💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 13-14
Bangane fita zakayi ba byn ko breakfast bakayi ba ina fa hankalce dakai fa duk kwanakin nan bakason cin abinci,
ina zaka ma tukun danaji kace fita zakayi naga week end ce yau .ta hade fuska ta mau hade da zuba masa idanunta.
Ya dan yi murmushi gefen baki har dimple dinsa ya lotsa" kyaunsa ya sake bayyana" ya mike daga kan cinyarta ya zauna sosai shima yana kallon yanayin umminsa" yana jin yadda soyayyar Ummi nasa fiyye da komai nasa "yana sonta baya son damuwarta itace duniyarsa sannan itace ke tattare da duk wani farincikinsa tana tsantsar " son shi da nuna masa duk wata kulawar da uwa kadai zata iya yin haka .
Hannuta yakamo duka cikin nasa ganin yadda ta damu muryasa a sanyaye kmr koda yaushe yace am so sorry my first lov muje zanci tayi murmushi tace kai ko hade da dan dungure masa kai "dan bazata iya fushi dashi "shi kadai Allah yabata " batada. Kmr sa duk duniya . Cikin dan daga murya Ummi tayi kiran zeenat .
DEENi ya yamutsa fuskar sannan ya langwabar da kai yace kibarta kawai "first lov .
ki zuba min da kanki nafi son naci dagareki dan ma banson wahalar dake ne ma da sabon girki zaki min yakarasa fadar maganar cike da shagwaba " ummi ta dubesa ta sake yin dariya tace Allah yashirya min kai yace Ameen yana kashe mata idansa .
byn yagama cin abinci duk da bawani abin kirki yaci ba "Amman hakan yatiwa ummi dadi ko bakomai ya dan saki ranshi ba kmr kwanaki ba" wayarsa ce ta sake karade parlour da kara wanda tun soma cin abincinsa yake jin kukanta "Amma ya" share.
ahankali yasa hannu ya dauki wayar yana kallon screen din " sunan FK yagani rubuce yana wayo "tabe baki Yayi kana ya manna wayar da kunnenshi , , FK najin alamun an daga wayar yace Yayi angon zeenat da girma "kujerarka . DEENi yaja tsaki yace ya'akayi ne" sarkin matsala.
bangaren FK kuwa shekewa Yayi da dariya sannan yace ina waje ina jiranka fa dan banson nashigo muyi westing time dan nasan halinka da son jikin tsiya " shima DEENi bay wani damu da shigorwasa ba dan baya son ummi tasan inda zashi ,
'Umminsa yake kallo har sanda yagama" waya sannan yace mata shi zai fita sai ya dawo tayi masa a dawo lfy " mikewa Yayi tsam cikin tafiyarsa ta kaisata ya nufi hanyar kofar fita ya daura hannushi kan handle ummi takira sunansa ya juyo yana dubanta tace kar kade fa yayi murmushi yace love you mum ya murda kofar ya fice .
Tsaye ya iske FK shi kadai jingine da jikin motar DEENI hannuwansa rungumeta da kirjinsa DEENi ya Mika masa suka gaisa sannan suka wuce kai tsaye gidan big dady.
FK na gaba DEENi na biye dashi a baya har suka karasa cikin gidan suka nufin inda suka san zasu tarar da big dady .
zaune suka hango tsohon mai tarin shekaru da dattako,sai dai" ya dan manyanta kadan domin shine "dan" Muhammad bello khaliyal na farko Kuma shi ke yanke hukunci ga duk abinda yataso dangane da komai" na cikin family .
Zaune yake idanunshi manner da medical glass "da Gani kasan nakara lafiyar ido ne.
suka karaso inda yake da sallarmasu ,da fararsa yake dubansu.
ya ajiye jaridar daily trust din dake hannushi gefe cikin sakin" fuskarsa dauke da murmushi ya amsa sallamar sannan suka gaidashi ya amsa yana tambaye aikinsu" suka ce alhmd .
shr yabiyo baya tsawon lokacin kafin da tsohon ya dago ya sake dubansu.
da fk, suka hada ido dan DEENi tun byn gaisuwar da Yayi masa Yayi kasa da kansa yana kallon yatsun kafarsa" tsai Yayi yana nazarinsu duka sannan yace lfy dai naganku haka duk da yana ganinsu koda yaushe "amman wannan zuwan nasu da dan banbanci "sai daya sake maimaitawa, tambayarsa sannan fk Yayi gyaran murya yasoma yi masa bayanin abinda ke tafi dasu.
