💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
*I really appreciate all my fans and all washers that called me when am sick thank God I recoved God bless all , and I pray for the people that are sick may Almighty Allah liet there wings up Ameen I so much loved you fans remain bless once again i appreciate all ur effort on me*🤝🏻🤝🏻🤝🏻
Page 75
A zafafe Ya qakaraso har zuwa inda take a durkushe sbd yanayin takaicin da yake ciki.
'dan bakaramin yamutsa masa tunaninsa tayi ba musamman lokacin daya daura idanushi akanta tsaye da kB.
ji yayi kansa nayi masa wani irin Sara tamka zai rabe gida biyu .
zuciyarsa kuwa zafi take masa tamkar zata kama da wuta.
Kuka take Sosai Na fitar hankali.
may taba zuciyar ma'abocin sauraro kallo daya zakayi mata kaji tausayinta ya tsargamaka km duk rashin imaninka idan kaga halin datake ciki wlh Dole ka tausayawa rayuwarta .
A halin da take ciki bata tunanin duk duniya akwai mutumin data tsana da kin gani ......sama da mutumin dake tsaye a gabanta ...
Kukanta da halin datake ciki ko ajikinsa "asalima kwata kwata bai damu ba.
km bai jin ajikinsa Hakan zai zama damuwarsa sai ma tarin haushinta da takaicinta dake daskare a kasan rashin .
gyara tsayuwarsa yayi sosai tare da rungume hannuwanshi duka a saman fadadden kirjinsa ya zuba mata rikitattun idanushi yana kallon yadda take kuka , kusan minti Goma ya dauka tsaye yana aikin kallonta batare da yace mata komai ba.
jin kukanta yaki tsayawa ne yasa zuciyarsa cunkushewa guri daya tasoma dugunzuma tamkar ana diga masa ruwan dalma .
Kafin ya ankare yaji
Ta sake kara sound din kukanta may tsanani cin rai da tsuma zuciyar ma'aboci sauraro tare da dagula lisafi .
Shr kawai yayi yana tunanin abinda yakamata Yayi gabadaya ilahirin jikinsa sun gama sagewa duk da sanyin AC dake aiki a parlour hakan Bai hana zufa keto masa ta koina ajikinshi, so yake yayi magana Amman km yakasa dan bazai iya yi ba, dan ko yace zaiyi mgnr muryarsa bazata fito ba dan hk Ya runtse rikitattun Idanunshi gam hade da Dan kamo lip's dinshi Na kasa yayita tsotsa ahankali yana jinta tana risgar kukanta dayaje jinsa har 'cikin ranshi .
baya kaunar ya bude idanunshi ya kalleta cikin yanayin halin datake ciki .
km bai jin zai iya furta mata daidai da kalma daya ce a yadda yake jin kansa
Dan hk yabarta tacigaba da kukanta wa tunaninsa idan ta gaji dan kanta zatayi shr amman Ina saima ji yayi ta kara sautin kukan sosai .
Ai take haushinta may gyaraye da tsansar takaicin abinda tayi masa Ya sake ya harzuka zuciyarsa .
bazato taji saukar rankwashi a tsakiyar kanta .
Da sauri tasa hannuta ta dafe gurin tare da sakin wata irin razananniyar kara Wanda ya farga da ummi dake zaune a part dinta .
idanunta suka sake kawo ruwan hawaye may dumi .. ya murde mata kunne da karfin gaske ta sake saki wata kara... tare da cewa wayyo Allahna .... Wayyo Allahna ...wlh Allah Ya isa ban yafe mak.....ai kafin takarasa taji Yasa bayan hannushi ya buge mata baki.
da sauri ta sanya hannyenta dukka akan bakin nata tana may zuba mishi shanyayun idanunta Wanda suke cike taf da ruwan hawaye .
