*BANI BACE
INNOCENT MARA LAIFI
*ELOQUENCE WRITER'S ASSOCIATION
Basira Sabo Nadabo
Wattpad @ Basira_Nadabo
Uwayen ɗakina kuna raina kuma ina godiya da kulawarku gare ni. Basira Sabo Nadabo tana godiya bisa kaunar ku a gare ni.
Uwar ɗaki na Aysha Sada Machika (MYSHA)
Uwar ɗaki na Mrs Hamisu (GOYON KAKA)
Dedicated To My Sweetat Ramalurv
6/08/2017
SHAFI NA ASHIRIN DA ĎAYA
Nagode ya mai shari'a ta cigaba da cewa malama Mariya zaki iya komawa ki zauna, zan nemeki wani lokacin in hakan ya taso, ya mai girma mai shari'a da haka nake neman alfarmar kotu data bani belin Wahiedat tunda har yanzu zarginta akeyi ba'a tabbatar da hakan ba kuma ina rokon wannan kotun mai adalci data kara bani lokaci akan kawo mata duk kanin hujjoji gamsashshu, nagode ta koma ta zauna barrister Abubakar sai harara na yakeyi ko kallo bai isheni ba muma mata muna da rawar takawa a kowani mukami aka ajiye mu ba komai bane bazamu iyaba ko wacce mace da irin baiwar da Allah ya bata, wata gurin iya magana wata kuma gurin iya kwalliya wata kuma gurin iya girki gadai sunan kowa da irin baiwar halittar da Allah yayi masa
Alkali yayi nazari mai zurfi yace kotu ta ɗaga wannan shari'ar zuwa goma ga watan da muke ciki sannan kuma wannan zama shine zama na karshe da kotun zata saurara, ya kara da cewa kotu ba zata baki belin wacce zargi ba za'a cigaba da rike ta har sai gaskiya tayi halinsa ya buga gudumarsa kowa ya mike alkali ya fita nima aka tisa keyata ziwa gidan jaru
JALINGO
Hajiya gaskiya da sake wallahi bazai yuwu ba ya za'ayi abar 'yar mutane a gidan yari kodan ke baki taɓa haihuwa ba shine yasa haka haba mana ina iliminki yaje ne kuma shi wannan abinda ake zarginta dashi ke kinsan abinda yasa tayi hakan ko kin nemi jin na bakin ta kafin ki yanke hukunci, ke kanki shaida ce yadda Zeenert take son Abban ta amma ace an wayi gari ta aikata abinda ke kike zarginta dashi donni har yanzu bana zargin 'yar talikar nan Allah
Haba yaya Aina'u ki saurare ni mana nice fa taki nice ya kamata ki saurare ni
Na saurare ki kice min me kice min kin kai 'yar da kika raina tun tana tsummar goyo sannan kice min bakisan abinda zata aika da wanda bazata aikata ba, ni kinga tafiyata kuma wallahi bazamu taɓa shiryawa dake ba idan dai zeenert bata dawo gidan nan ba
Haba yaya Aina'u don Allah karki tafi ki barni
Ah toh kidawo da Muzeenat gidan nan, na dai faɗa miki kenan, abinda wanda kikeyi don shi ɗinma bai barki ba nafasan komai duk wani kulle kullenku nasani kuma wallahi in bakiyi wasa ba saina kaiku kotu da gidajen radiyo tare da talebijin don bazan taɓa yarda da wannan cin kashin ba ehe
Don Allah ki tsaya kiji wallahi akwai abinda nake so mu tattauna dake yaya Aina'u, wallahi maganar tana da mahimmanci kila inna faɗa miki na samu saukin sa a cikin raina
Toh ina jinki, amma kisani bazan taɓa canjawa ba dole a cikin biyu kiyi ɗaya
Yaya Aina'u shekaran jiya ne wata mata tazo gidan nan wai tazo amsar 'yarta, ni ta kulle min kai saboda nasan bamu da wata 'ya a gidan nan sai zeenert kuma tazo harda min gargaɗin cewa inhar ban fito mata da yarinya ba kotu ce zata raba mu, toh kinji abinda yake damuna
Hmmm babban magana to ke baki tambaye ta wata 'yar ba ko kuma ta kawo miki wata 'yar ne bamu sani ba
Toh shine nima na kasa ganewa wallahi tun ranar kaina a kulle take na rasa yadda zanyi yaya Aina'u
Yanzu yaushe tace miki zata dawo?
Bata faɗamin ba, tadai ce inhar ban fito mata da 'yarta ba kotu ne zai rabamu
Toh shikenan ki bari tazo ɗin sai muji wayata 'yarta ne zamu bata ko
Hmmmm toh shikenan Allah ya kawo ta
Amin, ni zan koma saina sake dawowa ko, inhar tazo kiyi maza ki kirani
Uhmmm, sai anjima toh
GIDAN SU HIEDAT
Malam In Shaa Allahu mune da nasara gashi nan gaskiya ta fara futowa nifa ban yarda da wannan Mariyar ba, saboda ji daga barrister tayi bata tambayoyi harta wani rikice anya kuwa Alhaji
Ai In Shaa Allahu hajiya mune da nasara bakiga idon yarinyar nan ba harbwani zufa take gogewa na rashin gaskiya kai mutane basu da imani haba mana mutun ya kashe ɗan mutun kamar ya kashe kiyashi kai duniya ina zaki damu ne
Hmm badai gobe bane zaman mu na karshe zamuyi kallo ai, In Shaa Allahu, barin ɗan kwanta na huta malam
Toh hajiya ni inada aikin da zanyi ki tashi lafiya ko
*Eloquence Writer's Association
Karamar Su Babban Suce Ni Wato 'Yar Mutan Kd Ce
Basira Sabo Nadabo
Follow Me And Vote My Story On Wattpad @ Basira_Nadabo
YOU ARE READING
BANI BACE
Short StoryLabari ne akan wata yarinya da aka kaita gidan yari a dalilin kashe wani dan sarki da tayi, amma tace ba ita bace, shin itace tayi kisan ko kuma wani ne? kudai ku biyo ni don jin yadda zata kasance, sannan in kin karanta kiyi voting sannan kofar ko...