Episode 45

91 3 0
                                    

KANKI KIKA CUTA
    👩‍🦰👩‍🦰👩‍🦰
         👩‍🦰👩‍🦰
            👩‍🦰
(Tsantsar cin amana)

Story and ✍️ written by
Khadeejaht Hydar
(Young Novelist)

From the experience writer of.
.*IHSAN
*UQUBAR UWAR MIJINA
*WATARANA SAI LABARI
*PRINCE AIRAN AND MAIMOON.

And now with the heart touching one.
KANKI KIKA  CUTA

     ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ  g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶  *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

   
Vote and follow me on wattpad
@YoungNovelist4

My Facebook Group
https://www.facebook.com/groups/228916361333651/

My twitter link
https://twitter.com/YoungNovelistII?s=09

DEDICATED TO
All member of Hydar and Muhammad's Family.

SPECIAL GIFT TO
Anti Zainab Muhammad

Vote nd read via this link on wattpad
https://my.w.tt/ZxkqnOOO2bb

Like, join and comment to read this novel from page one.
https://www.facebook.com/Khadeejaht-Hydar-Hausa-Novels-YoungNovelist-101121485268631/

Episode Fourty Five🖊️

         Ba jimawa  suka isa wani private hospital da'ita,saida suka ƙarasa suka yaƙira su Ummi ,koda za'a shiga da'ita labour room hannun Saleem ta riƙe gam tana ciza leɓe tace"Sahab karka barni dan Allah,dakyer nurse ɗin ta kwace hannun Saleem sukayi labour room da ita idonta kyem akan Saleem da hankalinsa yagama tashi idanuwansu sunyi jazir don tausayawa Saleem don dagani ba ƙaramin dauriya takeba ,bayan kamar minti goma saiga su Ummi da Mama,tambayarsa suka fara  ina Saleem yace"Ummi tana labour room yanzu aka shiga da ita dama muna zuwa naƙiraku,zama sukayi suna mata fatan sauƙa lfya,shiru shiru tun shida na safe har yanzu takwas amma ba wanda yafito daga ɗakin da Saleem take nan hankulansu yatashi jiki na rawa Saleem yanufi ƙofar amma tun kafin yaƙaraso yaga babban doctor ɗin yafito yana sharce gumi yakalli Saleem yace"kaine kakawota ko?gyaɗa kansa yayi yace"Doctor ina matata ?ya take?ta sauƙa ne?,duk amsar tambayarsa yake jira,Doctor yace"eh to gaskiya da matsala,matsala shine abinda Saleem ya maimaita kawai saiyaga idonsa ya rufe baya ganin komai , jirine ya kwashi Saleem yafara koƙarin sula lewa amma Muhammad da yanzu shigowarsa da Falmata yayi saurin tareshi inaa Saleem ya sume😭,cikin tashin hankali Mama tace"Saleem katashi Saleemar fa ba mutuwa tayiba amma inaa,sai wani ɗaki aka kaisa,cikin tsoro takalli likitan amma tunkafin tayi magana likitan yakalli Ummi yace"bazata iya haihuwa da kantaba sbd ƙarfinta ya ƙare kum...kafin yaƙara magana wata nurse tazo da sauri tace"sir she is pushing the baby is coming da sauri yakoma yabarsu tsaye cikin tashin hankali.
    A ɗakin labour kuwa Saleema ce take koƙarin pushing tana ta salati,wani nishi mai ƙarfi tayi saiga ɗa y danno kai,likitan yace"u can do it push again,macen ce tace"yauwa kiyi nishi ga ɗanki yakusa zuwa dayake itace akanta zata ƙarbi ɗan,cikin wahala tace"Doctor dan Allah kaƙiramin mijina wlh zan mutu,tace"kiyi haƙuri zan,bai ƙarasaba tayi wani nishi tayi saiga ƴarta tafaɗo,hamdala sukayi su duka itakuwa ji tayi kamar anciremata wata wahalar,idanuwanta ta rufe tana maima Allah godiya,babyn kuwa sai tsantsara kuka take,gogemata jiki sukayi da olive oil sannan wata nurse tafita don ɗaukar kayan baby,dai dai fitowarta Saleem yafito a birkice yakalli Mama yace"Mama ina Saleem?likitan yace akwai matsala meyasameta?,haka ya jero mata tambayar bakinsa na rawa zaka iya hango  tsoro a kan fuskarsa ,Nurse ɗin ce tace"ka kwantar da hankalinka matarka ta sauƙa lafiya batare da anmata aiki ba kayan Baby zakubani,wata sanyayyar ajiyar zuciya Ummi tasaki ,dama sunzo da kayan tunda Saleem yafaɗa mata basuzo dashi ba,ƙarɓar  kayan tayi ta wuce Saleem bai tsaya jin bayanin taba ya wuce ɗakin da sauri amma a bakin ƙofa likitan yabasa umarnin ya tsaya ba'a gama kimtsa taba,saida yayi minti ✋ tukun akace yashiga suka shige tare dasu Ummi,kotakan yaron baiyiba gunta yanufa kamar zaiyi gudu,fuskarta yakama yakasa magana,murmushi tamasa tace"what happened,sai alokacin ya sauƙe ajiyar zuciya cikin kallon ƙwayar idanunta yace"i nearly died i mean i fainted when the doctor says there is a problem,nazata wlh kinbarnine da bansan inda zanje ba da bansan inda zan saka raina naji sanyiba,kallonsa tayi idonta nacikowa tace"i won't give on u Hamma just d way i knw u won't,zanrayu dakai har mutuwa,itama zanso ta ɗaukemu a tare,kissing ɗinta yayi a goshi sannan ya juya gunsu Mama dasuka tsaya kallonsu cikin sha'awa sam Saleem baida kunyar nunama duniya son Saleema,babyn ya karɓa saikuma yace"Alhamdulillah,bayn kyau ne da'ita masha Allah idanuwanta komai na Saleem da Saleem saboda inka kalleta bazakace ga dawa take kamaba cikin iyayennata,su Ummi ne suka iso suna mata sannu amsawa tayi tana kauda kai wai kunyar itama ta haihu,Ummi murmushi tayi ta taimaka mata ta jingina a pillow,miƙamata ƴar akayi wai ta shayar,yi tayi kamar ma batasan ana mata magana ba taya za'ace ta shayar ga Saleem gasu Mama,ganin  hakane yasa su Mama fita,kamar jira yake yazo yana koƙarin yaye rigarta yabawa ƴarsa mamma,riƙe masa hannu tayi tace"Hamma kadaina kabari inmunje gida,yace"so kike ta mutune ɗan bata kaɗan kinji Baby na,da wayo yasa taciroshi ta sama yataimaka mata tasamata shi a baki,saurin cireta tayi tana ɓata fuska,yace"miye ne kuma?,"Allah ni zafi nakeji ,yace"ai zaidaina sbd farkone kibata kinji,bata tayi itakuwa saita cafka tana tsotsa dariya yayi ganin yadda ƴarsa ta tsatson mace mafi soyuwa agareshi take shan nono,itama Saleema yarinyar ta sturama ido tace"Hamma dawa take kama ne wai?,yace"damu mana,dariya tayi zata sake magana akayi sallama,cire yarinyar tayi ta gyara rigarta,Falmata ce wacce batasamu shigowa ba don ta koma gida ɗakkoma Saleema ruwan zafi,da murmushi tashigo tana cewa"ah lalle mai jego ashe dai haihuwar ba zafi,harararta Saleema tayi tace"kefa kika sani tunda de bakiji kukanaba,murmushi Saleem yayi yace"ah ah faMummyn matata ai kema kisan jaruma ce,tea mai kauri tahaɗa mata ta karɓa tana miƙawa Falmata ƴar,tace"ah wlh kam kunga ƴarnan bata kama da kowa saiku baza'ace ga kamartaba ko dawa take kama kowa dama yaga iyayenta zaisan iri ne balantana yanzu da ƴarnan tasamu,wannan inta girma ai sai ai zaton ƙanwar kuce,dariya sukasa ,bayan aune aune likitan ta tabbatar ba matsala aka sallamesu misalin goma,sai alokacin suka fara bugawa ta haihu sbd ɗazu basa cikin nutsuwar su.

