa akan kada surabata da yayanta .
Gabadaya jikin deeni yayi Wani irin mugun tsayi km ilahirin jikinshi suka mace murus yarasa abinda ke masa dadi a zuciyarsa .
Ga koshi Ga kwana yunwa.
hankalinsa ya Kai kololuwar gurin tashi gabadaya yarasa abinda yakamata Yayi ahalin dayake ciki .
kukan farinciki zai yi ko haushinta zai ji Na sabon salon iskanci data tsiro ... sai kallon bbys din yake yana kallonta tsugunne agabansa tana risgar kuka tana rokonsa .
shima ajiye bby' girl din dake hannunshi yayi .
ya tsura mata rikitattun idanunshi da kyau yana cigaba da kallonta hade da nazarinta wato dai da gaske mutuwar son yaran take kmr yadda shima yake matsanancin son su .
duk Shi a tunaninsa yafita son su da bukartasu arayuwarsa ..
a zuciyarsa yaji wani irin matsanancin sanyi ya ratsashi tundaga tafin kafafunshi zuwa kwanyarsa , kennan idan yace zai isar da sakon zuciyarsa gareta bazai Sha wata wahalar shawo kanta ba adalilin wayan nan yaran ..
take km burin mahaifiyarsa ya fado masa .
yaya zaiyi da ummi wace oready tagama gaya duniya da shelar cewa zeenat ta haihu ?
..yaya zata ji idan tasamu wannan mummunar labarin ?
Kuka take Sosai ta rike kafafunshi gam deeni kayi hakuri nasan ban kyauta ba akan abinda nayi Amman Ina son ya'yana duk da kasancewarsu shegu wlh ba zan iya kyauta dasu ba kmr yadda nayi maka.. shiiiiii Karki kara kiran ya'ya Na da she.. shegu ni..Ni..ne ...sai km yayi shr ya datse harshensa da hakorinsa gam jikinsa Na wani irin matsanancin rawa idanunta dake cike da ruwan hawaye ta xuba masa tana kallon bakinsa .. zuciyarsa gabadaya gaskiya take son fada mata Dan ta daina danganta ya' yansa da kalmar shegu Amman yana jin matsanancin tsoron tashin hankali dazata shiga fiyye da wanda take ciki ahalin yanzu.. Shi dai yasan xuwa yanzu ya Mika duk rayuwarsa gareta sbd kaunar dayake mata ita da yayanta ...
'Cikin wannan halin zeenat da ummi suka shigo dakin atare turus sukayi ganin nablah durkushe gaban deeni rike da kafafunsa tana risgar kuka da iyakacin karfinta .
Da sauri suka karasa garesu suna tmbyr deeni lafiya meke faruwa ?
'cikin rawar jiki nablah ta Mike tsaye ta nufi gurin ummi tana layi tana kuka muryarta cike da kuka tace Dan girma Allah ummi ku min rai wallahi bazan iya bada ya'yan nan ba kumin abun alkhari nasani km Na gode da karamcinku gareni Amman kada Ku rabani da ya'yana .....
A zubure zeenat ta dafe kirjinta tare da cewa what ke kina da hankali kuwa ?
Ke wace irin mahaukaciya ce yaza'a yi kice bazaki iya bada ya'yan ba .....
take nablah ta fuskanceta sosai a fusace tace gaki nan babbar mahaukacirya da batasan abinda takeyi ba da sanin ciwon Kanta ba.
ke kinsan zafin haihuwa ne?
ko kinsa zafi ya'ya ke kinsa wahalar dana Sha akan wayan nan ya'ya?
to nace bazan bayar ba km idan sama da kasa zata hade bazan bada ya'ya nan ba ke ni akan ya'yan nan banki duniya takini ba ciki km har da iyayena wallahi wallahi dana bada ya'yan nan gara narasa rayuwata gabadaya.
ke indai kika ga nabada ya'ya nan sai dai idan bana numfashi a doron kasa .
rassss rassss gaban ummi yayi wani irin matsanancin bugawa da karfi ..Hk ma deeni gabansa ya km bugawa zuciyarsa tacigaba da rawar datake tun kafin shigiwarsu ummi ..