Sannan yakara danashi maganar tsakaninsa shemah .
big dady yaji dadi Sosai matuka da jin haka duk da yasan kusan irin aure da akeyi kennan a family din .
Amman duk da haka yaji dadi fiyye da kowani aure da'akeyi family din.
Yana murmushi yace har kun daidaita junan ku kennan ?
fk Yayi tsuru tsuru yana kallon big dady" yayinda shi DEENi har zuwa yanzu kansa na soke a kasa" yana jin duk abinda big dady ke cewa. take yaji karfin gwiwarsa tayi kasa big dady yace uhmm kun gama daidaita kanku ?
still fk ne ya sake bashi amsa yace A'a sai dai shi DEENi ya sanarwa umminsa" amman bata amince da abun ba.
big dady ya kira sunansu daya byn daya, a tare suka dago, suka zubawa masa ido.
big dady yace kuje ku nemi amincewarsu ku daidaita tsakaninku inyaso sai asan abin yi
DEENi zaune tamkar an dasa shi ji yayi kmr kasa ya tsage ya shige ciki haka yaji " dan wani irin kunya yaji tamasa rubdugu dan haka da kyar yasamu ya iya Mikewa tsaye suka bar part din jikisu duk a sanyaye barin ma fk da bai taba tunanin haka ba .
Suna fitowa daga part din big dady" DEENi yasoma zagin fk yana bude masa wuta , yace daman ka kawo ne a sake nuna min iyakata ?
,fk yace haba DEENi ka natsu mana musan abinyi "wlh ko ni kaina bansa haka zata faru ba dan Allah kayi hakuri ka sausauta wlh na dauka komai zai zo da sauki shiya gaji nace muje . wani irin duba DEENi ke jifansa dashi " DEENI yace ok wani sabon rainin wayon zaka sake kawo min .
gabadaya fk yakasa cigaba da magana illa idanu daya zubawa DEENi yanzu yace son zeenat yake" yace masa sam ba haka ba .
DEENi ya tsaya sosai suna kallon juna shi da kf .
a fusace yace kasan Allah kasan yadda zakayi da haukar, damuwar da kaman nami dan ban ai keka kabani irin wannan gurbataccen shawar ba.
Gabada ka rusa min komai , fk dayaga hassala shima jin zantuttukan da DEENi ke furtawa .
A harzuke yace ai bani nace kazo min da shawarar taka ba " iya abinda naga zan iyayi ne" na sanar maka.
Kai tsaye ka fito kace daman can kana son yarinyar" bancin haka daga baka shawarar , meye naka na damuwa daita .
DEENi bai san sanda ya dunkule hannushi" zai kaiwa fk naushi a baki ba.
Take fk ya goce yana kallonsa gabadaya yanayinsa yagama canzawa sai huci yake kmr mayuncin zaki .
Fk yace wai meke samunka ne ?
kodai kasha wani abu ne yau , a fusace DEENi yace wuta nasha ba wani abu .
Sai daya furzar da huci mai zafi sannan yace kasan Allah sai dai kasan yadda zakayi da tashin hankali daka jefani ciki .
fk yace idan ba haka ba Kuma fa "DEENi Yayi kyacci yace I will finish you.... ya wuce fuuuuuu kmr wani zaki .fk yabi bayansa da sauri yana kiran sunanshi yayi banza dashi yacigaba da tafiyarsa da sassarfa har yacimasa ya ruko hannushi "da sauri DEENi ya juyo, ya bige masa hannu " fk yace haba DEENi meyasa kake daukar komai da zafi ? DEENi yace da fetir ne kasan Allah idan har kana son zaman lafiyarka dani " wlh ka nemo solution ya wuce nan yabashi .