Tun kafin su isa gida wasu masu zuwa barkanma harsun rigasu zuwa,nan aka ɗunguma falon  Ummi,Saleem da Muhamamd suka wuce gidansa,acan cikin gida kuwa jama'ane maƙotansu keta tururuwar zuwa barka,gaskiya jama'ar lagos akwai kara,haka suka dinga zuwa barka ana ta yaba ƴar,daga ƙarshema Ummi ta ɗauketa ta goya ta rufe saboda yadda bakin mutane suka fara yawa a kanta duk wanda ya ɗauketa sai yay magana saidai in anzo ance ina jaririyar ace tana gun Ummi sbd likitan yace adaina yawan ɗaukarta shine tagoyata.

Da daddare Saleem yaji shiru baiga ankawo Saleema ba kawai yawuce gidan,a parlour ya taddasu banda Saleema dake bacci a ɗakinta na gidan Ummi,sai irin abokan su Mama na kusa waenda basu ida tafiya ba,gaidasu yayi sannan kuma ya nufi ɗakin nata,a kwance ya taddata tana bacci sai ya ɗau yarinyar don tafara kuka yafara jijjigata,Saleema ce ta tashi tace"Sahab sannu da zuwa yaushe ka shigo banma saniba zama yayi a gefenta ya miƙamata babyn,ƙarɓarta tayi tafara shayar da'ita,yace"ki gama shayar da'ita mutafi ko?,idanu ta zaro  saikuma ta maida tayi murmushi tace"to kafaɗawa Ummi zamuwuce tabaka magun gunan ta mutafi,tashi yayi ya fita parlourn babu kowa daga Ummi sai Mama saisu Abba gaoda su Abba yayi sannan yace"Ummi kibamu maganim babyn zamuwuce gida kar dare yayi..

Saimun haɗu gun suna Fans kuyi ado mai kyau.

Hhhh to nima Fans kubani comment mai ƙyau kafin dare yayi.

Taku dai a kullum.

Karku manta da

Comment
Share zuwa ga sauran groups.

Sannan jama'ata ta wattpad karku manta da danna min VOTE💃🖊️.

Autar💃🖊️
Billyn Hamma

KANKI KIKA CUTAWhere stories live. Discover now