Sannu ahankali ya bude idanunshi fesss suka sauka akan Kwakyawar fuskarta may cike da haiba yana mata wani irin kallo may tattare da tsansar tashin hankali . shiiiiiiiiiii kawai ya iya cewa.
ba shiri ta hadiye sauran kukanta Dan wani irin tsoronsa ne taji Ya caki tsakiyar zuciyarta.
yayinda gabadaya ta canza takoma wata kala daita abar tausayi Banda tsine masa da zaginsa bbu abinda take a kasan zuciyarta ...
daidai wannan lokaci ne
ummi da safeena suke saukowa daga upstairs sakamakon jin tashin sautin kukan yaki karewa km har zuwa time din DEENI na nan tsaye rungume da hannuwanshi .
Da sauri ummi takaraso Inda suke tana tmbyrsa lfy ?
ganin irin kukan da nablah keyi.
DEENI yayi shr kawai yaki cewa komai sai ma cigaba da kallon nablah da yake batare da ya amsa tmbyr da umminsa tayi masa ba .
Ahankali ummi ta dago nablah dake durkushe a kasa .
tana tmbyrta lfy nablah make faruwa ? Me yayi miki ? Hk ummi ta jera mata tmby .
shr kake jin nabla dan bbu bakin mgn sai ma kukan da take risga da iyakacin karfinta har da shesheka .
Ummi ta sake juyo inda deeni ke tsaye Wanda xuwa lokacin ya sake gyara tsayuwarsa tare da cire hannushi a saman fadadden kirjinsa ya mai dasu 'cikin aljihun wandonsa yana ciciza lips dinsa .
Deeni....ummi takira sunansa muryata a kausashe. Kasa amsawa yayi tsabar Haushi sai ma idanunshi daya dauke daga kan nablah ya maidasu gareta .
me yasame yarinyar mutane take kuka irin haka?
ko wani abu kayi mata ta jiho masa tmbyr a jere ..?
Kafin yace wani abu sai daya numfasa tukun sannan ya sauke ajiyar zuciya" tare da yatsina fuskashi" muryarsa a marairaice may cike da tsansar shagwaba kana yace Gata nan a gabanki first love ta fada miki abinda akama mata .
ummi ta bata rai sosai tana dubansa sannan tace bafa nason rashin mutunci deeni ....
Kafita idona Na rufe ...abinda kayiwa yarinyar mutane kawai nake son sani ba wanin rainin hankalinka daka sabawa yiwa mutane ba .
Shima hade rai yayi Sosai fiyye da dazu sannan yace haba first lov ya a gaban yarinyar zaki dinga yimin hk "salon kawai ta raina mutane byn nima hk naganta bansan abinda ya sameta ba.
yana gama fadar hk ya cire hannushi daya cikin aljihun wandonsa" yabar daya ciki tare da juyawa ahankali yasoma daga kyawawan kafafunshi yasoma takawa sannu ahankali 'cikin takun nan nasa may matukar daukar hankali , Ya nufi bedroom dinsa .. ummi tabi bayansa da kallon mamaki tana may tabe bakinta a ranta tace rainin km Na nawa...
Yana shiga bedroom dinsa yaje ya zauna 'bakin gado yana fidda numfashi ahankali ahankali tare da tunanin matakin dayaka mata ya dauka akan kb da ita kanta yarinya.
a dazu daya gansu ji yake tamkar numfashinsa zai fuzge ne daga gangar jikinsa sbd wani irin radadin azabar daya shigesa ...
Zuwa lokacin tuni safeena ta kamo hannu nablah dake kusa da ummi xuwa kan kujera tana tmbyrta abinda ya hadasu da bros dinta. yayinda ita km nablah taki cewa komai sai kuka da take .
Ahankali ummi takaraso kusa dasu ta zauna itama.
" tmbyr duniyar nan bbu irin Wanda ummi da safeena basuyi mata ba Amman Sam nablah taki cewa Ga abinda aka mata sai hawaye ne kawai ke fita daga idanunta ..
tun tana kuka a zahirance har ta dawo kukan zuci .. yadda taga ummi duk ta damu ne.
