038

1.2K 110 31
                                    

*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!

*038*

"Har Abdullahi yakai Office yana Tunanin maganganun Barkat Abun ya Dauremai kai matuka kuma Kaso mafi yawa Daga Cikin kimarta sai yaji Ta Ragu ba saboda komai ba sai Saboda Ta Nuna Kishinta karara akan Hafsah har kuma Hakan ya saka mata Tsanarta acikin Ranta Batare da ta mata komai ba..Miye laifin Hafsah..? Itafa tazo ta isketa da Mijinta Suna Rayuwansu Ta Shigo Cikinsu Ashe kuwa indai Ita bata Bude baki Tace tana Shigar mata Hanci bai kamata ita Barkat din Tace Haka ba,Domin Shi yana da yakini kan Hafsah 100%Bata da Tunani ko Zuciyar Cutar da Barkat Tana Zaune da ita ne Tsakaninta da Allah.

Tagumi kawai ya Zuba Lokaci Daya yana Cigaba da Auna Abubuwa masu Girma Ta Bangaran Hafsah da Barkat,Ko kankani basu ma Daidai ba Domin Akowani Mizani in ya Auna sai yaga Hafsah Tayi ma Barkat Fintinkau Bata iya ma Tsara da ita,Ta Bangaran Hakuri,ta mata Zarra ta Bangaran Ladabi da Biyayyah Wlh zai bada Rantsuwa kan cewa Duk Matan Duniya Ba Mace mai Ladabi da Biyayyah Uwa Uba Hakuri Bayan Hafsah,Sai kuma Bangaran iya Mu"amala da kuma Yadda zata Tafiyar da zamantakewarta Yafi kowa sanin Wacece Hafsah bai Taba Jin wanda ya Fadi aibunta ba Kama Daga Danginta Zuwa Danginsa ba,Hakika Tayi Gadon Dattako da kuma kyawawan Halin Iyayenta,Ya sani Mama Tamkar uwa take gareshi Ammh Ita kanta tana Girmama Hafsah,Umman Sadiq ita ta Haifeshi ammh Tafi Girmama Bukatun Hafsah Fiye da nashi Bukatun Kuma Tana Fadamai koda yaushe sukayi mgana kan ya Rike Hafsah da gaskiya da Amana Domin In ya bari ya Rasata ko kuma Giyar Rudin Duniya ta Sameshi ya Wulakantata Toh Tabbas Watarana zai yi Nadama,Kuma zai yi Kuka da idanuwansa Domin bazai Taba sanun mace kamarta ba bai kara gasgasata mganar Umma ba sai yanzu Daya Auro Barkat yaga Bambamce Bambamce Halayyah Da yawa ta Bangaran Hafsah sai kuma yanzu yake Tunanin kodai mganar Nazifi gaskiya Bayan Hafsah ba Macen da zata iya Hakuri ta zauna Dashi..?

Gabadaya Ransa yana Jagule ne Dakyar ya iya yakice komai ya maida kai ga aikinsa ammh Kuma Gefe Daya na Zuciyarsa na karfafamai Gwiwan Takama Barkat din Burki Domin Bazai Lamunci ta Raina mai Mata ba gaskiya Indai Hafsah batace ta Tsare mata komai ba itama bata da Wannan Damar da zata Fadi Wata mgana kan Hafsah Domin akomai Da take ganin Hafsah Ta mata Fintikau Halayyanta ne suka Siya mata Duk Wannan Kimar Datake gani tana Kishi akanshi.

******

Baiwar Allah Hafsah bata son Wainar da Aka Toya da safe Tsakanin Abdullahi da Barkat ba Dama Jiya ita ta Fita Girki Barkat din ta karba,Da Safe kuma Abdullahi ya Shigo mata Sallama ya isketa tana Wanka Su Amira Kuma Daman Mai mashin Dinsu ya kira yakaisu so basu Hadu ba Balle Taga Cikin yanayin Daya Fita Noor kadai Dake kwance kan gado yayi ma Wasa ya Fice.

Har Wajen 12pm na Rana bata ji Motsin Barkat ta Fito ta Daura Girki ba sai Abun ya bata mamaki Ta sani da Wuri take Gama Girkinta,Sai Tayi Tunanin kila Girki Daya Zatayi ammh sai me Har Pass2 shuru bata ji Motsinta ba Duk da haka dai bata Fito ba,Tana Daki Ita da Noor Dataji yunwa Sai Ta Hada Tea tasha,Har Amira suka Dawo Makaranta Barkat bata Fito ba Suna Ta Tambayan Abinci sai ta Hada musu Complex suka Sha Suka kwanta kafin Lokacin Islamiya sai Lokacin ta Fito Tsakar gidan Abun mamaki Dakin Barkat din ma na Bude ammh Kwata kwata ba Motsinta sai Hafsah ta Fara Tunanin kodai Bata da lafiya ne..? Kamar zata Shiga sai kuma ta Fasa Tunda Daman bata Shiga Dakinta sai ta kama Kuma Daman yau din Barkat din bata Leko Ta mata gaisuwan Safe da Abdullahi ya kafa Dokar Haka ba, sai kawai Zuciyarta ta bata ba lafiya.

Dakinta ta koma,Itama takwanta ita da Noor sai Hudu Saura Tatashi Tayi sallah tatashi Su Amira sukayi sallah sukayi Shirin zuwa islamiya,Ta rakasu Har Kofar gida kana ta Dawo Cikin Gida,Tayi Tunanin ta Kira Abdullahi sai kuma ta Tuna yana Office yana aiki bazata so ta tayar mai da Hankali ba,sai kawai ta Share acikin Ranta kuma Tayi Wani Tunani inda Barkat din Tana so ta san Tana Cikin wani hali ko bata lafiya da Ta Kirata ta sanar da ita Tunda suna Gida Daya amfanin zaman Taren kenan ammh Tunda taki Fitowa bata Bukatar wani ya sani kenan kawai sai ta Fita Batunta ta kama Harkan gabanta

MASIFAFFAN NAMIJI..!Where stories live. Discover now