3
🧚🏻♀️Abun Alfahari na🧚🏻♀️
Na
💕Teemahcutey 💕
Sallam ta rangad'a taji shiru ta qara rangad'a wata nan ma shiru taji kawai se tayi wuff ta shige a main parlour.....
Tad'an jima zaune se ga yar aiki tace mata Hajia tana bangaren mai Gidan Meenah tace tau.
Yaya haidar ne yay sallama ta amsa se ta gaida shi yayi mata ya hutu tace Allhmdllh.
Guri ya samu ya zauna yana tambayar ta yaushe zasu koma? Tace mishi next week ne
"Wai yaya Haidar yaushe Walida zata dawo ne? Yace mata "in the next 3 days...
()()()()()()()()
TUNA BAYA.
Alhaji Usman d'a ne gun Alhaji Shehu
Alhaji Shehu d'an kasuwa ne yana zaune a garin Sokoto a wata unguwa wacce ake kira Runjin Sambo, dashi da Matar shi daya Hajiya Gwammah.
Auren had'i ne aka musu, ba wata soyayya tsakaninsu amma dai sun fahimci juna sossai kuma suna qaunar juna Sossai...
A shekarar su ta biyu da aure Allah ya azurta gwamma da samun ciki, a ranar kuwa murna kawai suke musamman Alhaji Shehu dama yana matuqar son y'ay'a se gashi Allah ya bashi....
ranar wata asabar ranar ta zame musu ranar baqin ciki musamman a gun Alhaji Shehu saboda yammacin wannan ranar ne gwamma tafito daga ban d'aki kawai se tazame ta fad'i a qasa runtum.
Salati ne yake fita daga bakinta a yayinda jini yake gudana ta qafafunta, daidai wannan lokacin se ga Alhaji Shehu. " Assal.... sallamat da be isuwa ba kenan Saboda mawuyacin halin da yaga matarshi a ciki...
Batare da bata lokaci ba Ya sungumeta se hospital....
A nan ake sheda musu cewa lallai dan cikinta ya zube, tashin hankali ba'a sa mishi rana domin kuwa a ranar Alhaji Shehu kiris yarage yayi hauka.
Amma dayake Allah ya bashi matar qwarai ita ta dinga kwantar mishi da hankali har ya sassauto...
Washe gari aka yi discharging nasu suka koma gida...
Bayan wata ukku hajia gwamma taqara samun wani ciki .... bayan wata tara da awa tara da Minti goma sha tara wata wahaltattar naquda ta tada ita cikin dare ba qaqqautawa.
Batare da bata lokaci bah Alaji ya kaita asibiti...
Har qarfe biyu na rana ana abu daya amma haihuwar ta gagara, cikin ikon Ubangiji, Allah ya bata ikon haiho samballeliyar diyarta mai kama da ubanta.
Alaji yayi mata hud'uba da suna Fad'imatuh-zahra'u. Amma ana kiranta da Zarah.
bayan shekara biyar Allah ya qara azur tasu da haihuwar d'ansu mai suna USTHMAN daga shi se Allah ya qara basu wani mai suna umar dagannan haihuwar ta tsaya chakk..
Babu laifi Alhaji Shehu yana kula da y'ay'a sa yana biya musu buqatunsu
Fatima ta kammala makarantar ta anan Alaji yace ta fidda miji.
Tafitar da wani mai suna Ahmad, aka
mata aure aka kaita garin kaduna chan xata ida karatun ta cikin kwanciyar hankali.
Usman ya kammala karatunshi a Usmanu dan fodiyo University inda ya karanta engineering... kuma yana harkan kasuwancinshi domin kuwa Alhaji shehu ya azashi..... bayan ya kammala ne aiki ya gagara so ba yadda zeyi kawai ya aje kwalinshi ya fad'a kasuwanci ba kama hannun yaro.
A kwana a tashi har kasuwancin yayi albarka Allah ya albarkaci kasuwancin sossai gashi kuma saurayine mai qwazo saboda ana bashi kwangiloli..
Nan danan yazama yong billionaire...
So adaidai wannan lokaci ne Alhaji Shehu yace yakamata yayi aure....
Usman yace "to baba inshllh xan fidda wacce nakeso nan bada jimawa ba "
Batare da 6ata lokaci ba usman ya fidda wata diyar maqwabcin su mai suna Fareedah.
An daura auren Usman da Fareedah inda aka kaita Bado quarters suna zaman Lpia.
Anan ne Allah ya hada Hajia Fareedah mak'wabtaka da Hajia Rahmatu.
