023

924 84 11
                                    

*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!

*Intelligent writer' asso...*

*023*


"Haka Abdullahi yajema Hafsah Cikin Wannan Farincikin Wanda ya kasa Boyuwa Daga saman Fuskarsa,Tayi ta mamaki ganin Wannan Fara"a kamar me,Data Tambayeshi sai yace mata Bakomai koma miye zata ji Daga Baya.

Su Amira kuwa Auwal ya Dawo Dasu Bayan ya Dawo Daga Shago,Shi Abdullahi yama Manta Dasu ya Taho Shi kuma yana Dawowa Shago Mama tace ya Daukesu Amira ya kaisu Gida,ya Dade sai Wajen goma yayi musu sallama ya koma Gida Bayan yayi Dinner dinsa anan Suna ta Hira da Hafsah Abdullahi ko yana Ciki ya kwanta gajiya ta Saka Barci ya Daukesa da wuri.

Washegari Inna Abu ta kasa Zama sai da ta Shiga gidan Mama ta Fara Zegunta mata Hakika Mama tayi murna ammh acikin Ranta Tana Tunanin Jidda ne,ganin ai babu Soyayyah Tsakanin Nazifin da Jidda Tayaya wannan Halin zai yuyu,Koda yake Abdullahi ne in yace Eh din ne baya iya Sauyashi Duk Rigimar Jidda sai dai tayi Hakuri kawai.

Da Mama Taji Labari sai tayi Gum da Bakinta Tunda Abdullahin bai gayamata ba,Sai da ya taso Daga aiki,kana ya Biyo ya Kira Mama Cikin Dakin Auwal ya Gayamata komai Mama tayi Shuru kafin tace"Naji Dadin wannan mganar Domin Nazifi mutumin kirki ne,Ammh kana ganin Shi Nazifin zai so Jidda Har suyi zaman Aure..?

Abdullahi yace"Karki Damu da wannan Mama Abokina ya Tabbatarmin da Cewa Yana son Jidda Tsakani ga Allah kuma so na Aure.."Mama tace"Toh ita Jiddan Fa..? Zata so shi kuwa..? Kaga fa har yanzu Jidda Yarinya ce.."Abdullahi yace"Haba Mama Kina Wani mganar yarinya A yarinyar take Abunda ko Babban Albarka Ban damu Da tana son Shi ko Bata Sonshi ba nidai Hakkina na matsayin Babban Wa gareta Shine na Nema mata Gidan zama na Har Abada,ita ta isa tace bata son Nazifi ne..?dame tafishi...? Wlh shi ba ajinta bane sai dai kawai al"amarin Aure Ya gaji haka.."

Mama ta Rausayar Dakai Tana Fadin"Shikenan...Allah ya Sanya alheri ya Shige mana Gaba.."Yace"Ameen Na riga na Barma Baba wada wuka Da nama kan mganar Saboda haka zan Kira Zannira da Subai suzo gida muyi mgana inaso ayi komai Cikin Lokaci ne Mama.."Mama tace"Ya kamata..ammh Ya za"ayi zaka karbi Lambar Hajiya Sa"a ne ka Sanar da ita ko yaya..?

Cikin Mamaki yace"Wata Hajiya Sa"an..?Mama tace"Mahaifiyar Jidda mana.."Karamin Tsaki yaja kafin yace"Ni ba wacce zan Kira Mama..Yarta ta gayamata ko ke..! Jidda kuma gobe Ki Turomin ita Gidana Ta kwana zan sanar da ita Zuwa asabar ko Lahadi kuma Nazifi zai Shigo su gana in Allah ya kaimu.."Mama tace"Hakan ya kamata Allah ya nuna mana..ya kuma Sanya alheri.."ya amsa da Ameen da haka ya mata Sallama ya Fice Daga gidan..

Daga Mariya Har Jidda ba wacce ta kawo Tunanin komai acikin Ranta,Zannira da Subai"atu sum Ji mamaki kiran da Abdullahi yayi musu da kanshi yace in sun samu Dama Cikin Satinan su Shigo yana son mgana dasu sai Zannira Tace sai Dai Ranar sati Saboda karatun yara Shima Abdullahin yace Hakan yayi Saboda Office Ranar duk da yana da Karatu a Abu in ya Dawo sai Su Hadu gidan Mama.

Kowacce ta kira yar"uwanta Tana Fadamata Kiran ya Abdullahi suna Hasashen Allah sa Lafiya,Koda suka Kira Mama kin Fada musu tayi tace Bata sani ba,Mama bata samu Tura Jidda ba sai Ranar Laraba da yammah Tace ta Shirya Tatafi gidan Abdullahi ta kwana da safe sai ta Dawo Tun da Taji haka sai tasha Jinin Jikinta Tana Tsaye a tsakar gida Tana Ninke kayan Mama Data wanke mata a kan igiya,Mariya kuma tana gefe kan Tarbama ta baje littafai Tana karatu,Mama kuma na Daga kofar Kitchen tana Tsinkan allaiyahu Zata saka Cikin Miyar Taushan da zatayi.

Jin Abunda Mama tace ne yasa Daga Jidda Har mariya suka Dakata da Abunda suke suka Dago suka kallonta Gabadayansu Cikin Mamaki Jidda tace"Mama gidan ya Abdullahi kuma..? Har na kwana..? Lafiya..?

MASIFAFFAN NAMIJI..!Where stories live. Discover now