Page 16

419 31 2
                                    

Duk saurin Ustaz wajan dakatar da Ridayya daga shigowa cikin toilet ɗin, haƙarsa bata cimma ruwa ba. Ya dafe kai yana murza goshinsa da zufa ke fesu wa ta tsakiyar wajan. Cikin saurin kuma ya saki labulen dake tsakanin jacuzzie da mirror wajan shigowa. Ridayya ganin bata ga Ustaz ba ya ɗan leƙa kanta cikin sanyin muryarta ta ce "Abbiey, nine, gani" Ta furta idanunta na rufe wa sosai srup ɗin da Ammi ke mata ya yi matuƙar tasiri a kwakwalwarta, she's always sleeping. "Abbieynaa!" Ridayya ta furta tana mai janye idanunta ta buɗe su da ƙyar, saboda wani irin maganaɗisun bacci dake ribatar idanunta. Ustaz dake tsaye dafe da kansa gabansa sai tsananta bugawa yake, da ƙyar ya samu ya zura jallabiyya a jikinsa ko hiramin bai samu zarafin ɗaurawa ba ya ɗaga laubulen ya fito, idanunsa ya sauka a kan ta, ganinsa tsaye a gabanta ya saka ta buɗe bakinta tare da yin murmushi. Ya girgiza kai a hankali ya sunkuya ya ɗauketa a kafaɗa suka fice daga toilet ɗin zuwa bedroom ɗin Ustaz.

Ƙoƙarin kai hannu take zata taɓa tsayayyen gemunsa dake zubda ruwa ya yi saurin riƙe ɗan mitsitsin hannun nata, idanunta zube a kanta ya ce "Na roƙe ki Shalale ki ce ba kiga Abbiey yanayin haramci ba..," Ta yi shiru tana kallonsa ya janye idanunsa sai kuma ya juya da sauri bayan wani abu ya zo ransa ya cafke hannayenta muryarsa a daƙushe ya ce "Me hakan ke nufi Shalale? Da gaske ban fahimta ba, nikam ban fahimta ya zan yi da al'ƙawarin dana ɗaukar wa kai na? Kin rusa komai kin rusa tunanin Abbiye Shalale" Ya yi baya tare da kwanciya yana rufe ido, kokawa yake da tunaninsa wanda ya rabu kashi-da-kashi. "Babu mai ganin tsaraicina sai matata!" Kalaman suka dawo masa, koda wasa ya faɗi abu to gaskiyar kenan, ya zai yi da wannan jirkitaccen al'amarin? Ya miƙe tsaye kamar zai fita ya dawo ya durƙosa daidai tsayin Ridayya duk ya gaji da magana, kuma da taimakon shi dole bakin Ridayya zai buɗe, ya kalli cikin idanunta da suke sauya masa kala a kullum a kodayaushe a taushashe ya ce "Shalale kin ga abin a halin da matarsa ce kawai zata gansa?" Cikin rashin fahimta Ridha ta kalli Ustaz, jin ya ambaci sunan Abbiye ya saka ta yi murmushi dimples ɗinta na lomawa kana ta ɗaga kai, Ustaz ya yi saurin girgiza kai yana runtse gajiyayyun idanunsa masu laushi, faɗuwar gaba na wanzuwa a ko wanne lungu da saƙo na ƙofofin zuciyarsa, ya tsune laɓɓansa a nutse ya ce "Subuhanallahi! Hakan na nufin...?" "Zata zama Matarka idan har da gaske al'ƙawarin zuciya ne, kuma zuciyar ta Ustaz Muhammad-Bilal"

Ustaz bai juya ba, domin ya fi kowa sanin mamallakin muryar. Umma ta ƙarasa shigowa cikin bedroom ɗin ta juya ta kalli Ridayya ta kuma kalli Ustaz kana ta ce "Sai ka ce rainon matarka kake bamu da labari" Ya yi shiru ta taɓe baki kana ta ɗora da "Da sake an bawa mai kaza ƙafa, ka gaggauta sauya tunani" Sai a lokacin Ustaz ya kalli Umma kamar ba zai yi magana can dai ya girgiza kai ya ce "Umma please, kai na ciwo yake" Domin bashi wata magana bayan wannan ɗin, bayan ita kuma bai san wacce magana zai furta Umma ta gane tsakaninsa da Ridayya zumunci ne kawai. Umma ta ce "To, ta dai haramta a gare kuma, she's not your type, kwailar ma?" Ya kalli Ridayya sosai kana ya kalli Umma ya ce "Mene kwaila?" Ta ce "Baka sani ba?" Ya yi shiru ta yi murmushi ta ce "Kwaila ana nufin ƙaramar yarinya, ƴar mitsitsiyya wacce bata fara irgan dangi ba, balle batun al'ada" Ya sake juya idanunsa duk a gajiye yake daga jiya zuwa yau "Irgan dangi?"

"Nono irin na ko wacce ɗiya mace nake nufi Ustaz" Ustaz ya yi saurin rufe ido yana miƙewa tare da toshe kunnensa ya ce "Ya Rasulullah Asstagafirullah, ba a kunnen Muhammad-Bilal ba" Umma ta ce "Tunda na yi saƙo ba? Shekarar ta shida kai kuma shekara ashirin da biyar, ƙanwarka ce babu wani zance bayan wannan" Har ta fita ta tuna abinda ya kawo ta, ta ce "Ana kiran ka a sashin Baffa" Tana furta hakan ta yi waje tana jan tsaki, halin Ustaz gabaɗaya a bauɗe yake ta rasa waya gado? Tana fita Ustaz ya juya ya kalli Ridayya da ta yi shiru idanunta a kasalance ya saka ƙafa tare da zungureta ta buɗe ido a gigice jikinta na rawa da ɓari tunaninta Ammi ce, domin komai yana zaune a ranta daram kamar yadda al'amarin ya nuna a karatu, haddar ƙaramin yaro, kamar rubutu ne a kan dutse ganin Ustaz ya saka ta kwaɓe fuska za ta saki kuka.

MUNAFUKIN MIJINơi câu chuyện tồn tại. Hãy khám phá bây giờ