014

1.1K 116 6
                                    

*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*DEDICATED TO:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!

_Shafin yau Gabadayansa Sadaukarwa ne zuwa Gareki *MY BEST❤️HALIMA..* ALHERIN ALLAH YA KAI MIKI ADUK INDA KIKE AMEEN..._

*014*


"Falon babu Kowa sai karan Talabijin Daya ketayi Shi kadai...Kwata kwata Babu motsin kowa Cikin mamaki Dukkansu suke Bin Falon da kallo ganinsa kaca kaca da alama dai matar Gidan bata Dubashi ba.

Saman Center Table din Dake Tsakiyar Falon Ga Filet nan da kofuna da kuma Goran ruwa da lemo Wanda da alamu Harda wanda akayi amfani Dashi Jiya da Daddare dana yau da Safe, kila da megidan zai Fita ne,ya Taimaki kanshi.

Suna Ta Raba ido Cikin Falon,Subai Ta kalli Hafsah tana Fadin"Ke wai matar gidan kuwa tana nan..? Hafsah tace"Tana nan mana..Da bata nan da batace tana nan ba kinsan tace batajin Dadi kila Tana ciki ne.."Mariya ce Ta kara bude baki ta kwarara Sallama sai ga Sakina ta Bude wata Kofa dake yammah haka ta Fito Dagani Daga barci tatashi Domin Rigar barci ce ajikinta mai igiyoyi,Sai wata Hula Dake saman kanta Fuskarta Duk ta yamutse Alamun dai Tun barcin Jiya bata iya Tashi ba sai yanzu.

Da Mirmishi ta Tarbesu Lokaci Daya tana karisowa kusa dasu Cikin Fara"a tace"Sannun ku da zuwa..ku zauna Ashe Kun kariso...?Hafsah tace"Eh wlh..Muna Ta sallama muka ji Shuru..? Ta fada tana zama kan Daya Daga Cikin kujerun da sukayi ma Falon kwanya,Suma su Subai"atu da mariya da Jidda Hade da Inna Talatu suka nemi waje suka Zauna,Lokaci Daya suna gaisheta ta amsa Tana kallon Inna Talatu ganinta Babba yaasa ta gaisheta ita kuma ta amsa Tana Tambayanta gida da yara.

Mirmishi Sakina tayi batayi mgana ba Hafsah ce tace"Wasu yaran Inna..? Wadanan yan Boko ne yara ba yanzu ba.."Inna Talatu tace"Ikon Allah daman Haihuwan Tsarata ake sai sonda Mutum yaga dama..? Kai yaran zamani.."Tafada tana kyabe baki Dariya suka sakamata Harda Sakinan Subai ce tace"Inna baki gane ba..Ba yanzu suke Bukatar ya'yan ba sai zuwa Gaba.."Inna Talatu ta tabe baki Tana Fadin"Aikin Banza ai Duk wannan Shirme ne da Biyema ka"idan Yahudawa Annabi da kansa yace kuyi Aure ku Haiyayyafa sai nayi alfahari Daku Ranar lahira ammh ku kuma kuna ma Tsara Lokacin da zaku samu ya"yan ne Allah ya kyauta To.."suka kara sakamata Dariya saboda sanin Halin Inna Talatu na barkwanci da kuma Ban Dariya.

Sakina dai batayi mgana ba, sai Mirmishi sai chan ne,Hafsah ta kalleta tace"Kanwar Mama ce muna ce mata Inna Talatu.."Yake tayi Tana Fadin Allah sarki Kafin Hafsah ta Nuna Subai tana Fadin"Nasan baki santa ba Ita ke bima Zannira sunanta Subai"atu azaria take aure..su Mariya kuma nasan kila kin ganesu..? Sakina ta kallesu Daya bayan Daya kafin tace"Allah Sarki..Sannunku da zuwa.."Suka amsa da yauwa Subai"atu dai nata yan kalle kalle Tana Tabe baki Sakinar na Lura da ita,sai itama ta Dauke kanta ta Mike tana Fadin"Bari na kawo muku Ruwa...kunzo ban lahiya banyi komai Cikin Gidan ba.."

Hafsah tace"Ayyah bakomai da kin barsa ma munsha Ruwa saman Hanya muke.."Bata saurareta ba tawuce zuwa Kitchen suka Bita da kallo ganin yadda take wani taku ta kowani Kira na Jikinta yana amsawa Baki Subai ta Rike tana Fadin"Ji wai macen Aure..? Ji gidanta..?gaskiya Ya Nazifi kyan jiki kawai yabi da Dukiyar mahaifinta ammh banda haka wlh banga Abun so anan ba.."Hafsah ta Take mata kafa tana kyafta mata ido Mariya nata Dariya Inna Talatu dai bata saka musu baki ba Domin Itama Sakinar bata bata Sha"awa ba sam..

Ruwa da Lemo ta kawomusu da Kofuna kana ta koma ta Cikin Bedroom dinta ta Dauko wayarta tazo ta zauna ta Dora kafa daya Kan Daya tana latsawa Subai kuwa sai Binta da kallo take awulakance,ganin basu sha Ruwan ba yasa Sakinar ta kallesu Tana Fadin"Kun ki shan Ruwa..? Hafsah tace"Zamu sha..Dayake kinga Daga gidan zannira muke bamu tare da kishi.."Itace tasha Ruwan sai Inna Talatu Subai da Mariya da Jidda ba wanda yasha,Sunanan zaune sau Daya Sakinar ta Dago tana Tambayan Hafsah yasu Amira..? Tace suna Lafiya suna Gidan Ammi.

MASIFAFFAN NAMIJI..!Where stories live. Discover now