Yasa duk jikinta yayi tsanyi Sosai ta sausauta kukanta tare goge Hawayen idanunta .. jikinta a sanyaye ta bude bakinta Da kyar tamkar may koyon mgn takira sunnan ummi ...
ummi ta amsa tare da juyowa ahankali ta zuba mata idanun kawai tana kallonta hade da nazarinta ... sannan tace uhm nablah Ina sauraranki mekike son cewa ?
'cikin muryata may matukar sanyi da ban tausayi tace da Allah ummi Ina son zuwa gida naga mamana da sauran yan'uwana, takarasa fadar haka hawaye da yayi saura a idanunta yasamu nasarar silalowa kan kuncinta .
ummi tayi shr for the mean time tana cigaba da nazarinta sannan daga baya tace shine daman abinda Yasa ki kuka hk ?
Nablah ta girgirza kanta da sauri tana duban kasa.
to fada min meyye abinda yasaki kuka ? Ko km waccen babban kobon ne yayi miki wani abu?
muryata a raunane tace a,a ummi bbu komai fa Dan tasan koma ta fada mata , abinda yayi mata ba komai za'a yi masa ba ya rigada yacita bulus..
Shikennan amman zanso ki kara yin hakuri.
zaki je gida inshallahu Amman ki Dan bani lokaci kadan da kaina zan kaiki har gidan naku kinji .
kinga yanzu shirye shiryen zuwa India nakeyi tare da safeena zamu wuce har da Zeenat.
ke .. zaki cigaba da kula da al,amuran gidan .
Da zarar Na dawo duk da ba'a gidan nan zan sauka ba ,zan koma gidana zaki je gida kiga family dinki kinji .
gaban nabla yayi wani irin bugawa da sauri hankalinta yayi mugun tashi jin abinda ummi tace ta dago ahankali tare da zubawa ummi shanyayun idanunta kawai dan takara tabbatar da abinda taji tace .
Ahankali ta 'cikin hijab dinta tasa hannu ta dafe daidai saitin zuciyarta dake harbawa da sauri da sauri .
bata jin zata iya zama ita day ranta acikin tanbatsetsen gidan irin hk may cike da abubuwan ban tsoro "duk da tasan bada laraba za'a ba . amman ,hankalinta yayi mugun tashi .
Sake kafe ummi tayi da shanyayun idanunta tana kallonta da kyau yayinda sauran Hawayen idanunta suka cigaba silalowa . kadan ya rage zuciyarta batakarasa bugawa ba.
sbd rudanin da take ciki muryarta Na rawa tace Dan girman Allah ummi kiyi hakuri kibarni Na tafi tunda kuma tafiya zakuyi bazan iya zama Ni kadai raina acikin gidan nan ba wlh ni tsoro nake ji takarasa fadar hk wasu Hawayen nakarasa zubowa tare da hade hannuwata guri daya ta curesu may nuna alamun a tausaya mata .....
safeena dake zaune ta kamo tafin hannuta 'cikin nata tana murmushi cikin hadadden turancinta tace Kai nablah badai tsoro ba wlh.
kiyi hakuri kiyi zamanki kmr yadda ummi tace bbu abinda zai sameki inshallahu.
Ga laraba nan tare zaku zauna.
duk kinbi kin wani frigice daga jin za'a barki a gida.
nifa Na dade da gane wayonki so kike ki gudu wlh , safeena ta karasa fadar hk tana murmushi tare da duban saitin da ummi take ..
Murmushi ummi tayi kawai Dan tun ba yau ba itama tasan yarinyar ta gaji da zama dasu.
, tun ba'a je koina ba.
Amman tasan ba laifin yarinyar bane .. laifin mutane gidan dake frigitata ..