Zeenat tace Wallahi wallahi baki isa ba nablah kinyi kadan km sai kin bada yaran nan tunda tun farko ke kika amince km kinyi alkawarin zaki bada su muryar zeenat Na rawa takarasa fadar hk .
Wani irin kallon tababbiya nablah tayi mata sannan muryarta Na rawa rawa tace to..to.. yanzu nafasa badasu sbd nima Ina son abuna dama can danayi kyautar su bansan zafinsu bane yanzu kuwa sai dai nabawa wasu labari .
Baki isa ba wallahi sai dai kuwa ki rasa ran naki dakike ikirarin rasawa akansu Amman kmr kin bada ya'ya kingama .. Ok zanga wanda ya isa dazai rabani da ya'yana ..
ke nifa nafiki zafin Kai da rashin mutunci akan yaran nan zan iya miki duk abinda yazo zuciyata inji cewa zeenat .
baki nablah ta saki tana kallon zeenat da mamakinta hakan yabawa zeenat damar cigaba da maimaita kalmar dole abasu yara tunda tun farko an rigada anshirya hk da surutai kala kala tayi kan baby's cike takama zata dauka nablah tayi kuka kura ta dire gabanta cike da maseefa tace ubanwa yabaki damar taba min yara ?
Ubanki da km uban Yayi miki ciki a gidan nan .
a fusace ummi tashiga tsakaninsu tana jan zeenat baya.
ummi ta dinga mamakin abinda nablah tayi duk da tasan Yar tatace da fadan rashin gsky Amman batayi tunani nablah zata iyawa zeenat rashin kunya da tsiwa Haka ba .
Ni zaki kawo danyen Kai da ranshi kunya ta fadi Haka tana nuna nablah da yatsan hannuta Dan girma Allah ummi ki matsa Na canzawa wannan Yar iskar yarinyar halitata dama Ina da ciki daita Ina takaici ta wlh.
kallon kasa da sama nablah ke bin zeenat dashi ahankali wanda ke nuna alamun bata isa ba .
Kina takaicina ai sai kixo ki kasheni ki huta banda mijinki daya nace akan zai taimakamin da tuni ban san inda dare Yayi min .
zeenat tayi sororo tabi deeni da wani irin kallo tana jiran taji yakarya mgnr yarinyar .
Amman taji Yayi shr yana binsu da idanu kawai .
my hrt ummi kuna jin fa abinda yar iskar yarinyar kecewa ko.
ummi tace munji ai zance nata duk shirme ne bakya ganin duk abinda take bata 'cikin haiyacinta tasoma jijjga zeenat din kiyi shiru mu yanzu bawannan shirme bane agabanmu yadda yara zasu zama naki shi kawai .kiyi shr ki natsu asan abin yi .
nablah najin Haka ta buga kafarta daya a kasa ta nufi gurin da bbys dinta suke kwance gadan gadan tasa wani irin mahaukatan kuka tana cewa wllahi tallahi ban bada ya'ya Na .
ya'yan guda uku ta rungumesu ajikinta tana sake sakin wani irin matsanancin kuka me ban tausayi da taba zuciyar ma aboci saurare ..
Tashin hankali wanda ba'a saka masa ranar zuwa .
zaune kawai deeni yake yana kallon sarautar Allah.
Yana mamakin daman zafin kan yarinyar nan yakai hk Shi Bai sani ba ....abu kmr a film yarinya tana kokarin birkice musu da dagula musu lissafi.
hatta ummi tsaye kawai take sake da baki tana kallon ikon Allah da yadda nablah ke nuna reaction dinta akan bby din da batasan taka maimain wanda yayi ma 'cikin su ba .
,to wannan idan km tasan ya'yan deeni ne km jikokinta me zai faru ? Tayi wa kanta tmbyr tana cigaba da kallon nablah rungume da yara tana kuka .
tamkar wata zautaucciya .
