01

4.8K 276 32
                                    

*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:Jamilaumar351*

*DEDICATED TO:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi...!*

_Bismillahir rahmanir Rahim in the Name of Allah,The Most  Beneficent The Most mercefull Praise be to Allah Lord of The Words..._

*001*

*ZARIA..*
Area:Tukur-Tukur...

'"Hafsah!...Hafsah...!Hafsah...! sunan danaji Megidana Abdullahi na Tsagamin shi da Asuban fari,wanda hatta mazan da suke wucewa ta kofar gidanmu in sun dawo Daga masallaci suna iya Jiyo kwakwazon Kiran Sunana da Abdullahi keyi muryansa Kakkausa kamar zata tsaga gidan.

Kaina na Dafe ina Daga Durkushe acikin karamin Kichen dinmu Dake tsakar Gida Ina Faman kunna Risho sai na kunna Lagwanin sai ya mutu da kanshi Tun Wajen 6 da wani abu na safe na Fito ina idar da sallar Asuba ban ma yi Tunanin komawa ba Saboda yau din Litini ne farkon Sati Su Amira nada Makaranta kada su makara Abdullahi ya Dora Laifin akaina Tunda tare yake Wucewa dasu in zai tafi aiki Bisa Mashin Dinsa mai Suna Wayyo Kudina.

Saurin Mikewa nayi Jin kiran yafara Kusantoni kada na Kular Dashi dogon Sikat din Jikina na gyara Lokaci daya da Hijabin danayi sallah wanda ban cire ba Jin garin yau din an Tashi da sanyi sanyin Damuna dayake Jiya an kwana Tsala ruwa,ina kokarin Shiga Dakin muka ci karo Dashi zai Fito,Da Sauri nayi baya ina Raba Ido Cikin Kulufuwa da Takaichi yake Jifanta da wani kallo kafin ya Daga Murya yana Fadin"Wani sabon Iskanci kuma kika samo Hafsah..!?

Muryanta cikin Sanyi nace"Name fa Abban Amira..? Harara ya wurgamin yana Fadin''Bansani ba..Nace bansani ba bandama Salon iskanci kira nawa nayi miki Tun ina Daga cikin Daki baki amsa ba sai da na Fito..? Yafada yana wani karkace tsayuwa Cikin Jin Haushinta,Ajiyar Zuciya ta sauke kafin ta kada kai kawai ta wuce shi Zuwa Cikin Dakin bayanta yabi yana Fadin"Hafsah ina mgana kina Tafiya..? Yafada cikin Mamakinsa.

Atsakiyar Falon Taja ta tsaya tana Fadin"A"a kayi Hakuri ba Tafiya nayi ba na Shigo Daki ne kada makota su jiyo Fadanka,mganar kuma Kira banji bane Lokacin danaji na amsa kenan zan taho Dakin sai ga ka kayi Hakuri.."Tafada Cikin Sanyin Murya Kawai Tsayawa yayi yana Kallonta cikin Fada,sai yanzu na karemai kallo Dogon Namiji ne mai Cikar zati da kamala mai Fadin Kirji da cikar Cikakken Da Namiji mai iko Ba fari bane ammh Wankan Tarwada ne,Fuskarsa bata da Tsawo sosai sai dai tana da Fadi kadan Hancinsa Dogo ne Turbarkallah Masha Allah Sajensa daya zagaye bakinsa shi yake karamai kyau da Kwarjini.

Abdullahi Usman Direba kenan Dan Misalin Shekaran Haihuwan 32 da biyu Aduniya Mai iko ne kuma mafadacin Namiji ne ga iyalansa bai da sauki ko kadan Ballatana Ragowa a kallan Farko in kayi mai bazaka taba Zaton Abdullahi ya iya Fada ba ammh Ranar dakayi katarin zuwa gidansa nan zaka ga Abunda ake Kira Tijara da kudinka Sai kayi Mamakin Dama Abdullahi na iya Dogon Mgana ne..?haka yake baka iya yankema Abdullahi Hukunci ga Dabi"unsa matarsa Hafsah ce kadai Zata iya Fadar Wanene Abdullahi 90%Cikin Halayyarsa wanda Mutane basu sani ba,sai yan"uwansa makusantansa.

Numfashi ya Sauke Lokaci Daya yana Fadin"Eh Lalle wato kada makota Sujiyo Fada na ko Hafsah..? Wato ga mafadaci ko..? Yo in gaskiya kikeso Uban wa ke sani Fadan in bake ba.Kullum kwakwalwarki bata Daukan Mgana Koda yaushe sai dai adinga nanata miki Mgana Daya,ko karatu ya isa ki gama Haddaceshi acikin kwakwalwarki ammh Ina baki da Buri illah Kiga Ina Mgana Shine Burinki sai anyi Mgana kiwani Langwabe kai kamar Wata marainiya kina Sharan kwallar karya.."Yafada yana kallonta tana goge kwallarta da gefen Hijabinta,Bata dagoba ta kara kwantar da Murya tana Fadin"Allah ya baka Hakuri.."

Tsaki yaja yana Fadin"Ameen...Sai ana mgana ki wani fama ma mutane kuka kina wani Allah baka hakuri"yafada yana kwaikwayan Muryanta cike da Haushi ita dai bata Dago ba kanta na kasa tana kallon Center Capet din Dake tsakiyar Dan madaidacin Falon nata wanda yaci Kujeru saiti Daya mai Dauke da Karama Mai zaman mutum biyu Guda biyu da kuma Mai zaman mutun uku guda daya na kuma mai zaman mutum biyu,Babu komai daga kujerun sai Tibin Bango Plasma dake kafe a bangon Dakin,wanda ya samu mahadin Dish din da suke kallo Dashi..

MASIFAFFAN NAMIJI..!Où les histoires vivent. Découvrez maintenant