"Dan hk ummi tayi murmushinsu irin Na manya kana tace wai hk ne nablah kina son ki gudu daga 'cikin family dina?
take nablah ta sake rudewa a frigice take kallon ummi tana girgirza mata kanta . muryata a sarke tace wlh ummi ba hk nake nufi ba Ni dai tsoro kawai nakeji.
safeena ta Mike tsaye sbd wayarta data dauki kara sautin may dadi ta nufi dakin ummi.
tabar ummi da nabla zaune a gurin suna cigaba da zantawa.
Byn kmr minti shabiyar sai Ga DEENI ya sauko byn ya sauya kayan jikinshi zuwa wasu kananan kaya" masu shegen kyau da daukar hankali.
wando jeans ne three quarter da whit top wanda gaban riga akayiwa rubutu da ratsin baki kmr hk super man sai kamshi turare ke tashi ajikinshi.
ta koina ka kalleshi dole kaji yashiga ranka . idanushi kyam akan nablah dake zaune a gefen ummi .
Ya dan tabe bakinsa sannan ya samu guri ya zauna kan kujera dake facing din ta ummi tare da dan zamowa jikinshi kadan yana may yatsina fuskashi sannan muryarsa a sanyaye yakira sunan ummi ... first love ....
Ummi Ta bar abinda take ta dago tana dubansa ya kashe mata Idoshi daya kana yace mata am feeling hungry... ummi tace Allah ko? Ya daga mata cike da shagwaba Ok sai kabari matarka ta dawo tabaka abinci .
...haba first lov meyasa kike min hk ne yanzu ?
Ni wlh Gani nake ma gabadaya kin canzamin kin daina sona da ji dani kmr da .
km nasan shiga tsakaninmu akayi wlh amman nasan maganin abu yakarasa fadar hk yana sake tamke fuskarshi ...
ummi tayi murmushi ,ta nan km zaka bullo ?
Bbu wani ta nan zan bullo ai gsky Na fada.
Uhmmmm to yake son shiga tsakanin "da" da uwa ?
Mayun dake rayuwa damu acikin gidan nan ya dan dauke numfashi sannan yacigaba Allah first love kinsan dai sarai banason Amin kishiya. amman gabadaya sai wani kokarin kike ki hadani da wasu which,s bad ..
ummi tana jinsa har ya dasa aya amman Tayi masa banza tamkar bataji shi ba tacigaba da abinda take .
ahankali km a shagwabe yabar wancen zance yasoma yiwa ummi naci yunwa yake ji ..
Ummi tasan halin nacinsa km tun da yace yana son cin abinci tasan yuwan oready tagama cinye cikinsa .
Dan hk kawai tace nabla taimaka dan Allah ki shirya masa wani abu may sauki kinji diyata ko zai rabani da wannan nacin nasa ..
DEENI da idanushi ke kan umminsa Ya tsina fuska tare da cewa yanzu first lov wannan yarinyar ce zatayi min wani girki?
yarinyar da kwata kwata bata iya komai ba.
,Kai nifa banason cin jagwalgwalon abincinta wlh nablah ta dago shanyayun idanunta da niyar kalonsa sbd yadda taji tana sakin maganganu karaf idanunsu suka sarke cikin juna ya watsa mata wani matsiyacin kallo wanda yasa ta dauke idanunta da sauri yayinda zuciyarta tashiga dokawa .
wannan km son ranka ka fada kawai dan kaji dadin bakinka amman mgnr jagwalgwalon abinci take dafawa karya ne wannan domin bbu Inda girki nablah bazai shiga ba a duk fadin Africa.
cin jagwalgwalon abinci km sai dai kar a km domin yanzu kasoma .
dan Allah rabudashi kinji nabla tashi maza kije ki samar masa wani abu me sauki .
Nablah ta Mike tsaye amman gabadaya ilahirin jikinta bbu Inda baiyi sanyi ba ..ita kanta ba,a son ranta take masa wasu abubuwan ba darajar ummi kawai yake ci agurinta .