Cikin tsanyi jiki zeenat ta mike tsaye byn taci kukanta ta koshi . bathroom tashiga ta wanke fuskarta tukun sannan ta fito' ta murda handle din kofar ' daidai lokacin da shemah ta mike tsaye itama " tasa byn hannuta tana goge fuskarta " yayinda wasu ke sake silalowa" wani irin kallon zeenat ke binta dashi ,kmr takasheta haka take ji wanda kallo daya shemah tayi mata "tarasa dalilin dayasa zeenat ke mata irin wannan kallon haka .
Zeenat tace munafuka ashe zuwan dakike mana gidan" ba dan Allah kikeyi ba.
Shemah tace lfyr kuwa , bangane nufinki ba.
zeenat tace zaki gane manufakar banza kawai daga karki sake shigo mana gida tunda kinada manufarki ta zuwa .
jin haka yayi mugun hassala shemah, gashi daman tana tare da haushin abinda DEENi Yayi mata , hannuta tacire ta dauke zeenat da wani mari wanda ya frigita zeenat .
ai kafin ta sauke hannun zeenat bata tsaya wata wata ba" ta damki makonshi shemah tace ni kika mara.. kika mareni daga bazaki sake marin wata ba ,wani irin nishi shemah ke fitarwa tana mutsu mutsun kwatar kanta har hawayen wahala take fitarwa ,zeenat tace ba kukan soyayya kikeyi ba zan aikaki abarzahu inyaso kya ji dadi yin kukan da tushe .
Km still tana damke da makoshinta " tace nufinki kice kina son yaya DEENi ko .
Wlh yarinya karyar tasha karya " da kyar shemah tasamu tasa iya karfinta ta kwace kanta daga rikon da zeenat ta mata .
Take suka suma kwokuwa da juna gabadaya hayaniryasu ta cika gidan ,a tsorace ummi takaraso gurinsu ta shiga tsakanin" zeenat da shemah wacce har shedewa take saboda kukan dayaci karfinta gabadayansu fuskarsu tayi jazir,.
zeenat na kuka shemah na kuka cikin fushi da bacin rai ummi ke tambayar su abinda ya hadasu fada amman cikin bbu wanda yabata amsa har sanda " DEENi yashigo gidan ya samesu tsaye cirko cirko , yaja ya tsaya yana jan tsaki dan tun shigowarsa yake jin hayaniryasu yanzu ma ganin ummi ne yasa ya tsaya , da kallo yabisu dashi " ummi na ganinsa tace yauwa gara ma daka shigo , ta sanar masa abinda faru ummi nagama fada masa takama gabanta .
ai yana gama jin abinda umminsa tace ya fara dauke zeenat da wani mahaukacin ,mari dayasa taji dan guntun fitsarin dake makale da mararta zubowa , itama shemah bata nata sannan ya gwara kansu gabadaya waje daya jikake gum....... Bbu wacce tayi kokarin yin kuka cikinsu dan sunan halinsa sarai bakaramin aikinsa bane ya hada musu da punishment.
tsawa ya daka musu yace kowace ta takama gabanta tun bai sabauta musu jiki ba , hade da cewa yan iskan yaran kawai .
Dakinsa ya wuce yasoma zariya daga farkon daki zuwa karshe hannuwansa duka yasa yana balbale botura rigarsa" wani irin zafi yake ji a zuciyarsa tamkar ana zuba masa barkono , gumi ke tsatsafo masa takoina kmr ba dazu yayi wanka ba " sai daya balle botura rigar ya cire yayi jifa daita ya fada kan bed idanunshi na kallon sama celling dakin ahankali .
Ahankali yasoma runtse idanunshi har ya rufesu ruf gabadaya tunani mafuta kawai yake tabbas indai sai ya tunkari yarinyar nan da sunan yana sonta to wlh ya hakura daita har abada kai auran ma yafasa gabadaya .
MMN SUDAIS CE