Gabadaya Daga deeni har ummi kasa tabuka komai suka yi sai idanu da suke bin nablah dashi ...
Wani irin tausayinta ne me gyaraye da tsansar soyayyarta ke sake huda kirjinsa da mamaye gangar jikinshi da zuciyarsa .
alahakikanin gaskiya Bai taba tunani yarinyar zata canza salo irin Haka ba.bai dauka zata so ya'yan da ta dinga hauka akan acire mata su ba .
Wani irin gumi ne me zafi ya shiga tsaftsafo masa ta koina ajikinshi yazama tamkar wani mutun mutumi a zaune yana kallon nablah kwakwume da bbys ajikinta duk tayi firi firi tafita haiyacinta .
Take zeenat ta dinga jin zuciyarta tamkar zata fashe ta tarwatse kan takaicin nablah.
ita kanta wani irin mugu mugun son bbys din ne yashiga ranta tun sanda suka zo duniya ta daura idanunta akansu taji sun shiga ranta.
duk da duk sanda ta kallesu gabanta Na tsananta faduwa akan tsananin kamanin da yaran keyi da mijinta.
Dan ko mahaukaci ya kalli yaran yasan kamarsu daya da deeni babu wani bambanci launi ko sura daidai da yatsun kafafun yaran dana hannusu irin na deeni ne sak .
bakinsu da hanci komai Nasu irin nasa ne .
sosai take taji wani irin mugun son yara Na sake ratsata har 'cikin zuciyarta tana jin bazata iya rayuwa bbu su ba ....
Amman Ga tashin hankali da uwarsu tazo mata dashi wanda take jin bazata iya jurawa ba .. Amman duk da Haka durkusawa wada ....
gabadayan ilahirin jikinta yayi mugun sanyi jikinta banda kirma bbu abinda yake tsabar tsoro da rudani .
Ga mamaki deeni da ummi har nablah.
suka Ga zeenat ta zube a gaban nablah tana kuka tare da rike kafafunta tana rokonta Dan girma Allah nablah ki rufa min asiri kada ki min Haka wannan ita kadai ce damata da zata min katanga tare da yi min shingi da kishiya arayuwa ta.
Dan girma Allah kibar min yaran wallahi nafiki bukatarsu zan kular miki dasu fiyye da tunaninki .
zan basu gatan duk duniyar nan .
zan kaunace su fiyye da ke kanki da kika kawo su duniya ..
Dan Allah kibar min su Karki fasa kyautar mana dasu kmr yadda kikace ummi Dan Allah kisa baki tabar min su .. my hrt kaima kayi shr kaki cewa komai please kuyi mata mgn kozataji nafita bukatarsu takarasa mgnr tana fashewa da wani irin matsanancin kuka.
kuka zeenat take tana rokon nablah akan tabar mata yaran ... ahankalin deeni ya Mike tsaye Daga zaune dayake yaje har gaban nablah ya mika mata hannunwansa duka alamun tabashi yaran Amman taki .
Yayi yayi tabashi yayan taki sai ma matsawa da tayi Daga kusa dashi tana jijiga yaran da zuwa yanzu hayaniyarsu tasoma tayar dasu .
da kyar deeni ya shawo kanta ta hanyar ce mata bbu inda zanje da yaran nan nablah zan kwantar dasu ne kawai ko bakiga yadda kika matsesu ba ajikinki ba kar wani abu yasamesu .
sannan ta Mika masa mace da Na namiji zuciyarta cike da tsoro da fargaba yaje ya kwantar dasu .
ya dawo ya amshi dayan ma ya kwantar dashi kusa da yan'uwasa kana ya janyo hannuta ciki sanyi jiki Ya zaunar daita akan gadonta ya tsura mata rikitattun idanunshi yana kare mata kallon tsanake .
sannan yasoma magana 'cikin sanyi rai da zuciya...
MMN SUDAIS CE