A sanyaye ta nufi kitchen "ahankali yabi bayanta da kallo yana tabe baki tunda daman ta gababshi zata wuce km shi yakan so yaga yadda take tafiya kmr an tsamota 'cikin ruwan tsanyi .
"yana juyowa idanushi karaf 'cikin Na umminsa sukayi four eyes .. yayi saurin dauke idanunshi . waskewa yayi tare da sosa byn keyarsa alamun kunya sai dai ya sake hade ran nan nashi tamkar yana filln daga ..uhm kawai ummi tayi tana murmushi da girgirza Kai..
nablah ta dade tsaye a kitchen tana saka da warwara abinda zata daura mishi may sauki wanda bazai dauki lokaci ba.
zuwa can ta yanke shawarar dafa masa jollouf din cuscus .
ta hada masa haddadiyar jollouf din cuscus Wanda ta wadatu da kayan hadi carrot green beans da piece koda da hanta a mamadin nama kamshin Curry da tyme ne kadai ke tashi ta barwa laraba gyaran kitchen din ta zubo masa cuscus din shake da plet ta fito hannuta rike da plet .
Tun daya jin motsin tahowarta gabadaya Hankalinsa yakarkata gareta Wanda shi kansa Bai San dalilin dayasa yake jin hk a tare dashi ba.
har takaraso ta janyo wata Yar karamar stood ta ajiye masa plet din abinci akai hankalinsa Na kanta ahankali ta juya zata koma kitchen taji sautin muryarsa ke.......
Ta juyo tare da dan tsayawa darajar ummi dake zaune a gurin.
zoki kwashe wannan banzar abincin da kika ajiye ance miki Ni jaki ne ?
A ranta ko tace Ai kamafi jaki hauka agurina .
ya buga mata wata razananniyar tsawa tsayuwar uwar me kikewa mutane ?
zuciyar tamkar zata tarwatse tsabar takaici da tashin hankali a kufule takaraso tasoma kokarin daukar plet din ummi tace barshi nablah yi tafiyarki kawai .
ta juya ...Ta koma kitchen Inda ta iske laraba tana aikin gyara kitchen tasaka hannuta tare sukayi komai sunayi suna hira ..... .
Tsawon lokaci ya dauka zaune yana operating din phone dinsa batare ko kallon arziki yayiwa abinci ba.
hakan kuwa yayi mugun batawa ummi rai" tare da hassalata .
dan duk da tsananin son da takewa tilon "dan" nata hakan bazai sa taga yayi ba daidai ba ta kasa yimasa mgn .
Dan hk a kufule tace wannan km wani sabon salon wulakanci ne hk ?
Ya dago yana kallon umminsa tare dage mata girarsa daya alamun tmby ?
minti biyu kacal Na baka ka fara cin abinci nan tun kafin raina, bai Kai Ga baci ba.
abinda ya tsani ji da gani kennan bacin ran umminsa .
km yakasance shine zaiyi dalilin shigarta halin damuwa .
dan hk bbu wani ja inja ko bata lokaci yasoma tsakurar abinci yana ci tamkar yana cin magani ba dan rashin dadin abincin ba sai dan tsagwaron wulakanci irin nasa.
Nablah na kitchen taji ummi Na kiranta da sauri ta amsa tare da barin abinda take ta fito.
,yauwa nablah jeki dakina dan Allah kicewa safeena tabaki jakata ki kawo min kinji.
ta juya kennan taji sautin muryarsa ke....dawo ki kwashe wayan nan abubuwan ..dole ta sake juyowa takaraso Inda yake duk ilahirin jikinta rawa yake.
wani irin abu taji ya dunkule mata a kahon zuciyarta ,ahankali tasoma kokari hada kayan abinci data kawo masa wanda bawani cin arziki yayi ba .
ummi ta dakatar daita ta hanyar cewa barshi nablah karki hada komai agurin nan .