Hajia Ramatu tana da y'a'ya biyu Aisha ce ta farko se Haidar.
Allah ya azurta Hajia Fareedah da Alaji usman haihuwar farko inda suka samu Maryam wacce ake kira da Miemie.
Sunyi matuqar farinciki sosai bayan shekara biyu Allah ya qara azurta Hajia Fareedah da mak'wabciyar ta Hajia Ramatu da samun ciki... cikin ikon Allah suka haihu rana daya Hajia Fareedah ta haifi Ameenah wacce ake kira Meenah, Hajia Ramatu ta haiho Waleedah...
Bayan zagayowar shekara hajiya faredah taqara haihuwar Maneer
Agurguje...
Hajia Fareedah da Alhaji Usmab suna da y'ay'a 3 Miemie, Meenah and Maneer
Hajia Ramatu kuwa tana da y'ay'a 3. Aisha, Haidar da Waleedah.
Tsakanin haidar dasu walida akwai taxarar shekara 13 tsakani.
An saka su duka a makaranta Miemie da Meenah da Waleedah.
Meenah da Waleedah dsame class suke while Miemie ta wucesu da aji biyu.
Ana cikin haka se Allah ya qarama Alhaji Usman yalwar arziqi ya qara sa gina musu sabon mansion a bafarawa estate.
Ba bata lokaci suka tashi daga bado.
Watam su daya da tashi suma su hajia Ramatu suka 6a66aka suka koma sabon gidan su na kaduna road.
Zumunci tsakanin su ba'a magana
Domin kuwa sun zama kamar yan uwa.
Suna ziyartar juna.
Tun a quruciyar yaran guda biyu wato Waleedah da Meenah suke tafka rashin arziqi domin basu Jin magana ko kad'an ga d'an banzan rashin mutunci ga jan fada amma se tsoro.
Akan tsananin surutunsu yasa aka bama Meenah class rep Waleedah ass. Acewar malamai tunda an basu shugaban ci ba batun surutu.
Wannan kenan.
()()()()()()()()
Cigaban labari.
Dama Waleedah taje hutu ne gidan Anty Aisha dake aure ah Zamfara state.
Yaya Haidar yace yaushe zaku rubuta jlc ku ne? Tace da ankoma da sati biyu zasu fara yace tam Allah ya taimaka tace Ameen tana wasan hauru...
Bata jima ba se ga Hajia Ramatu ta shigo "ahhh yau menah ce ah gdan? Kodai batan hanya kkyi domin nasan baki zuwa se in Waleedah nanan"
"Laaa Mama bahaka bane mommah ce ta aikoni"
Ta fad'a tana sosa qeya.
"ohh anyi haka kuwa domin d'azu takirani tacemin ai zata aiko a kar6an mata saqo"
bayan gaishe gaishe aka gabatar mata da abinci tace ta qoshi
Mama tabata saqon tace takaima mama. Takarba tace to.
Amaimakin ta tashi ta wuce se ta gyara zama, Mamah ta kalle ta amma se ta qyaleta ta d'auka ta gaji ne.
Bayan 1hour Mamah tace "Meenah kije ki Kaimata tun marece beyi bah"
tace "tau " se ta tashi tace to Mamah se anjima.. ok bye.. Allah ya tsare ....
Kamar barauniya haka take tafiya tana sand'a har takawo bakin gate.
Tana sand'a ta leqa aikuwa taga har yanxu mazannan nanan basu tashi ba..
Ai kuwa ai hanzarce ta koma ciki...
Mama tace "lpia baki wuce bah meenah? Ko mantuwa kikayine??
"Ehmmmm ahmmm ehnnn" take fad'a tana y'an soshe soshe, "Mama dama Anty Aisha nake son ki kiramin taba Waleedah zanyi magana da ita...
"Ok to jeka daki ki dakkomin wayana... taje ta dakko se tabata ta kira mata ita....
Aiko kamar wacce za tayi waya da saurayi ta shige dakin walida suka gaisa
Anan meenah zufah na keromata ta gayamata abunda ya faru tana neman mafitah agun walida...
Acan bangaren bana jin abunda walida take cewa meenah kawai se naga meenah ta saki murmushi se suka katse wayar..
Ahankali tafito tana sanda... kitchen tanufah a hankali, ba wanda yangan ta kawai senaga ta d'auki knife🔪 tasaka a jakanta gurin fitowane ta hadu da mama
Mama tace kingama wayar tace ehh se tabata wayar ta tafice ah gidan...
🧚🏻♀️Abun Alfahari na 🧚🏻♀️
Na
💕Teemahcutey💕
Truncated by watsapp #wattpad