029

862 71 13
                                    

*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!

*029*

*YININ BIKI...*!

"Yau ta kama Asabar ne wanda yayi Daidai da Ranar Daurin Auran Jidda da Angonta Nazifi Tuni Kowani bangaren gidajen ya kaure da Sha"ani Tare da Shagalin Biki ba Gidan Mama ba,ba gidan Inna Abu ba,kuma Ta ko"ina Area su ta Dinke da Jama"a Tunda dama Duk anguwa Daya ne sai Taron Mutane yayi yawa Sosai.

Bangaran ango kuwa Tun Wajen 9am na Safe suka Baro Gidan Abdullahi Cikin Shigar Shadda mai Ruwan Sararin samaniya Riga da wando Duka Harda Babban Riga,Kala Daya sukayi Hatta Takalmi da agogo Wanda Shi Abdullahin ya Dinka musu Shi kuma Nazifi sai ya Siya musu Hula zanna Bukar mai kyau da Tsari.

Shagalinku Hotel suka Nufa Inda Sauran abokan Nazifin suka Sauka Abokan aikinsa Wadanda Suka zo Daga Kaduna sai Wadanda sukayi karatu Tare,chan suka Bata Lokaci sai Gabda Daurin Auran kana Motocinsu suka Shigo Cikin Gari,Dama a masallacin kusa da Gidan Baba Wada za"a Daura Auran da Misalin Sha Daya na Safe Koda suka isa Waje ya Dinke da Jama"a ba Tsaka Tsinke Dakyarsuka samu Hanyar Shiga Cikim Masallacin.

Karfe 11:10am na safe Shaidu suka Shaida Daurin Auran Hauwa"u Usman Direba Jidda da angonta Nazifi Wada kan Sadaki mafi Daraja kuma lakadan ba ajalan ba,Ayayinda Baba wada ya zama Wakilin Amarya Shi kuma Mijin Goggo Habiba Ya zama Wakilin ango Daurin Auran Daya samu Dimbin Hallatan Mutane Daga Waje Waje dadama Ciki akwai abokan aikin Abdullahi da abokan karatunsa Haka bangaran ango ma akwai abokan aikinsa Daga kaduna da Wasu Daganan Zaria,da abokan Auwal da Tsofaffin abokan Baba wada Dama na Mahaifinsu.,sai kuma Dangin Hajiya Sa"a na Uwa Dana Uba Duk sun mata kara Sunzo kwarai da gaske Taro fa Yayi Taro Abun sai wanda ya gani da idanuwansa Harda Salisu yazo Daurin Auran kuma Dashi Bayan Daurin Auran suka yada zango a Usmaniya Restaurant Dake kongo Zaria akayi Reception.

Bangaran Amarya kuwa agidansu Rumana kawarta suke zama,Dayake abinci aiki suka kai akayi musu Ba wanda ya Wahala Hatta Drinks Nazifi ya kawo musu Tun Safe mai kwalliya tazo ta gwangwajesu,sai wanda ya gani Amarya Jidda tayi kyau Har Gaji da kyau,Da Safe Shadda ta saka Wacce Duka Gidajen Biyun Sukayi ankonta Da gidan Mama da gidan inna Abu Sukayi ankonta kowa ka gani Dashi,Daga Cikin Gida kuwa Su Hafsah da su Subai"atu ke kai da kawo Abinci anan aka Dafa Tuwon Shinkafa,da Shinkafa da Wake,Sai zobo da Ruwa Suma Din Biki yayi Biki Tuni Kowa yaci wankansa yana ta Warwarsawa su Hafsah makotansu Mama sukaje sukayi wanka Suka Shirya Daman Kayansu da komai da komai yana gidan Bayan sunyi Wanka Sunyi kwalliya suka Dinga Daukan Hotuna Su da ya"yan Goggo Habiba su Jamila kowacce ta yarda ya"ya suna chan Gidan Mama suna Shan Biki,Subai"atu dai bata da yarda zatayi Saleem na Tare da ita Taso Ta makalama mahmud da yazo Daurin Aure Shi kuma ya gudu yaki karbanshi,Zanniratu kuma Tana Wani Daki Tare da Dangin Mijinta da suka zo mata Biki Subai"atu kanwar mijinta ne Tana Tare da kawayen Amarya.
,Su Ummi kuma sunzo har sun Tafi.

Ita kuma Hajiya Sa"a da Tawagarta Suna gidanta chan Take nata Taron sai zuwa yammah yan chan zasu Taho akai amarya dasu.

Nazifi Suna wajen Reception ya Ciro Wayarsa yaTurama Sakina Sakon... *Alhamdulillah...An daura Aure..Yau na Tabbata Miji ga Hauwa"u...Fatan Allah ya bamu zaman lafiya.......*Ya Turamata da gayyah ya nuna mata ya zabi Jidda Fiye da ita aikuwa Tana gani Sakina ta Fara kuka Tana Fadin manganganu Tunda Ta Dawo Gida bata da kwanciyar Hankali ko wajen aikinta Bata koma ba Tun Tana Tunanin ganin Nazifi har ta Daina Ta Shiga Damuwa Sosai kullum sai kuka Bata taba Tunanin haka take son Mijinta ba sai wannan gabar Kawarta Rukky Ita Hajiya ta Kirata tazo Tana Bata baki Bayan ta karanta Sakon Nazifi Sakina na kuka Tana Zagin Nazifi da Abdullahin da Ita kanta Jiddan Rukky ta Bude Baki Tana Fadin"Wai ina ce ba wannan abokin nashi da kuke Mutumci da matarsa bane Nazifin ya auri kanwarsa..?

MASIFAFFAN NAMIJI..!Wo Geschichten leben. Entdecke jetzt