Sannan tayi facing din DEENI da kyau tana harararsa kana tace kabari laraba tazo ta shige dasu .
aikin nablah a gidan nan girki ne kawai .
Sai daya yatsina fuska tare da tabe bakinsa tukun yace Ok Ai duk daya ne first lov Dan aiki Dan aiki ne, bbu wani bambanci da may girki da may shara da sauran ayyukan gida duk dai Yan aiki ne ..
Duk Yan akine Amman ita wannan nata aikin may lasisi ne wanda kasan da hk ko kana daja ne?
uhmmmm first lov Ni Na isa Naja dake ..ok
Yi tafiyar ki kinji nablah ..
Karfe biyar daidai matar gidan tashigo gidan agajiye fuskarta cike da izza da Mulki da nuna isa .
ta zauna tare da Kiran washi Allahna sannan tace ummi sannuku da gida .
ummi ta dubeta tana murmushi may cike da nuna tsansar kulawa da soyayya kana tace yauwa mamana ya gajiya da karatu ?
Kai ummi wlh karatu nan kwata kwata bbu sauki. 'cikin hk nablah ta fito daga kitchen takaraso har inda Zeenat ke zaune tayi mata sannu da zuwa tare da tmbyrta abinda za'a daura Na dare .
Sai data yamutsa fuskarta sannan tace daga dawowata zaki zo min da wani mgnr abinci tun mutun bai gama huta wa ba tamkar wasu mayunwata mtssss taja tsaki.
Ita dai nablah dake tsaye bata sake cewa komai. sai ma ummi ce, tace haba mamana ki dinga bin yarinyar nan ahankali fa kinsa bawai ta taba zuwa aikatau bane wannan shine first time dinta .
to ai tace ummi daga sannu da zuwa sai mgnr abinci .
to ya isa hk wannnan duk ba laifi bane dan ta tmby. Ni dai dan Allah ki dinga sausautawa yarinyar nan yanzu dai gaya mata abinda zatayi.
inji cewar ummi "
sai da Zeenat ta sake yatsina fuska sannan tace paten doya zakiyi min .
..muryar nablah a sanyaye ta amsa da to aunty.
Amman banason yayi kauri yayi ruwa ruwa ..takarasa fadar hk tana duban sashin da ummi take ummi ku mezaku ci ?
Duk abinda mamana zataci .
Zeenat Tayi murmushi tare da cewa Ok amman shi my hrt ki mishi poundo yam da miyar ugu sauran ki yiwa mutane shirme .
Hk nablah ta sake koma kitchen Wanda zuwa lokaci har laraba ta kammalawa da gyaran kitchen din ta fita zuwa wani aikin Na daban.
ahankali take bare doyar zuciyarta tamkar zata buga tsabar bakinciki zamanta ciki gidan ta hada source Na asaro.
Kusan awa biyu da shigar nabla kitchen.
' sai Ga Zeenat tashigo da waya a hannuta tana yatsina fuska da baki sannan tace wai har yanzu akin kikeyi baki gama ba?
nablah da ranta yake a bace matuka .
a dakile tace eh aunty sauran kadan Zeenat taja ta tsaya tana rike da wayarta har lokaci ita dai nabla dataga tana aikin dadaddana waya wanda batasan abinda take yi ba.
km kusan duk sanda take girki a kitchen sai tashigo tayi mata tsaye a ka da waya a hannuta.
byn ta fita ne sai ga laraba tashigo tace nablah ....
Ta juyo tana dubanta batare da ta amsawa laraba.
kinsa me aunty take miki Inda tashigo kina girki . nablah ta girgirza mata kanta ahankali alamun batasani ba .
to wlh video take miki .
Nablah ta Dan tsorata da mgnr har idanuta suka Dan fito waje video km name?
oho Nima bansani ba wlh amman nima hk take min lokaci da nake mata girki.
bangane video ba to tayi me dashi ... ?
nablah ta sake tmbyr laraba .
uhm kawayenta take turawa idan kin yi mistake sai kawayenta suzo har gida su zageki tasssss nima hk ta min kwanaki kafin kizo takira kawayenta sukazo suka minrashin mutunci da zagi iri iri bbu halin ramawa ... .
"nablah nagama jin karshen zance laraba taja tsaki tana jin jina girman al,amarin Zeenat.
sannan tace wanna km iskancin sai dai suyi miki shi Amman Ni ....ta nuna kirjinta da dan yatsanta daya .
wlh bazan dauka ba sai dai hakan yayi sanadiyar barina gidan nan daman km hk nake so.
laraba ta kwashe da dariya nablah kennan Ga tsoro Ga ban tsoro .nan dai suka bar zance suka shiga wata hirar har zuwa sanda nablah ta sauke girki tare da shirya dinning .
sannan ta nufi dakinta bata km fitowa ba har sai data daidaici lokacin dayakama tayi serving Nasu abinci.
sannan ta fito jikinta sanye da doguwar rigar wace ta kama jikinta sosai.
Wanda daga samanta kana hango tundun nonuwanta yayinda kasan rigar keda Shep din flay ta nade kanta da dan karami 'bakin mayafin ganin darene hakan datayi , ya sake fito da ainihin sihirtaccen siffar kyawun ajikinta.
ahankali take daga kafafunta 'cikin takunta may matukar daukar hankali kmr koda yaushe .. takaraso dinning area .
sai dai me kawai ganinsu Tayi zaune tuni sunyi nisa 'cikin cin abinci Amman Banda oga deeni Dan Haka ta juya zata wuce taji Zeenat takirata da sunan datafi tsana a rayuwarta ke..... nablah ta dawo ahankali ta tsaya batare da tace komai ba .Kusan minti Goma tana nan tsaye amman kwata kwata Zeenat bata da niyar cewa mata komai.
sai byn data gama cin abinci ne tukun ta dago fuskarta a tsine tana duban nabla dasu .
hk nace kimin asaro bance miki may ruwa ruwa nake so ba .
mamaki da al,ajabi kalar iskancinta ne ya mamaye zuciyata .amman a dake tacigaba da tsayuwa a gurin sbd bata da halin tafiya taja mata kan wani sabon tashin hankali.
magi nawa ma kika saka acikin abinci ?
nabla tace daidai Wanda zaiji.
nifa banason albarzazanci a gidana akaida magi shida a pot daya ya isa .
jiki a sanyaye nablah tace to shikennan zan kiyaye inshallahu,karma ki kiyaye taja tsaki Zeenat nagama fadar hk ta Mike tsaye tana kakkabe jikinta tabar gurin .
ba nablah dake tsaye ba hatta ummi bataji dadin abinda Zeenat din tayiwa yarinyar ba.
amman taki saka musu baki dan batason tana yawan shiga tsakaninsu tunda tare zata barsu ..
da kyar nablah ta daga kafafunta .takarasa ficewa daga gurin ta nufi BQ ta zagaya Inda Anan dakin laraba yake da fara,a laraba ta tarbeta tana dariya sai yau Allah yayi zaki zo min ?
Murmushi nablah Tayi wanda har wushiryarta ya bayyana ta gaida laraba hirarsu suka Shagayi sosai dan ba ita tabar part din laraba ba.
sai wajen takwas da rabi Na dare tare suka ci abinci da laraba sannan ta baro part din .
Tafiya take sannu ahankali 'cikin sanyin jiki da natsuwa ,ahankali iskar damuna ke kadata kasancewar lokacin ruwa da'ake ciki Wanda kusan yanayin garin Lagos kennan, basu rabo da ruwa sama kasancewar basu da rani da damuna koda yaushe 'cikin ruwa sama suke .
Daidai ta kawo wajen parking space ta jiyo motsi ta dan jiyo ahankali idanunta suka sauka akan fahad abokin deeni kawai ta kauda kanta ta juya tacigaba da da tafiyarta a tunanita Bai ganta ba.
" kawai ta tsinci muryarsa haba Yan mata irin wannan shan kamshin hk Ai akalla ko gaisawa munyi,duk da cewa zuwan nan danke nayi , inji cewar fahad Wanda oready tuni har yasha gabanta.
Take kirjinta yashiga dukan uku uku fatanta kada Allah Yasa ya furta mata kalmar so...dan ita tsoron kalma take
Km bata jin har 'cikin zuciyarta lokacin yin soyayyarta yayi.
domin tafi son ko zatayi soyayya sai ta kammala da karatunta so that sai tasamu daidai da matsayinta .
dan hk a gaugauce zuciyarta cike matsanancin tsoro tace Ina yini .
lfy lau nablah ya gida da aiki?
Kanta ta dago da sauri tana dubansa jin ya ambaci sunanta dan batayi tunanin yasan da zamanta a gidan ba . ballanantana har yakai ga sanin sunanta . yacigaba Ina son ganinki km sbd ke naxo gidan nan zuciyarta ta sake bugawa da karfin gaske..
Ahankali Ta maimaita abinda yace Tare da dan ware shanyayun idanunta akansa .
yace uhm amman idan nagama da DEENI zansa a min kiranki da fatan ba zaki ki zuwa ba.
fuskarta a daure tace Allah yabani iko tana gama fadar hk da sauri ta juya tasoma kokarin barin gurin dan ganin DEENI dake tahowa Inda suke tsaye .
duk da saurin datake hakan Bai hanata jin sautin muryoyinsu ba kasancewar sun biyota a bayanta ne..
Fahad deeni yakira sunanshi a kausashe kafita daga idanuna Na rufe meyasa baka jin shawara ne shege kawai may shegen daurin kan tsiya..
Fahad ya kwashe da dariya sannan yace Kai km meyesa kacika girman kan tsiya da kafiyar maseefa Allah bai haramta min yarinya ba amman Kai kana neman ka rabani da soyayyata.
Na dade da kamuwa da matsanancin kaunar yarinyar nan amman kwata kwata ka kasa ka tsare ka hanani fahimtar daita .
meyasa zaka hanani isar da sakon zuciyata gareta ?
Ok hk kace ?
DEENI yakarasa fadar hk cike da huci yana kallon tsakiyar idanun fahad..
Yes hk nace idan km kaima kana sonta ne kafito ka kasanar sai Na janye maka dan bazan taba iya cigaba da son abinda kake so ba.
bawai ka dinga kokari hanani isar da sakon abinda zuciyata ta kamu da matsanancin so ba
Kasan Ni ..kasan halina km kasan koni waye idan ba son yarinyar nan nake da gaske ba bazan takura kaina akanta ba .
Wulakance DEENI yake masa wani irin duba cike da tsansar tashin hankali yayinda gabadaya yanayinsa yagama sauyawa.
akansa zuciyarsa yace wannan wace irin maseefa ce hk .
Tun bai gama da matsalar kB .
Ga fahad wanda shi ya dan kwana biyu dayi masa zance yarinyar.
Ahankali Fahad yace deeni kana son yarinyar nan fiyye da yadda nake sonta wlh .
idan har kasan kana sonta zan janye amman muddin baka sonta to kabari na shiga sawun manemanta kawai .
Kai wlh Azimi ko rantsuwa nayi bazanyi kaffara ba wlh son yarinyar nan kake yi km so may tsanani fahad yakarasa fadar hk yana share gumin daya fufeshi duk da isakar dake kadawa .
Sai DEENI daya furzar da wata iska ta bakinsa may dumi sannan a zafafe yasoma managa muryarsa cike tashin hankali billahi azim fahad zaka jawowa kanka maseefa ne kawai .
km hakan zai iyayin sanadin da zamu samu mugun matsala may girman gaske da kai idan ka sake furta kalmar....
MMN SUDAIS CE